Ticker

6/recent/ticker-posts

Waƙar Alu Magatakardar Wamako Mai Suna “Wamakko Za ni Gobe” Ta Sani Sabulu

Wannan na ɗaya daga cikin waƙoƙin Alhaji Musa Ɗanba'u Gidan Buwai.

www.amsoshi.com

Gyara Ubangijina,

Ya Allah Sarkin Gabas da Yamma.

Gyara Ubangijina,

Gyara Allah Sarkin Gabas da Yamma,

Allah mai Kudu mai Arewa,

Ya Allah Ubangijinmu,

Gyara.

 

Ku doka tambura,

Ku ƙara tambura,

Ku doka tambura,

In ka ji tambura,

Ai an ga babba zaune,

In ka ji tambura,

An game da manya.

 

Wamako za ni gobe,

Don darajar Alun Magatakarda,

Huta da lafiya lau.

 

Wamako za ni sauka,

Don darajar Alun Magatakarda,

Ya Allah kyauta zamaninka,

Ka kyauta wa Sani mai kalangu,

Abin da kake min,

Na yaba da kyauta.

 

Ya Allah ya kyauta zamaninka,

Huta da lafiya lau,

Mijin Arziki sai godiya nake ma,

Mijin su Atika,

Na yaba da kyauta,

Ya na Atika Alun Magatakarda,

Ya Allah ya kyauta zamaninka,

Alun Hassa yana nan,

Ya kyauta wa Sani mai kalangu,

Dan Darajar Alun Magatakarda.

 

Ada mai fetur,

Ada mai fetur Arkilla,

Na yaba mai,

Dean darajar Alun Magatakarda a fili.

 

Huta da lafiya lau,

Ya Allah ya kyauta zamaninka,

Huta da lafiya lau,

Jan zaki Alun Magatakarda.

 

Allah shi ma, Ah!

 

Shekaran jiya,

Na yi mafarki

 

Ya maƙi garaje,

Ya Allah ya kyauta zamaninka,

Na Audu Sifika godiya nake ma,

Yayan Audu,

Yayan Audu na yaba da kyauta,

Audu sifika ina yaba ma,

Don darajar Alun Magatakarda.

 

Ya ba ni kuɗi,

Ya ƙara kuɗi,

Ya ba ni kuɗi,

Kuma yaaa haɗa da riga,

Don darajar Alun Magatakarda a fili.

 

Marigayi Dingyaɗi na yaba ma,

Sannu diji na yaba da kyauta,

Sannu na Tambari maƙi garaje,

Ya Allah ya kyauta zamaninka,

Ka kyauta ma Sani mai kalangu,

Alun Magatakarda.

 

Haƙin sama sai raƙumi,

Akuya na so ba ta iyawa,

Akuya na so wuyanta bai kai ba,

Ta koma ta ci hakin da lasa dole.

 

Ya gyra gida,

Ya gyara dawa,

Ya bai wa gida,

Ya bai wa dawa,

Na gode Alun Magatakarda.

 

Ya gyra gida,

Ya gyara dawa,

Ya bai wa gida,

Ya bai wa dawa,

Na gode Alun Magatakarda.

Ya bai wa ‘yan gida,

Ya bai wa baƙi.

 

Ya Allah shi biya ka darrajan ma’aiki,

Sannu Diji Alun Magatakarda,

Allah ya kyauta zamaninka,

Godiya nake yi,

Ina Alun Hassan?

Ina Alun Hassan?

Na yaba da kyauta,

Dan darajar Alun Magatakarda.

 

Ada Arkilla,

Na yaba ma,

Domin darajar Alun Magatakarda,.

 

Audu kamsila, kakakin majalisa ne,

Audu kamsila,

Kuma kakakin majalisa ne,

Mai ba ni kuɗi,

Ya ba ni kuɗi,

Ya ƙara kuɗi,

Ya haɗa da riga,

Don darajar Alun Magatakarda a fili.

 

Huta da lafiya lau,

Hakin sama sai raƙumi mutane,

Akuya na so ba ta iyawa,

Ta koma ta ci hakin da lasa.

 

Yi musu hairan,

Ka mai da sharri,

Kar ka damu.

 

Gyara Ubangijina,

Gyara Allah Sarkin Gabas da Yamma,

Allah mai Kudu mai Arewa,

Ya Allah Ubangijinmu gyara Allah.

 

Ku doka tambura,

Ku ƙara tambura,

Ku doka tambura,

Da ka ji tambura,

Ai an ga babba zaune,

In ka ji tambura,

An game da manya.

 

Wamako za ni gobe,

Domin darajar Alun Magatakarda,

Huta da lafiya lau.

 

Wamako za ni sauka,

Domin darajar Alun Magatakarda,

Ya Allah ya kyauta zamainka,

Ka kyauta wa Sani mai kalangu,

Abin da kake,

Na yaba da kyauta.

 

Ya Allah kyauta zamaninka,

Huta da lafiya lau.

 

Mijin su Arziki sai godiya nake ma,

Mijin su Atika na yaba da kyauta,

Ya na Atika Magatakarda,

Ya Allah ya kyauta zamaninka.

 

Alun Hassan yana nan,

Ya kyauta wa Sani mai kalangu,

Don darajjar Alun Magatakarda.

 

Ada mai fetur,

Ada mai fetur,

Arkilla na yaba mai,

Don darajjar Alun Magatakarda.

 

Huta da lafiya lau,

Ya Allah kyauta zamaninka,

Huta da lafiya lau,

Jan zaki Alun Magatakarda.

 

Allah shi yi ma,

Eyeh!

 

Shekaran jiyua,

Na yi mafarki,

 

Sannu na Atika maƙi garaje,

Ya Allah ya kyauta zamaninka.

 

Na Audu sifika godiya nake ma,

Yayan Audu,

Yayan Audu na yaba da kyauta,

Audu sifika ina yaba ma,

Don darajjar Alun Magatakarda.

 

Ya ba ni kuɗi,

Ya ƙara kuɗi,

Ya ba ni kuɗi,

Kuma ya yaɗa da riga,

Don darajjar Alun Magatakarda.

 

Maigari Dingyaɗi na yaba ma,

Sannu Diji na yaba da kyauta,

Sannu na Tambari maƙi garaje,

Ya Allah ya kyauta zamaninka,

Ka kyauta wa Sani mai kalangu.

 

Alun Magatakarda,

 

Hakin sama sai raƙumi mutane,

Akuya na so ba ta iyawa,

Akuya na so wuyanta bai kai ba,

Ta koma ta ci hakin da lasa dole.

 

Ya gyara gida,

Ya gyara dawa,

Ya bai wa gida,

Ya bai wa dawa,

Na gode Alun Magatakarda,

 

Ya gyara gida,

Ya gyara dawa,

Ya bai wa gida,

Ya bai wa dawa,

Ya bai wa ‘yan gida,

Ya bai wa baƙi.

 

Ya Allah shi biya ka darrajar Ma’aiki,

Sannu Diji Alun Magatakarda,

Ya Allah ya kyauta zamaninka,

Godiya nake yi.

 

Ina Alun Hassan,

Ina Alun Hassan,

Na yaba da kyauta,

Don darajjar Alun Magatakarda.

 

Ada Arkilla,

Na yaba ma,

Domin darajjar Alun Magatakarda.

 

Audu kansila,

Kakakin majalisa,

Audu kansila,

Kuma kakan majalisa.

 

Mai ba ni kuɗi,

Ya ba ni kuɗi,

Ya ƙara kuɗi,

Ya haɗa da riga,

Don darajjar Alun Magatakarda.

 

Huta da lafiya lau,

Hakin sama sai raƙumi mutane,

Akuya na so ba ta iyawa,

Ta koma ta ci hakin da lasa,

Ah!

 

Ka musu hairan,

Ka mai da sharri,

Kak ka damu da su Magatakarda,

Ka san yaro ba ya kai ga babba.

 

Canjin rauji da kiɗa

 

Yaƙi noman sarki,

Tafiya noman falke,

Yaro kauce a faɗa maka,

Manya sun zo da shiri.

 

Mu koma BK don in ga Habu babana,

Mu koma BK don in ga Habu babana,

Sannu DG ka kyauta min da yawa,

 

Allah shi yi ma sutura,

Yadda kau wa Sani bahago,

 

DG na gode ma,

DG ka kyauta min.

 

Manya kanun gayya,

 

Mu koma BK don in ga Habu babana,

Sannu DG ka kyauta min da yawa,

Allah shi yi ma sutura yadda kau wa Sani bahago,

DG na gode ma,

Baban Lawal Habu,

Ah!

 

Baban Lawal Habu mai kwana da shiri,

Yadda kai wa Mamman gaishe ka nake,

Allah shi yi ma sutura yadda kau wa Sani Bahago.

 

Ranan Alhaji Mamman Sani,

Na zo in wuce ishe DG Garba,

Da nas same shi,

Eyeh!

 

Rananan a ofis naz zo,

Wani a yag ga Mamman Sani,

Sai yac ce mani Mamman Sani,

Mi ya sa ba ku bar roƙo ba,

Ah!

 

Sai nac ce,

 

Sha’anin duniya kowa da abin da ya dame sa,

Sha’anin duniya kowa da abin da ya dame sa,

Wasu sun ce roƙo zunubi ne,

Wasu sun ce roƙo zunubi ne,

To amma ba mu musu,

Mun yadda da roƙo zunubi,

Amma matambayi ba ya ɓata,

Don haka na yi tambaya,

A faɗa mini rowa ladarta nawa?

 

Wai shi mai rowa ladassa nawa?

 

Mai rowa maƙiyin Allah ne,

Ba shi ganin Annabi,

Saboda azaba ɗai anka yi shi.

 

Kowas sami abin duniya,

Yaz zama ya cinye shi ɗai,

Da ya mutu ya san wahala –

Ta ɗauko gammo ta kai shi ƙasa.

 

Shi ɗai zai mutuwa,

A kwasai a saka rami,

A ƙyale shi ciki,

Walakiri ya iske shi gida,

Ya sa mishi sarƙa ta wuta,

Ya lanƙwashe hannunsa ciki,

Ya huje gaba nai hannun ya shige,

Ya huje baya,

Sai a faɗa mashi rowa tak kai shi haka.

 

DG na gode ma,

DG Garba,

Wanda ya samu kuɗi,

Ko da yaushe ya sauka gida,

Ka kama mu ƙwarai ka riƙe,

Yadda Allah ya yi ma sutura.

 

DG Garba,

Garba da ya samu kuɗi,

Ko da yaushe ya ɗauki ɗiyan jama’a,

Ka kama mu ƙwarai ka riƙe,

Yadda Allah ya yi ma sutura.

 

Awaikin dutsi ka gagari ‘yan yara ado,

Awaikin dutsi ka gagari ‘yan yara ado,

Kuma ka yi wa manyansu gwaram ga wuya.

 

Arna tsoron ka suke,

Ga yaƙi kai an ka sani.

 

DG na gode ma,

Sannu Habu ka kyauta,

Yadda kai wa Mamman Sani bahago.

 

Allah shi yi ma sutura,

Habu mai kwana da shiri,

Ah!

 

Alƙali Mustafa uban ɗakina,

Yadda yai mini ya kyauta min da yawa,

Domin Baba mai kwana da shiri.

 

Audu na Binji ya kyauta min,

Bam mance da Bala zaki ba,

Bala zaki ya kyauta min,

Bala zaki ya kyauta min da yawa.

 

Allah shi yi mai sutura,

Yadda yai wa Sani bahago,

Ah!

 

Almu na Jega ka kyauta min,

Alhaji Almu na Jega ka kyauta min da yawa,

Allah shi yi ma sutura yadda kau wa Sani bahago.

 

Da uban gari na gode ma,

Yusuf ka kyauta min.

 

Mu koma BK don in ga Habu babana,

Sannu DG ka kyauta min da yawa,

DG Garba,

Yadda kai wa Mamman gaishe ka nake,

Allah shi yi ma sutura yadda kau wa Sani bahago.

 

Yaƙi noman sarki!

 

Canjin rauji da kiɗa

 

Taimaka Rabbana,

Ya Jalla ka ceci ‘yan zamani,

Ikon Allah ka tserad da mu,

Ka Hana mu ɓata,

Ka ganad da mu gaskiya.

 

Taimaka Rabbana,

Ya Jalla ka ceci ‘yan zamani,

Inji mai waƙa uban Zainaba, Sani.

Abin mamaki bai kamaƙ ƙarewa malam,

Abin mamaki bai kamaƙ ƙarewa,

Sai kullum ƙaruwa za ya yi,

In kana yawo gari-wa-gari,

Inda duk ka shiga.

 

Taimaka Rabbana,

Ya Jalla ka ceci ‘yan zamani,

Ikon Allah ka tserad da mu,

Ka hana mu ɓata ka ganad da mu, gaskiya.

Abin mamaki bai kamat ƙarewa,

Inda duk kash shiga,

In kana yawo gari-wa-gari,

Sai ka iske mutum cikakken mutum,

Ka sami mutum kamak kamili,

Hannu na mutum, ƙafafun mutum,

Kai nai na mutu, idanun mutum,

In ka duba cikin zuciya tai,

Sai ka ga gwamma kura da shi,

Ka gane irin harkag ga sai Rabbana,

Sha’anin duniya wuya ag garai,

In ka yi kure akwai ‘yar ‘yar wuya.

 

Sai ka samu mutum kamaj jarumi,

In ka duba cikin zuciya tai,

Sai ka ga gwamma raggo da shi,

Sha’anin duniyag ga sai Rabbana.

 

Taimaka Rabbana.

 

Yo gaba malam in yi zance da kai don Allah.

 

Yo gaba malam in yi zance da kai don Allah,

Amma inji mai waƙa uban Zainaba,

Sha’anin duniya wuya ag garai.

 

Idan ka ga mutum kana ra’ayi nai, malam,

Wai kan da ku zan jiki dai da shi,

Na so ka yi bincike nai kaɗan,

Kuma ka bar dubin huska da kaurin jiki,

Kai dai ka yi binciken zuciya,

Da irin halin da duk ag garai,

Ka san cinikin ɗan Adam wuya ag garai,

Ko an bar ma sule goma,

A cikin naira rage ‘yab biyar,

Ka gane kana zaton faɗuwa wata rana.

 

Wasu sun yi gamon katar,

A cikin suɗi sun tsinci guru guda,

Ku tsaya ku raba shi kowa ya ci,

In anka raba a sam min ƙashi ni dai.

 

Wasu sun yi haƙo cikin rijiya,

Wai sun aza gargaza ta shiga,

Suka kamo talibambam guda,

Da anka taɓa shi yak kumbure.

 

Taimaka Rabbana,

Ya Jalla ka ceci ‘yan zamani,

Sha’anin duniya wuya ag garai, Sani.

 

Wasu sun ce roƙo wuta ag farai,

Zunubinsa yana da dama cike,

Amma in anka yi binciken zuciya,

Han na san, Ah!

Na san wani Sani,

Gwamma Sani da shi.

 

Ni na san wani gwamma dai,

Na san wani gwamma Sani da shi,

 

Taimaka Rabbana,

Ya Jalla ka ceci ‘yan zamani,

Ikon Allah ka tserad da mu,

Ka hana mu ɓata ka ganad da mu, gaskiya.

 

Ka ga ana wata,

Ga wata ta fita,

Inji mai waƙa uban Zainaba,

Wai mutum shi yi ma rowa ya yi fushi da kai,

Don Allah kak ka yi min rowa ka yi fushi da ni,

Idan kai min rowa kai fushi da ni,

Komi yaf faru kai kab biɗa,

Babu ruwan Mamman uban A’isha.

 

Kyauta sai Allah cikin lokaci malam,

Kyauta sai Allah cikin lokaci,

Shi ya ba ka uwa ya ba ka uba,

Shi yi ma mata ta yi ta haihuwa,

In an ce wane ɗan wane ne,

Kuma sai an ce uban wane ne,

Irin hikiman ga sai Rabbana,

Shi ɗai.

Taimaka Rabbana,

Ya Jalla ka ceci ‘yan zamani,

Ikon Allah ka tserad da mu,

Ka hana mu ɓata ka ganad da mu, gaskiya.

 

Alhaji Garba na Gwaggo ka taimaka,

Na gode ma,

Habu jikan Jatau a gaishe ka dai,

Ɗan Tabawa kana da halin yabo,

Allah ya biya ka don Rabbana,

Amin, inji mai waƙa uban Zainaba.

 

Magajin Ƙirgi Sani,

A gaishe ka na gode,

Wanda ban taɓa raina irin kuzarinsa ba.

 

Ummaru Boɗinga ya taimaka,

Yanda yai wa Aliko,

Wanda ban taɓa raina irin kuzarinsa ba.

 

Taimaka Rabbana,

Ya Jalla ka ceci ‘yan zamani.

 

(canjin rauji la kiɗa)

 

Gyara Jalla mafi girma,

Ya Allah ka kiyaye mu.

 

Yaƙi noman sarki,

Tafiya noman falke,

Ku riƙa dai yayana,

Kowa ya gaji bai saba ba,

Dole wan naƙi.

 

Tafiya noman falke,

A gwada domin noma,

Kowa ya san kowa.

 

Haba yara mu koma Agwada ya fi,

Haba yara mu koma Agwada ya fi,haba yara mu koma Agwada birni.

 

Tun ban zo Agwada ba,

Ana labarin Agwada kullum.

 

Tun ban zo Agwada ba,

Ana labarin Agwada kullum.

 

An ce Agwada dawa,

Kuma an ce Agwada gero,

An ce Agwada naira,

Kuma an ce Agwada maiwa,

An ce Agwada ilimi,

Kuma an ce Agwada shanu.

 

Da na je Agwada,

In gwada musu waƙa da kiɗa tsantsa.

 

Da na je Agwada,

In gwada musu waƙa da kiɗa tsantsa.

 

Mutanen Agwada,

Sun gwada mana aikinsu zuwa gona.

 

Dubi da mai ɗari hadda bakwai daidai,

Dubi da mai ɗari hadda bakwai daidai,

Suka bai wa Bahagon Indo,

Kuma ga wan tauzan ka daɗa,

Domin nono da siga Sani.

 

Ba ni koma zuwa gona,

Ba ni koma zuwa gona,

Na futa da yini rana,

Ah!

Idan na ji yunwa Agwada nay yi.

 

Ko ba ni ba,

Ni mai waƙa da kiɗa Sani,

Kowa ya ji yunwa,

A gwada masa hanyar Agwada birni,

In ka ji yunwa a gwada maka hanyar Agwada birni,

Da ka zo Agwada,

Su gwada maka shago da dawon gero,

Da nono da siga kai ɗai.

 

Haba yara mu koma Agwada ya fi.

 

Yaƙi noman sarki,

Inji Sani bahagon Indo.

 

Yaƙi noman sarki,

Inji Sani bahagon Indo.

 

Yaƙi noman sarki,

Inji Sani bahagon Indo.

Aikin tafiya,

Falke aka bar wa da mutane nai.

 

Sha’anin duniya,

Kowa ya bi hanyar da yake tsira.

 

Sha’anin duniya,

Kowa ya bi hanyar da yake tsira.

 

Ko waƙ ƙi ka da ɗa,

Ya gane ka da jikanka kana tawai,

Kuma ba ya da halin ya taɓa ma shi.

 

Sha’anin duniya,

Kowa ya bi hanyar da yake tsira,

Sakkon sallai,

Ba shi ke maishe ka Musulmi ba.

 

Mutum na salla,

Zuciyarsa ta zam ba ta Musulmi ba.

 

Amma inji Mamman bahagon Indo,

Amma inji Mamman bahagon Indo.

 

A bayar a rasa,

Ita ke hana yaro ka ji motsi nai.

 

A bayar a rasa,

Ita ke hana raggo ka ji motsi nai.

 

Allah wadaran samun raggo,

Bai ci ba bai sha ba,

Bai tsere wa abokai ba.

 

Amadun Rikiji ɗan Cindo,

Allah ya kiyaye ka,

Na gode ka taimaki gangata.

 

Yadda kai mini,

Ka taimaki gangata.

 

Sannu Audu Magajin Agwada sakko,

Tsartsatsa bahagon gulbi,

Ka ci gwani dud da jirage nai,

Na san ba ka barin bami.

 

Yara ina ɗan mutuwa Ada,

Mai fetur,

Na Haɗiza ka taimaki gangata.

 

Sale ɗan mai daji,

Allah ya kiyaye ka.

 

Mijin Manga na gode,

Ka taimaka wa ƙanin Indo,

Ban raina maka kyauta ba,

Ya Allah ya kiyaye ka.

 

Kansilan Agwada Umar,

Ya taimaki gangata,

Na gode.

 

Sani hayaƙi na gode,

Allah ya kiyaye ka.

 

Ummaru mai zani na gode,

Karkarak ku karakarar mata ce,

Inda kag ga maza to katarike su,

Alkla ya kiyaye ka,

Ka kyauta wa ƙanin Indo,

Sarkin maƙera na gode,

Eyeh!

 

Sani na Sarkin Maƙera na gaishe ka,

Ka taimaki gangata,

Haba yara mu koma Agwada ya fi,

Haba yara mu koma Agwada birni.

 

Ado mai shayi yadda yai mini,

Allah ya kiyaye ka,

Ya kyauta wa ƙanin Indo,

Allah ya kiyaye ka.

 

Mani DPOn Kwatarkwashi,

Mani DPOn Kwatarkwashi.

 

Sannu jijin Zainab,

Mijin Hajiya Rabi a gasihse ka,

Mani mai Allah.

 

Mijin Hajiya Rabi a gaishe ka,

Mani DPOn,

Mani DPOn Kwatarkwashi.

Eyeh!

 

Yara mu je yawo,

Kwatarkwashi ga Mani DPOn da gaishuwa.

 

Yara mu je yawo,

Kwatarkwashi ga Mani DPOn da gaishuwa.

 

Ya Allah shi yi ma sakayya,

Abin da kake malam.

 

Ya Allah shi yi ma sakayya,

Abin da ka wa Mamman,

Sannu mijin Zainab,

Mijin Hajiya Rabi,

Mijin Binta,

Gira sai Allah.

Mijin Hajiya Rabi,

Mijin Binta,

Gira sai Allah.

 

Dattijo sannu mijin Zaiban,

Na Adamu na gode da gaskiya.

 

Mani DPOn,

Sannu nake kun na wace,,

Sannu nake kun na wuce,

Riƙa ƙwarai,

Mani DPOn,

Yadda kai wa Sani na gode,

Riƙa ƙwarai.

 

Ku sa mana tamburan,

Ku sa mana tamburan,

Amma saboda Mani DPOn,

Ku sa mana tamburan.

 

Nahuce mu je yawo,

Nahuce gariu za ni,

Amma saboda mani DPOn,

Nahuce gariu za ni,

Amma saboda mani DPOn,

 

In ba shi a Nahuce,

Haba yara ku zo hanya mu wuce.

 

In ba shi a Nahuce,

Haba yara ku ɗau hanya mu wuce,

Kwatarkwashi.

 

Ina Mamman Rikiji?

Yara ina Mamman Rikiji Kwatarkwashi?

Yara Mamman Rikija,

Na Sa’adatu Sani ya gode,

Na Sa’adatu giwa sai Allah,

Yadda kai mini na gode da gaskiya.


Mani DPOn.

Post a Comment

0 Comments