Ticker

6/recent/ticker-posts

Karin Magana Mai Labari: Wani Shaƙo Daga Kare-Karen Maganar Hausa


Citation
: Hassan, H. and Yankara, M. M. (2021). Karin Magana Mai Labari: Wani Sha
ƙo Daga Kare-Karen Maganar Hausa. FUDMA Journal of Hausa Studies (FUDJOHAS), 1(1). Dutsin-Ma: Federal University Dutsin-Ma. P70-81

Karin Magana Mai Labari: Wani Shaƙo Daga Kare-Karen Maganar Hausa 

Hussaini Hassan, Ph.D
Sashen Hausa
Kwalejin Ilimi ta Tarayya,
Pankshin, Jihar Filato.
+234 703 9283 077
husssainihassan387@gmail.com 

Da
Muhammad Musa Yankara
Sashen Hausa
Jami’ar Tarayya Dutsin-ma,
Jihar Katsina.
+234 806 2367 496
esemwaiy12@gmail.com

Tsakure

Maƙasudin wannan takarda shi ne fitar da wani ɗan tsalli daga cikin sassan adabin Bahaushe don bayar da misalai ga ‘yan uwa ɗalibai domin ƙara faɗaɗa bincike da nazari. Nazarin ya yi ƙoƙarin bayyana nau’in karin magana mai labari a matsayin wani shaƙo daga cikin kare-karen magana na Hausa”. An tsara binciken ta hanyar garkuwa da misalan karin magana guda ashirin da bakwai (27) waɗanda tushen su labarai ne ko dai ya faru da gaske, ko kuma kunne ya girmi kaka domin a daddagi bagiren sosai da sosai, a cashe a fitar da tsaba da tsakuwa a ɗebe kokonto. Sakamakon nazarin ya tabbatar da cewa karin magana tamkar wani kogi ne da kowane mai nazari kan yi iya shiga ya ɗebo abin da yake so daidai buƙatarsa ya yi amfani da shi, kuma ya bar shi a nan. A ƙarshe aka shawarci ɗalibai da su faɗaɗa bincike a kan wannan nau’i na karin magana mai labari ta hanyar gwama na Hausa da na wasu harsunan.

 

1.0 Gabatarwa

Tunanin mutane da suke sarrafawa a fatar bakunansu wani yanayi ne da ke bayyanar da fasaha da hikimomin kimiyyar rayuwarsu da yadda suke cin gajiyarta. A kowane sashe na adabi, ana samun nazarce-nzarce masu tarin yawa, amma har yanzu haƙa ta ƙi cim ma ruwa na ganin an kai ƙarshe. Koyaushe aka buɗe ido ana ganin sabon binciken ilimi wanda masana da manazarta suke aiwatarwa da gudanarwa. Karin magana, magana ce mai tsawo wadda aka dunƙule ta, ta zama gajera cikin hikima, da zalaƙa kuma ta ƙunshi ma’ana mai yawa in za a tsaya a warware ta. Farfesa Abdullahi Bayero Yahya a wani darasin ajin digiri na uku, shekarar 2017 shi ya bayyana kalmar shaƙo da cewa kamar mutum ne ya yi nutso a kogi, to abin da ya ɗebo na daga ruwa a jikinsa shi ne shaƙo. A bisa hasashe ake kallon karin magana mai labari a matsayin ɗan wani abu da akan shaƙo daga cikin kogin karin magana na Hausa. Abin nufi dai, karin magana wani fanni ne mai faɗin gaske wanda yake tamkar kogi ne ga mai son nazari, ta yadda duk iya kwalfa da ɗiba, sai dai a ɗebo wani abu a bar saura. Don haka ne ma ɗaliban adabi ke ganin karin magana wani babban rumbu ne na kimshe hikimomin al’ummar Hausawa da ba zai taba ƙarewa ba komin yawan masu ɗiba a kowane zango na rayuwa.

 

1.1              Ma’anar Karin Magana

Garba, (2017) a wata maqala da ya rubuta mai taken “Nazarin Karin Maganar Hausa” ya kawo ma’ana daban – daban daga masana kan karin magana, wanda ya ce wasu daga cikin masanan da suka tofa albarkacin bakinsu dangane da ma’anar karin magana sun haɗa da: Finnegan (1970), Hassan (1981), Tudun wada (1982), Ɗangambo (1984), Guoling (1985), Umar (1987), Koko (1989), Yahaya, da wasu (1992), Aliyu (1996), Bichi (1997), Birniwa (2005), Junaidu da ‘Yar’aduwa (2007), Muhammad (2009), Hassan (2009), Gwammaja (2010), Koko (2011), da Ɗanhausa (2012), Bugaje (2014). Misali Finnegan (1970) ta ce: “Karin magana jerin kalmomi ne mai dubun hikima da zalaƙa wanda ke zuwa a gajarce, tare da ma’ana mai gamsarwa idan aka tsaya aka yi sharhi”.

Sai kuma Tudun wada (1982) wanda yake ganin ba wani abu ne karin magana ba illa: “magana ce wadda ake lanƙwasa ta, ta yi daɗin ji a kunne ta kuma yi ma’ana”.

Shi kuwa Tudun Wazirci (bkw) ya ƙara da cewa: “karin magana wani lafazi ne mai ƙunshe da hikima, wanda yake ƙunshe da ma’ana biyu, watau bayyananniyar ma’ana (ma’ana ta zahiri), da kuma ɓoyayyiyar ma’ana (ma’ana ta baɗini)

A taƙaice za a iya cewa karin Magana tsararren zance ne wanda yake zuwa a gajarce na hikima da zalaka tare da bayar da ma’ana gamsasshiya mai fadi, mai yalwa, musamman in aka tsaya aka yi bayani daki-daki. Wato karin magana takaitacciyar magana ce `yar kil wadda ta kunshi hikima da zantukan ma’ana.

1.2              Asalin Karin Magana

Kusan a iya cewa kowacce al’umma a duniya na da irin nata karin maganganun. Misali ɗauki harshen Larabci a inda Bahaushe ke cewa “gani ya kori ji” balarabe kuma cewa yake “laisal al – khabar ka al – mu’ayanah”, to haka dai abin yake. To amma dangane da batun ko yaushe ne aka fara karin magana da kuma ko wane ne ya fara karin magana, to “nan fa ɗaya wai an ce da shege ina ubanka”?, don kuwa a bisa bin diddigin masana tarihi na adabi da al’adu da harshe ba a sami wani takamaiman rubutaccen abu dangane da asalin samuwar sassan adabin baka ba, sai dai hasashe. A sakamakon sanadiyar faruwar wani abu sai wani abu ya samu, to wannan shi ya faɗa kan karin magana (Ɗangambo, 2008).

 Masana sun ce kusan zai yi wuya wani ya bugi ƙirji ya ce ga wanda ya fara karin magana ko ga lokacin da aka fara, wato kamar yadda yake da wuya a ce ga wanda ya fara magana a duniya, to haka shi ma karin magana. Kusan ai ko shi kansa harshen ma wato magana, hasashe ne da ra’o’i birjik kan asalin samuwarsu a duniya, wanda yayin da wani ya kira sunan ra’insa da suna Bow –bow, wani kuma da pooh – pooh ya kira sunan nasa ra’in, wani ya ce ding – dung, wani kuwa ya ce ai tun ran gini ran zane, magana ta fara ne daga waƙa, wato daga ran da aka haifi yaro ya fara kuka ai waƙa ce, wato ra’in “tarara – bun – diya”. Wasu ko suka ce atafau abin na da alaƙa da addini.

 To ashe kuwa ke nan a iya cewa an fara karin magana tun lokacin da ɗan Adam ya fara sa hikimomi da fasahohi cikin managarsa wanda ya ke tun kaka da kakanni ne. Sai dai akwai hasashe da dama kan waɗanda ake jin su ne suka fi yin karin magana ko haɓaka karin magana a Hausa.

Hasashe na nuna cewa mata, da ‘yan daudu, da maroƙa ne suka fi kowa karin maganar Hausa. Dalilan da ke nuna mata a cewar Tudun wada (1982) ya ce wai kusan kullum zaune suke a gida in ka ɗauke ‘yan ƙananan aikace-aikacen gida ba sa wani aikin cas bare as, sai dai a kawo musu su dafa su wanke goma su tsoma biyar, ba sa yin faɗi-tashin neman abinci irin na maza, kai in har ma ka ga sun fita to da dalili wani abu ne ya taso na buki ko kuma wata larura ta zuwa asibiti. Wannan ya sa da sun haɗa ‘yan aikace-aikacensu na gida sai su zauna zaman hira, wannan ne ma ya sa Bahaushe ke cewa “ƙarfin mata sai yawan magana” to cikin yawan maganar ne suke jefa ‘yan karin maganganu wani lokacin ba ma tare da sun sani ba, shi ke nan fa sai wani ya ji ko wata, wanda suma da sun ɗora a gaba sai ka ji wannan karin magana ta yaɗu wanda ya ji ya ƙara yaɗa ta.

Wata madogarar kuma ita ce ta fuskar kishi. Bisa al’ada mata ba sa son kishiya ko kaɗan, wannan ya sa ma suke kiran kishiya da cewa tunkiya. Kishi kumullon mata in ya motsa sai an haras, wannan ya sa a zamantakewarsu da kishiya suke jefa wa junansu ‘yan maganganu na habaici da karin magana don muzantawa da tunzurawa. Tabbaci game da wannan shi ne samuwar karin maganganu da ke nuna kishi kamar haka:

i.                                   Ba zafi barkonon taro a idon kishiya.

ii.                                 Ban gane ba an doki ɗan kishiya.

iii.                               Da alheri uwar kishiya ta hau kura.

iv.                               Da zaman banza gara aikin kishiya ko tsine mini aka yi na samu.

v.                                 Haka tara inji kishiyar mai mageduwa.

vi.                                Wada da wadaƙa, ta da kai da ɗan kishiya.

vii.                             Ya na iya da abin da ya gagari wuta inji kishiyar ƙonanniya.

viii.                           Ku taya ni figa, uwar kishiya ta zama kaza.

Idan kuma aka juya ga ɗan uwan ɗayar, wato Ɗandaudu wanda shi ma bisa ga hasashe an nuna cewa yana ɗaya daga cikin waɗanda suke ƙirƙiro karin magana. Wannan kuwa shi ma bai rasa nasaba da yawan maganarsu da kuma kasancewar su cikin mata a kodayaushe ba.

Rukuni na gaba shi ne na maroƙa, wanda su ma ba baya ba ne wajen taka mahimmiyar rawa ga ƙirƙiro ko samuwar karin magana a Hausa ba. Su maroƙa su ne waɗanda suka riƙi roƙo a matsayin sana’a, wannan roƙo kuwa kan iya zama roƙon baki ne irin waɗanda ake cewa maroƙan baki ko kuwa masu amfani da kiɗa ne, duk dai harka ce ta magana wanda wannan ne ya sa suke da yawan karin maganganu. A cikin maganar ne sukan yabi wanda suke son abinsa. Don haka kusan ya zama dole su yi amfani da kalamai masu armashi wanda karin magana na ɗaya daga ciki. To fa a nan ne za ka ji karin magana na fita, wani lokacin ba tare da ma sun sani ba. Duba kirarin da sukan yi wa jarumai ko yabon gwanayensu za ka iske karin maganganu ne a ciki.

 Shi kuwa Gusau (2003) a nasa bayanin, cewa ya yi irin waɗannan zantukan karin magana sun samo asali ne lokacin da Bahaushe ya fara yin farauta yana kama namun daji, idan wani ya yi ƙoƙari ya kama dabba ko ya kashe ta, a wajen wannan yunƙuri na bajinta yakan faɗi wasu lafuzza na maganganu na kuranta kai waɗanda suka ƙunshi hikima ko wasu kalmomi da suka yi kama da “karin magana”. To, a na ganin daga irin waɗannan maganganu ne aka fara ƙirƙirar karin magana.

Koma dai ya abin yake, a ƙarshe dole a tafi bisa ga ra’ayin nan na tun ran gini tun ran zane. Wato babu wanda zai iya cewa shi ne asali ko mafarin karin magana, kowa sai dai ya buɗe ido da kunnuwa ya ji ana yin sa.

 

1.3              Rabe–Raben Karin Magana a Hausa

Garba, (2017) ya bayyana cewa dangane da ire – iren karin magana a Hausa, akwai masana da dama da suka tofa albarkacin bakinsu. Sai ya kawo misali da Hassan (1981), Ɗangambo (1984), Guoling (1985),Yahaya, da wasu (1992), Aliyu (1996), Hamisu (2006), Junaidu da ‘Yar’aduwa (2007), Hassan (2009), Tudun Wazirci (bkw). Sai dai kusan kowane da yadda yake kallon yadda ya kamata a rarraba karin magana. Wasu na la’akari da lokacin samuwar karin maganar ya yin rarraba su, ya yin da wasu kuma ke la’akari da siga ko tsari ta wannan karin maganar. Ko kuma a yi rabon ta la’akari da jigogin karin maganar. Amma dai a wannan takarda an kawo dukkan rabon da manazarta da masanan suka yi ne a zube, kan yadda aka samar da kowane nau’i na karin magana. Ga su kamar haka:

·                     Karin magana mai “tambaya da amsa”.

·                     Karin magana mai “labari”.

·                     Karin magana mai “in ji”.

·                     Karin magana mai “an ce”.

·                     Karin magana mai “ya fi” ko “ta fi”.

·                     Karin magana mai “kowa”.

·                     Karin magana mai “nasiha”.

·                     Karin magana mai “habaici”.

·                     Karin magana mai “Hausawa sun ce”.

·                     Karin magana kafin zuwan addinin Musulunci.

·                     Karin magana bayan zuwan addinin Musulunci.

·                     Karin magana bayan zuwan Turawa. Misali:

·                     Karin magana mai ɗauke da gajeruwar Jumla.

·                     Karin magana mai “ɓangare biyu”.

·                     Karin magana mai “alaƙa da tarihi”.

·                     Karin magana mai mai “faɗar gaskiya”.

·                     Karin maganar “ko oho”.

·                     Karin maganar da ta fara da “In” a farko.

·                     Karin maganganu masu daɗaɗɗen asali.

·                      Karin maganganu da suka samu a sanadiyyar la’akari da rayuwa.

·                     Karin magana mai mutumtarwa.

·                     Karin magana mai kamantawa.

·                     Karin magana mai kanbamawa.

·                     Karin magana mai korewa.

·                     Karin magana mai tabbatarwa.

·                     Karin magana mai nuna sana’a.

Daga cikin waɗannan rassa ne maƙalar za ta yi magana a kan ɗaya wato karin magana mai labari.

 

2.0              Karin Magana Mai Labari

Wannan wani nau’i ne na karin magana wanda a bisa asali ya samu ne ta hanyar wani abu da ya faru. Ire-iren waɗannan karin maganganu sukan samo asali ne daga wani labari wanda ya faru da gaske, ko kuma wani labari da aka ƙirƙire shi wanda bai faru da gaske ba, ko kuma labarin da aka same shi daga wata tatsuniya, (Gwammaja, 2018). Shi irin wannan karin maganar da wuya a fahimci abin da ya sa gaba ko abin da ake nufi da shi, idan ba a san asalin labarin da aka samar da karin maganar daga shi ba. Domin haka ana fahimtar karin maganar ne idan an san labarin abin da ya faru wanda ya haddasa samuwar wannan karin magana. Wannan takarda kamar yadda aka bayyana a baya wajen gabatarwa za a kawo irin waɗannan karin maganganu tare da bayyana yadda labarin asalinsu yake. Kaɗan daga cikin misalan da wannan takarda ta yi ƙoƙarin bincikowa sun haɗa da:

1.                  Saurin Tagumbi Saurin Banza.

2.                  Sammakon bubukuwa

3.                  Gyaɗar Dogo.

4.                  Biɗar Gatarin Arne.

5.                  Sautun Mahaukaciya.

6.                  Adashen Balaraba.

7.                  Adashen Uwar Nuhu.

8.                  Isar ƙadagi Isar Banza.

9.                  Cin Daƙuwar Buzu.

10.              Faɗan Gwaggo a Kofa.

11.              Sanin Damisar Bunu.

12.               Jiran Gawon Shano.

13.               Gaba ta Kai ni Gobarar Titi a Jos.

14.               Rufin Kan Uwar Daɗi/Lulluɓin Taladan.

15.               Zuwan Fara Garko.

16.               Lissafin Dokin Rano.

17.               Dare Mahutar Bawa.

18.               An Yi Daidai, Sayen Wandon Bafullace.

19.               Fargar Jaji.

20.               Jifan Gafiyar Vaidu.

21.               Ƙunar Baƙin Wake.

22.               Ɗaukar Ruwan Ɗan’amo.

23.              Gamon Katar

24.              Sayen Dusar Kwarto

25.              Biyar biyu ba ta goma

26.              Taka Wutar Ungulu

27.              Ana so Ana Kaiwa kasuwa.

Domin fito da ma’anar muƙalar, ga bayanin kowane daga cikin karuruwan maganar da aka ciro da tare da dalilan amfani da su a harshen Hausa.

 

2.1              Saurin Tagumbi Saurin Banza

Wai wani mutum ne da matan sa guda huɗu amarya da uwar gida, da turaki da kwari. Ita amaryar ita ce mai suna Tagumbi. To a bisa al’ada sukan je gona su ɗebi amfanin gona, amma akan ware wata rana da za su je. Sai ranar kwanan amarya ya faɗa don haka sai mijin ya gaya mata, kan ta yi sammako ta je don kafin kishiyoyinta su iso ta tara da yawa, saboda ya fi son ta samu mai yawa. Da asubahin fari amarya ta fita ba tare da ta sanar da sauran matan ba, sai bayan ta tafi da daɗewa ya zo ya faɗa wa uwargida da turaki, da kwari suka fito suna sauri. Bayan sun kusa kaiwa gona sai suka haɗu da amarya, ita da ta je amma ta juyo, suka tambayi Tagumbi lafiya? sai ta ce “ai ta manta da laujen da za ta yanki shinkafar, domin haka za ta koma gida ne ta ɗauko”. Ai ko kafin ta dawo sun tara shinkafa mai yawa sai saura kaɗan. To wannan shi ne idan mutum saboda sauri ya mance wani abu muhimmi sai a ce wannan ai shi ne saurin Tagumbi saurin banza.

 

2.2              Sammakon Bubukuwa

Bubukuwa tsuntsuwa ce wadda kan yi sammako da sassafe duku-duku, ko ma ka ce da assalatu ta tafi bakin ruwa kiwo amma kuma ba ta fara kiwo sai rana ta take, bayan ƙwari da dukkan abin ruwa sun koma. Da yamma sai ta tafi can kan tudu ta kwana. Wannan ya zama sammakon banza domin ga shi ta fito tun safe amma ba ta fara kiwo ba sai bayan ƙwari sun koma na ruwa sun shige ruwa wanda ya zama sammako marar amfani. Ana amfani da shi lokacin da mutum ya kasa moriyar amfanin wani abu lokacin da ya dace, sai bayan lokaci ya ƙure.

 

2.3              Gyaɗar Dogo

A nan ma cewa aka yi wani mutum ne ake bin sa bashi, sai ya ce in amfanin gonarsa ya yi zai biya. Ya yi ta karvar bashi da zummar in an sare amfani gona zai biya. Sai ya shuka gyaɗa, ga shi kuma bashin yana da yawa. To a she a gonar bai sani ba varayi wata rana sun yiwo satar kuɗi sun zo gonar sun binne. Da gyaɗa ta nuna ya zo farɗa, yana tona rami guda sai ya ga kuɗi. Bugu da ƙari ya samu amfani mai yawa, ga kuma kuɗin da ya tono, ya biya bashin da ake binsa duka har ya rage saura. Idan mutum Allah ya taimake shi ya samu mafita kan wani al’amari akan ce Allah ya masa gyaɗar dogo.

 

2.4              Biɗar Gatarin Arne

Shi kuma wannan kamar yadda aka sani galibi shi arne kullum gatarinsa na kafaɗarsa. An ce wani arne ne ya zo yana ta faɗan ina gatarinsa yake, ya manta da cewa yana nan a kafaɗarsa. Daga nan ne in mutum ya manta yana neman abu bayan abun na gare shi ko ma a hannunsa akan ce wannan ai shi ne biɗar gatarin arne. Ga abu a hannunka kana ta nemansa har da faɗa.

 

2.5              Sautun Mahaukaciya

Mahaukaciya ce ta ga za a kasuwa kowa na ba da nasa sautun, wannan ya ce ga shi a sayo min abu kaza, wannan ya ce a sayo min abu kaza na kaza. Sai ita ma ta ɗauko kuɗi ta ce ga shi. Aka ce “me za a sayo miki” sai ta ce “ni na sani?”. A wata faɗar kuma aka ce ta ce “komai”. A wani labarin kuma cewa aka yi ta ce “a sayo mata nama, amma ban da ƙashi ban da tsoka ban da kitse ban da jijiya”. Idan mutum ya yi abin da shi kansa bai san mene ne ba sai ace masa ya yi sautun mahaukaciya.

 

2.6              Adashen Balaraba

Ita dai Balaraba ta ga matan unguwa sun shirya adashe, aka taya mata sai ta ji kunyar ta ce ba ta yi don kar a ga kasawarta, sai ta yarda za ta yi duk da cewa ta san ba ta iya zubi, don ba ta da sukuni kamar sauran matan, domin haka da lokacin zubi ya yi sai ta aiki ‘yarta maƙwabta ta ranto mata kuɗi sai ta zuba, da wani lokacin zubin ya yi sai ta sake aika wa wajen wasu daban aka ranto mata kuɗi ta zuba. Haka ta yi ta yi har lokacin ɗauka ya zo da ta kwasa sai ta rarraba wa waɗanda ta yi ta karɓo kuɗin su tana zubi. Da ‘yar ta ce to ke inna ba ki samu ba, sai ta ce ba dai mun shiga mu ma an yi da mu ba.

 

2.7              Adashen Uwar Nuhu

Akwai wata mace da ake kira uwar Nuhu, wadda ta shiga adashe irin na mata. Da shigar ta sai ta yi sa’a aka ba ta kwasar fari. Da lokacin zubi ya yi aka zo karɓa, don a haɗa a ba wata, sai ta ce ai ita ta fita adashen tuntuni. Wannan karin magana mata sun fi amfani da shi in suna son nuna wa mutum ya kasa rama alkhairin da aka masa musamman wajen rikicin biyan buki.

2.8              Isar Ƙadagi Isar Banza

Wani mutum ne mai suna Ƙadagi, wanda shi a kullum yakan yi kyauta ne da abin da ba nasa ba, saboda isa. Hausawa na amfani da wannan karin magana idan mutum ya yi kyauta da abin wani ko kuma yana nuna iko da abin da ba nashi ba sai a ce isar ƙadagi isar banza.

 

2.9              Cin Daƙuwar Buzu

 Wannan na kusan ɗaya da sayen sabulun Ba’auzini. Wai buzu ne ya sayi wani abu da ake yi da toka. Ya gan shi kato a cure ya ɗauka daƙuwa ce, ya kira yarinya ya ce mata ke ban daƙuwa. Sai ya ba ta kuɗi ta bashi. Ita kuma ba ta ce masa ai ba daƙuwa ba ce. Da ya tafi sai ya fara ci ya ji abu ba daɗi. To don kar ya yasar, ya yasar da kuɗinsa sai ya ci gaba da ci, yana rufe ido, wannan shi ake cewa cin daƙuwar buzu. Wasu kuma cewa suka yi Ba’auzini ne ya sayi sabulu ya ɗauka abin ci ne ya kama ci, ya ji ba daɗi. Ba ya son kuma ya zubar yana ganin ya yi asarar kuɗinsa. Ana amfani da wannan karin magana in mutum yana amfani da abu a bisa dole ba da son ransa ba.

 

2.10          Faɗan Gwaggo a Kofa

Wai wata tsohuwa ce ta ci kwalliya irin ta yara ‘yan mata ta sa takalmi coge ta yi shafe-shafe irin su jan baki da sauran su kwalliya ta yara, ta shiga cikin birni. Tana tafiya sai ta haɗu da yaran birni suka yi ta mata ihu da dariya, ba ta kula su ba. Sai bayan da ta dawo gida ƙauye, wato garin su sai ta haɗu da wasu yara na wasa sai ta hau su da zagi da duka wai yara sun mata ihu a cikin birni. To daga nan ne aka sami wannan karin magana in mutum ya tasamma faɗa ba a inda ya dace ba sai a ce wannan ai shi ne faɗan Gwaggo a Kofa.

 

2.11          Sanin Damisar Bunu

Wai an ce shi kuma wannnan karin maganar ya samo asali ne daga wani da ake kira Bunu. Wanda aka tambaye shi ko ya san damisa ya ce eh, aka ce ya take. Sai ya ce tana nan jikin ta dabbara-dabbara kamar jikin mussa, wato kuliya. Sai aka ce eh lalle ka san ta, sai ya ce tana ma da ‘yan ƙahonni. Sai aka bushe da dariya aka ce, ya san ta amma ba sosai ba. Shi ne in mutum bai san abu sosai ba sai a ce ya wa abin sanin damisar Bunu.

 

2.12          Jiran Gawon Shano

Wannan kuma an ce shanu ne za su kiwo sai suka ga gawo, wani ita ce ne mai ‘ya’ya wanda ‘ya’yan a wajen dabbobi abu ne mai daɗi, kamar ka ce mayunwaci ne a ƙasar Hausa ya samu damammiyar fura da nono kindirmo, ko ya samu tuwon laushi miyar kuɓewa da man shanu da yaji da naman rago. To amma fa shi gawo sai iska ta ɗan kaɗa yakan faɗo. Domin haka, ba tabbas ba ne cewa zai faɗo. Sai kawai shanun nan suka ƙi tafiya kiwo suka zauna jiran in ɗan gawon nan ya faɗo su ci. Har dai suka gaji, su ba su je kiwo a ranar ba, shi kuma gawo bai faɗo ba. Shi ne Bahaushe ke amfani da wannan karin maganar in mutum ya tsaya jiran abin da ba shi da tabbacin samunsa. Maimakon ya tafi ga wanda yake da tabbaci.

 

2.13               Gaba ta Kai ni Gobarar Titi a Jos

Wai wata ce ana ce mata Titi, wuta ta kama ɗakinta ta yi gobara kusan komai nata ya ƙone wuta ta cinye. Mutane suka yi ta zuwa suna mata jaje, duk wanda ya zo jaje yakan ɗan zo mata da wani abu, wani ya kawo riga wani ya kawo zani mai abinci na kawo wa, mai kawo kayan amfanin gida ya kawo har aka haɗa wa Titi kaya sama da abin da gobar ta cinye. Sai ta ce wannan gobara ai ni gaba ta kai ni. Wato ta samu abu sama da wanda take da shi. To shi ne ya zama karin magana Hausawa na amfani da shi in sun so nuna yadda wata asara ta juye zuwa samu ko amfani.

 

2.14          Rufin Kan Uwar Daɗi/ Lulluɓin Taladan

Uwar Daɗi wata dattijiya ce mai tsananin sakarci. Wata rana ta fito za ta je maƙwabta daga ita sai zane ga ba ɗankwali ba mayafi, ko ma ka ce ɗaurin ƙirji. Sai kawai ga surukinta tare da abokansa sun doso wajenta, can gefe kuma ga taron jama’a suna zaune suna hira. Da ta ga sun yi ido huɗu da surukinta cikin wannan hali, sai kunya ta kama ta. Saboda haka, sai ta cire zanen da take ɗaure da shi ta rufe kanta da shi ta bar gabanta fayau a gaban surukinta. Wannan ne ya sa Bahaushe ya ɗauki wannan labari ya mayar da shi karin magana yake amfani da shi in ya so nuna cewa mutum ya bar abin da ya fi dacewa ya tafi zuwa ga wanda ba shi ya dace ba, ko bai kai shi muhimmanci ba. Wasu ma kan ce rufin kan uwar daɗi gabanta babu kariya ko lulluɓin Taladan.

 

2.15          Zuwan Fara Garko

Wai wata rana ne fari suka dira cikin wani gari da ake kira Garko da nufin yin ɓarna. Amma da suka isa garin sai suka tarar har an tattare amfani an sanya cikin rumbu an rufe. Domin haka sai farin suka kama hanyar da suka fito, amma sai mutanen garin suka riƙa kama farin ba tare da sun bari sun kai labari ba, suna cinyewa. Wannan karin magana shi ne Hausawa ke amfani da shi in sun tashi nuna wani ya je neman wani abu amma maimakon ya samo sai ya rasa nasa. Ko ma ya halaka a can, kamar yadda farin suka halaka.

 

 

2.16          Lissafin Dokin Rano

Rano bawan wani sarki ne mai yawan dawakai. Wata rana ya je kiwo sai ya hau doki ɗaya. Lokacin dawowa gida ya yi, Rano sai ya ƙirga dawakin don ya tabbatar ba a bar ko ɗaya a baya ba. Ko da ya ƙirga sai ya ga babu ɗaya, sai ya sauko daga doki don ya duba ko ya je wani waje ne, amma bai gan shi ba. Sai ya komo ya sake ƙirgawa ya ga sun yi daidai, amma da ya sake hawan dokinsa ya ƙirga sai ya ga kuma ba su cika ba. Bai san cewa shirme yake yi bai ƙirgawa da wanda yake saman sa ba. Akan yi amfani da wannan karin magana idan mutum yana shirme a cikin lissafi.

 

2.17          Dare Mahutar Bawa

Shi kuma wannan an gina ta ne kan labarin wani bawa da ya taɓa katoɓara a kunnen maigidansa. Shi dai wannan bawa an ce kullum ba shi da hutu cikin aiki yake, sai dai in dare ya yi yakan je ya kwanta kafin safiya ta waye ya koma kan aiki. A haka ne wata rana ya yini yana aiki ya matsu dare ya yi ko ya kwanta ya huta. Da dare ya yi ya zo kwanciya sai ya ce “dare mahutar bawa ko ubangida bai so ba”. Ashe ubangidansa na kusa kuma ya ji abin da ya faɗa. Domin haka nan take ya umarci bawan nan da ya je gulbi ya ɗauko ruwa kai/sau goma. Sai bawan nan ya fahimci cewa ubangidansa ya ji abin da ya ce. Domin haka da ya ƙare ɗiban ruwan ya zo ya kwanta sai ya ce “dare mahutar bawa in ubangida ya so”.

 

2.18          An yi Daidai, Sayen Wandon Bafullace

 Wannan kuma labarin na cewa wai wani Bafullace ne ya je kasuwa don ya sayo wando. Da isar sa shagon farko, sai ko ya ga wandon da yake so. Ya tambaya nawa wando? Aka ce naira biyar (5), ya ce an yi daidai, da ma su kaɗai ne a cikin aljihun amshi ga su. Hausawa na amfani da wannan karin magana idan an so a nuna cewa faɗuwa ta zo daidai da zama.

 

2.19          Fargar Jaji

Shi kuma wannan an ce wani mayaƙi ne Jaji wanda a saboda tsananin shirinsa har layar ɓata yake da ita. Wadda in ana yaƙi in ya taɓa ta sai ya ɓace. Wata rana aka je yaƙi, amma Jaji ya manta da cewa yana da layar ɓata, har dai aka sare masa kai can sai ya tuna bayan har an riga an sare kan. Wai kafin ka ce me ana sare kan sa sai ya taɓa layar sai ga kan Jaji yana ɓingirawa ɓingir-ɓingir, amma gangar jiki kuma ta ɓace. Wato ya makara, bai yi amfani da layar ba a lokacin da ya dace. To shi ne in mutum ya tashi yin abu bayan abin ya wuce akan ce wannan kuma ai ya zama fargar Jaji.

 

2.20          Jifan Gafiyar Ɓaidu

Shi dai Ɓaidu an ce mafarauci ne. Wata rana ya je farauta sai ya kama gafiya, har ya juya zai tafi sai ga wata kuma ta fito daga ramin a guje, sai Ɓaidu ya kai mata jifa da ta hannunsa da nunin ya buge ta ya haɗa ya kama duka biyu. Sai ita ma ta ware ta bi ‘yar uwarta suka gudu, ya yi biyu babu, ba wadda ya kama ba wadda yake son ya kama ɗin. Shi ne mutane ke amfani da wannan karin magana in an ga mutum na neman sakin wanda ke hannun sa bayan bai riga ya samu wani ba.

 

2.21          Ƙunar Baƙin Wake

Shi kuma wannan wani bawan sarki ne mai suna baƙin wake. To shi sarkin nan yana da wani ɗa wanda shi maimakon ya hau doki irin yadda sauran ‘ya’yan sarki ke yi, a’a shi bawa yake hawa. Bawan ya goye shi ya zaga da shi duk inda yake so saboda isa da ƙasaita. Dukkan bayin nan abin na damunsu. Sai ranar nan abin ya faɗo kan baƙin wake, wato yau shi za a hau. Domin haka yana ɗaukar ɗan sarkin nan sai ya ruga ya faɗa da shi cikin wutar katsi da ake dafa baba na yin rini. Ya kuma riƙe ɗan sarkin nan suka ƙone gaba ɗaya ana kallon su ba mai shiga. Ɗan sarki ya yi ta ihu, ina a banza suka ƙone da shi da ɗan sarki. To shi ne in mutum ya ta shi hallaka wasu ko wani, duk da cewa shi ma zai mutu tare da wanda yake son ya kashe, shi ne ake cewa ƙunar baƙin wake.

 

2.22          Ɗaukar Ruwan Ɗan’amo

 Shi kuma wannan wai wani tsoho ne da ake cewa Ɗan’amo wanda yake son ya samu wani aiki na lada da zai riƙa yi. To amma kuma ba shi da ƙarfi na yin wani aiki mai wahala, saboda haka sai ya zaɓi da ya ji an yi mutuwa ya je ya ɗebo ruwa a bokiti ya kai ya ce ga shi a wanke mamaci da shi. To shi ne aka samu karin magana, wanda in an yi wani abu da mutum ke neman shiga abin da zai kai shi ga mutuwa sai a ce kai kar Ɗan’amo ya ɗauko maka ruwa. Ko kuma a ce yanzu Ɗan’amo ya ɗauko maka ruwa.

 

2.23          Gamon Katar

Katar wani mutum ne mai aikata saɓo, ɗan fashi ne. Ya kashe mutum har ɗari ba ɗaya. Sai shiriya ta zo masa ya ce yana so ya tuba in Allah zai gafarta masa. Sai ya sami wani malami ya ce masa, kaji-kaji irin aikina, amma so nake na ji ko in na tuba Allah zai gafarta min. Sai malamin nan ya ce kai wannan aiki naka ya yi muni, mutum ɗari ba ɗaya, ai ba kai ba rahama, ba abin da Allah ya ƙi kamar kashe ran mumini ba tare da haƙƙi na shari’a ba, tafi-tafi ba ni wuri kar laifinka ya shafe ni. Ƙatar na jin haka sai ya ce ah to ai tun da haka ne, bari na cike na ɗarin, sai ya kashe malamin. Duk da haka Ƙatar bai haƙura ba sai ya sake zuwa gun wani malamin ya bayyana masa halin da yake ciki. Sai malamin ya ce masa ai Allah mai gafara ne in ka tuba Allah zai gafarta maka. Sannan in ka tuba akwai wani gari na tubabbu da za ka je can ka yi ta ibada in ka mutu sai ka shiga aljanna. Sai ya ce to ya ji ya gode, Ƙatar ya tuba ya kuma kama hanya zuwa garin nan da malamin ya faɗa masa. Ya kusa isa garin sai Allah ya ɗauki ransa, Ƙatar ya faɗi ya mutu. Sai mala’ikun rahama da na azaba suka iso waɗannan na cewa nasu ne, waɗannan na cewa nasu ne. Sai nan kuma Allah ya aiko wani mala’ika don ya raba musu gardama, aka ce a auna da inda ya baro da inda za shi ina ya fi kusa. Sai aka ga inda ya nufa ya fi kusa. Sai aka ce to na mala’ikun rahama ne. Mafarin amfani da wannan karin magana shi ne idan mutum ya shiga tsaka mai wuya kuma ya samu fita.

2.24          Sayen Dusar Kwarto

Wannan karin magana ya samu ne lokacin da wai wani mutum da matarsa bayan ya tafi wurin neman abinci wajen fatauci kullum sai abokinsa ya zo wurin matar. Sai rannar nan mijin matar ya nuna wa abokin ai zai yi tafiyar nan da ya saba. Da ya tashi sai ya tura matar gida ya zauna shi kaɗai. Can sai kwarton ya zo kai tsaye ya shigo gidan sai mijin ya fito ya ce me ya kawo ka sai ya ce dusa na zo saya. To shi ne in mutum ya yi wani rashin gaskiya aka kama shi amma ya waske sai a ce yay i sayen dussar kwarto.

2.25          Biyar Biyu ba ta Goma

An ce wai wani mutum ne yake da ‘ya’ya huɗu sai ya auro wata mace ita kuma da ta zo sai ta zo masa da ‘ya’ya huɗu sannan kuma ta haifa masa ɗaya. Idan an haɗa da ɗan matar da nasa huɗu sun zama biyar ita ma idan ta haɗa da na mijin da huɗun sun zama biyar amma kuma da za a haɗa biyar da biyar ɗin ba za su zama goma ga kowannen su ba. Shi ne ake cewa biyar biyu ba ta goma. Ana amfani da shi idan an ga wani mutum ya tashi nuna isa kan wani abu wanda duka ba nasa ba ne.

2.26          Taka Wutar Ungulu

Karin maganar ta samo asali wai lokacin da ɓera ya ga ungulu za ta taka wuta, sai ya ce mata ungulu za ki taka wuta. Sai ta sa ƙafa ta taka ta ce masa “an taka ɗin ina ruwan ka”. Da ungulu ta ji zafi sai ta fitar ta ce “an ɗauke kuma an ƙi a taka”. To shi ne in mutum zai yi wani abu aka hana ya ƙi bari, bayan ya aikata sai ya yi nadama nan da nan sai a ce ya taka wutar ungulu.

2.27 Ana so ana kai wa kasuwa

Shi kuma wannan karin maganar labarin samuwarsa ya nuna ne cewa wai wata rana ne wata Bafulatana ta xauki nono za ta kai kasuwa, sai ta haxu da wata mahaukaciya ta ce mata “ke zo, kawo sauke, zuba na xari” Bafulatana ta zuba tana rawar jiki, ta sake ce mata “to shanye” Bafulatana ta shanye, ta sake ce mata “qara na xari” ta zuba ta sake ce mata “shanye” Bafulatana ta shanye. Sai ta ce mata “to xauke tafi, a she ana so ake kai wa kasuwa”. To shi ne asalin samuwar wannan karin magana da Bahaushe yake cewa ana so ana kai wa kasuwa. Wato idan mutum ya na son abu amma yana nuna kamar ba ya so, yana fulako shi ne sai a ce masa oh kana so kana kai wa kasuwa, kana so kana nuna kamar ba ka so.

3.0 Kammalawa

Hikimar Hausawa ta cewa “zama wuri ɗaya tsautsayi in ji kifi” shi ya tabbatar da zancensu na da koyo a kan iya. A wannan takarda kamar yadda bayani ya gabata an ga cewa karin magana wani fannin nazari ne a farfajiyar adabin baka wanda ke da faɗin gaske. Kowane rabo aka ɗauka a cikin waɗannan ya isa a yi bincike mai yawa a kansa har a samar da abin da ake hanƙoron samu. Kuma kamar yadda aka sani kowane harshe na da karin magana duk da dai in dambu ya yi yawa ba ya jin mai. Amma duk da haka mai nazari kan iya kwatanta na wani harshen da wani harshen domin ganin ta ina suka yi kama da kuma ta ina suka bambanta kuma ta wace fuska, tsari ko jigo. Akwai harsuna masu yawa cike da guraben bincike da ɗaliban Hausa ya kamata su ɗauki ko da nau’i ɗaya tare da kwatanta shi da na harshen uwa domin ganin ya ya yi kama ko ya bambanta. Sannan a duba a ga ko wannan nau’i na karin magana mai Labari akwai shi a wasu harsunan ko kuwa babu? Ko ba komai da komai hakan shi zai sa a ƙara inganta fannonin da samar wa kowane fanni gyauto daidai da kwankwason sa. Domin kuwa tabbas zancen Hausawa gaskiya ne da suke cewa da rashin tayi akan bar arha.

Manazarta

Aliyu, M. (1990) “Sabbin Karin Magana A Hausa”. Kundin Digiri Na Farko. Zaria: Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Ahmadu Bello.

Amin, M. L. (2004). ‘Re – Interpreting Hausa Proverbs On Duniya.’ Harshe 2. Zaria: Department Of Nigeria And African Languages, Ahmadu Bello University.

Birniwa, H.A. (1984). “Tsintar Dame A Kala: Matsayin Karin Magana A Cikin Waƙoƙin Siyasa”. Ɗunɗaye Jounal Of Hausa Studies. Department Of Nigerian Languages. Sokoto: Usman ƊAnfodiyo University.

Bugaje, M. H. (2016). HaƙUri Da Juriya A Mahangar Bahaushe: Tsokaci Daga Karin Magana. Takarda Da Aka Gabatar A Taron ƙAra Wa Juna Sani, Jami’ar Bayero Kano Ranar 9-12 Ga Watan Oktoba, 2016.

Bugaje, M. H. (2014). Karin Magana Mahanga Tunani: Nazarin Lokaci A Hausa” Kundin Digiri Na Uku. Zaria: Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya Da Afirka, Jami’ar Ahmadu Bello.

ƊAngambo, A. (1984) Rabe-raben Adabin Hausa Da Mahimmancinsa Ga Rayuwar Hausawa. Kano: Triuph Publishers Ltd.

ƊAngambo, A. (2008) Rabe-raben Adabin Hausa. Zaria: Amana Publishers Ltd.

ƊAnhausa, A.M. (2012). Hausa Mai Dubun Hikima. Kano: Century Research And Publishing Company.

Garba, B. (2017). Nazarin Karin Maganar Hausa. A Cikin Reading In Languages, School Of Languages Federal College Of Education Pankshin.

Guoling, Z. (1985). “Kwatanta Karin Maganganu Na Hausa Da Na Sinanci” Nazari A Kan Harshe, Da Adabi, Da Al’adu. Kano: Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero.

Gusau, S.M. (2003) Jagoran Nazarin Waƙar Baka. Kano: Benchmark.

Gwammaja, K. (2010). “Karin Magana A Ƙasar Hausa”. Kano: A Division Of Rabi’atu Publishers.

Hamisu, A. (2006). Dangantakar Karin Maganar Hausa Da Wasu Ayoyin Ƙur’ani Da Hadisai.” Kundin Digiri Na Farko. Zaria: Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya Da Afirka, Jami’ar Ahmadu Bello.

Hassan, M.B (1981) “Karin Magana Da Salon Maganar Hausawa”, Nazari A Kan Harshe, Da Adabi, Da Al’adu. Kano: Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero.

Hassan, S. (2009)Nazarin Karin Magana Da Suke Nuna Rarrashi”. Harshe 3. Zaria: Department Of Nigeria And African Languages, Ahmadu Bello University.

Junaidu, I. Da Yar’aduwa, T.M (2007) Harshe Da Adabin Hausa A Kammale Don Manyan Makarantun Sakandire. Ibadan: Spectrum Books Limited.

Kirk – Greene, A. H. (1966). Hausa Ba Dabo Ba Ne. Ibadan: University Press Ltd.

Koko, H. S. (2011). “Hausa Cikin Hausa”. (Ba Maɗaba’a).

Koko, H. S. (1989). “Karin Magana A Hannun Mata A Garin Sakkwato.” Kundin Digiri Na Farko, Sakkwato: Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usman Ɗanfodiyo.

Kwakwaci, K. H. (2010) Asalin Hausawa. Kano: Harsashi Punlishers, Ltd

Muhammed, Y. M. (2003). Adabin Hausa. Zaria: A.B.U University Press Ltd.

NNPC (1958). Karin Magana. Zaria: Northen Nigerian Publishing Company.

Tudun Wazirci, A.G.I (Bkw). “Ƙalailaicewa A Kan Karin Maganar Hausawa.” Kano: Sashen Nazarin Harsuna, Makarantar Shari’a Da Nazarin Addinin Musulunci Ta Aminu Kano.

Yunusa, Y. T/Wada (1981). “Tsari Da Ma’ana A Karin Maganar Hausa”, Nazari A Kan Harshe, Da Adabi, Da Al’adu. Kano: Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero.

Yusuf, Y. (1970). Hausa A Dunƙule. Zaria: Northern Nigerian Publishing Company.

Post a Comment

0 Comments