Ticker

6/recent/ticker-posts

Hukuncin Macen Da Ke Sa Kayan Mijinta?

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu Alaikum, malam barka da warhaka, malam tambayata ita ce, mun karanta hadisai da suke nuna mana cewar Allah da Manzonsa sun tsine wa namiji mai kamanceceniya da mata, haka ma ita ma macen, to malam tambayata a nan ita ce shin malam har da macen da ta sanya kayan mijinta don raha da wasa a tsakaninta da mijinta wanda kuma ba fita za ta yi da su ba? shin malam ina hukuncin yin hakan? ALLAH ya ƙara wa malam lafiya.

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa'alaikumus Salamu, Matuƙar Shari'a zta haramta abu da nassi ingantacce kuma bayyananne, to ba ya halasta mutum ya ce zai kwatanta yin wannan abun don ya daɗaɗa ma wani, saboda haka ba ya halasta mace ta sa tufafin mijinta don wasa tsakaninta da shi, Ibn Abbas ya ce: Manzon Allah ﷺ ya la'anci masu kamanceceniya da mata daga cikin mazaje, da masu kamanceceniya da maza daga cikin mataye" Bukhariy 5885.

A wani hadisin kuma da yake magana a kan sanya kayan ma ƙuru-ƙuru, wanda Abuhuraira ya ruwaito yana cewa: "Manzon Allah ﷺ ya tsine wa namiji mai sa kayan mata, da mace mai sa kayan maza" Abu Dáwud 4098.

Saboda waɗannan dalilai, ba ya halasta namiji ya sa kayan mata ko na wace ce, haka nan ba ya halasta ita ma mace ta sa kayan maza ko na wane ne a zance mafi zama dai-dai.

Allah ne mafi sani.

Jamilu Ibrahim Sarki, Zaria.

Zauren Tambaya Da Amsa Abisa Alkur'ani Da Sunnah. Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin mu...

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments