𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum, idan mutumun na cikin matsanantchiyar damouwa mi ya kamata ya yi dan magance ta? Dan Allah kumin kokari na samu amsa da wuri.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus
salam, Ibn Mas'ud Allah ya ƙara masa yarda ya ce: Manzon Allah ﷺ ya ce: "Wata damuwa ko baƙin
ciki ba sa taɓa samun
mutumin da ya karanta wannan addu'ar, face Allah ya tafiyar masa da wannan
damuwa da baƙin
ciki, kuma ya canja masa da kwaranyewar damuwar:
"اللَّهُمَّ إِنِّي عَبْدُكَ وَابْنُ عَبْدِكَ وَابْنُ أَمَتِكَ ، نَاصِيَتِي بِيَدِكَ
، مَاضٍ فِيَّ حُكْمُكَ ، عَدْلٌ فِيَّ
قَضَاؤُكَ ، أَسْأَلُكَ بِكُلِّ
اسْمٍ هُوَ لَكَ ،
سَمَّيْتَ بِهِ نَفْسَكَ ،
أَوْ عَلَّمْتَهُ أَحَدًا مِنْ خَلْقِكَ ،
أَوْ أَنْزَلْتَهُ فِي كِتَابِكَ ،
أَوْ اسْتَأْثَرْتَ بِهِ فِي عِلْمِ
الْغَيْبِ عِنْدَكَ: أَنْ تَجْعَلَ الْقُرْآنَ
رَبِيعَ قَلْبِي ، وَنُورَ صَدْرِي
، وَجِلَاءَ حُزْنِي ، وَذَهَابَ هَمِّي
؛ إِلَّا أَذْهَبَ اللَّهُ هَمَّهُ وَحُزْنَهُ ، وَأَبْدَلَهُ مَكَانَهُ
فَرَجًا".
MA'ANA:
"Ya Allah
ni bawanka ne, ɗan
bawanka, kuma ɗan
baiwarka, makwarkwaɗata
(maɗigata) a hannunka
take, hukuncinka zartacce ne a kaina, kuma ƙaddararka a gare ni mai adalci ne, ina roƙonka
da dukkan sunayenka, wanda ka ambaci kanka da shi, ko ka saukar da shi a cikin
littafinka, ko ka sanar da shi ga wani daga cikin halittarka, ko ka keɓance kanka da saninsa a
cikin ilimin fake (gaibu) da ke wurinka, ka sanya Alƙur'ani ya zama daɗi ga zuciyata, ya zama
haske ga ƙirjina,
ya zama kwaranyewa ga baƙin cikina, ya zama mai tafiyar da damuwata".
A ƙarshen
hadisin an ruwaito cewa Sahabbai sun tambayi Manzon Allah ﷺ cewa; shin ba ma koyi
wannan addu'ar ba? Sai ya ce: "Tabbas, ya kamata wanda ya ji addu'ar nan
ya koye ta"".
Musnadu Ahmad
(3712), Sahihu Ibn Hibban (972).
Wanda ba zai
iya yi da Larabci ba ya yi da Hausa.
FA'IDOJIN
WANNAN HADISI:
1. Idan damuwa
da baƙin
ciki suka dami mutum to ya lizimci wannan addu'ar.
2. Yawan
karanta Alƙur'ani
yana taimakawa wajen yaye baƙin ciki da damuwa.
3. Allah kaɗai ne yake iya yaye wa
mutum baƙin
ciki da damuwa ba waninsa ba.
4. Duk idan baƙin
ciki da damuwa suka matsa wa mutum ya yi addu'a ne, ba zuwa gidan boka ko ɗan tsubbu ba, musamman ma
wannan addu'ar.
5. Idan mutum
ya sami labarin wannan addu'ar shi ma ya yi ƙoƙarin sanar da waninsa.
6. Sahabbai
suna ba da himma wurin koyon abin da Annabi ﷺ
yake koyar da su, kuma ba sa rowar sanar da al'umma ilimoman da suka koya a
wurin Manzon Allah ﷺ. Da
dai sauran fa'idoji da dama.
Allah ne mafi
sani.
Jamilu Ibrahim
Sarki, Zaria.
Ga Masu Buƙatar
Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin
mu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/GUƙ2GCCzlcdL6nknƙLYYox
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.