Ticker

6/recent/ticker-posts

Amadu Maradun - Waƙar Alhaji Aliyu Magatakarda Wamakko (ALU)

 Wannan ɗaya ce daga cikin jerin waƙoƙin da aka yi wa Alhaji Aliyu Magatakarda Wamakko (ALU). A hasashen manazartan Amsoshi, ALU shi ne gwamnan ƙasar Hausa da ya fi kowane gwamna yawan waƙoƙi da aka yi masa.

Taimaka mana Jalla magaban Sarki,

Taimaka mana Jalla magaba,

Allah mai bai wa kowa samu.

 

Sakkwatawa an yi ta ƙare,

Ko gobe Alu ne gwamnan Sakkwatawa.

 

Sakkwatawa an yi ta ƙare,

To ko yanzu Aliyu ne gwamna sabo hul.

Hankali kaɗan shafa min ya fi,

Ehen!

Alu, angon Murjaaa angon Murja.

Da ranarka.

Angon Arziki mai dubun nasa har kullum.

Angon Arziki mai dubun nasara har kullum,

Baban Hodiyo jarumina ne kai komai,

Baban Mahadi ban manta girmanka,

Yauwa!

 

Alu gwamnan Sakkwatawa,

Ina babab Yasiraaa Allah ya kyauta darshanka,

Ga addu’ar Ahmad nan na turo,

Ga addu’ar Ahamad na turo,

Baban A’ishaaa Allah ya cece ka,

Amin, amin muna murna na har kullum,

Sannan kuma Bello Koc,

Bello Koc a gaishe ka ɗan girma

Bello Koc a gaishe ka ɗan girma

 

Shiko Bello na duba,

Baban Hindo a gai –

Ohƙ!

Angon Hindo na duba,

Angon Hindo mai nasara ɗan girma,

Angon Hindo mai nasara,

Allah shi jaaa zamanin sarki.

 

Baban Yasira ne,

Baban Madi a gaishe ka,

Allah shi biya ka nau Bello,

Baban Sadiya a gaishe ka,

Kai komai.

 

Baban Hodiyo jarumina ne,

Yauwa!

Domin Momi ina roƙo,

Bello ka ba ni tau mota sabuwa kau.

 

Domin Momi a ban mota,

Alu gwamnan Sakkwatawa,

Dauri ‘yan ta-ɓare suna zwatci,

Yanzu ‘yan ta-ɓare suna gureman.

 

Dauri ‘yan ta-ɓare suna ihu,

Yanzu ‘yan ta-ɓare suna ƙugi yan nema,

Domin Alu gwamna ya dawo,

Gaishe ka mai dubun nasa ɗan girma,

Jama’ar birni suna son,

Jama’ar ƙauye da na ohƙ!

Ko ta inda niz zaga,

Aliyu jarumi nau ne sun zaɓo,

Kuma malamai suna ta faɗi suma, ohƙ!

 

Kutareee had da guragu duk suna murna,

An ce wa Aliyu ar riƙon Sakkwatawa,

Mai dubun jama’a,

Kana mai dubun nasa kai komai,

Alhaji Bello Koc namu,

Yadda kai Allah ya biyashe ka,

Kuma ɗan Alu gwamnan Sakkwatawa,

Kuma ɗan Alu gwamnan Sakkwata,

Girman kuka ta banza ce,

Don mun san ba ta yin sanwa,

Ko ɗai-ɗai.

 

Biri na tsula an ce ohƙ!

Biri na tsula mai jaddara,

An ce koma a can daji ka yi noma,

An ce aje jad darar taka ka yi noma,

Don mu sam ba mu son samna ko ɗai-ɗai.

 

Da ɗan Maraduuuu

Mai girma muna waƙa,

Don Ali ag gwamna,

Muna ta rawa muna ta kiɗa,

Aliyu Aliyu,

Dogon daji na gode,

Na Aliyu na gode,

Na Aliyu kaaa kyau,

Aliyu Aliyu,

Dogon Daji na Aliyu ag gwamna,

Na Alu a gaishe ka,

Allah shi tsare ka mun gode har kullum.

 

Allah sarkin sarauta,

Allah taimaki Ali Wamako,

Ko gida bale daji,

Angon Arziki mai dubun jama’a,

Angon Murja mai dubun nasara,

Baban Hodiyo a gaishe ka,

Ali Wamako,

Baban Madi a gaishe ka,

Allah shi biya ka na gode kai komai,

Baban su Yasira dattijo,

Baban A’isha A’i,

Baban A’isha A’i,

Ilela a ban fata,

Domin mun kama aikin gwamnoni,

Aikin manyan wane yaro,

Yaro ka ja gefe,

Bello Koc,

Na Alu a gaishe ka,

Allah shi biya ka na gode kai komai,

Yauwaa!

 

Bello Koc a gaishe ka,

Ɗa ga Alu a gaishe ka kai komai,

Bello Koc a gasihe ka,

Uban Hindu da ranarka,

Angon Hindu a gaishe ka kai komai,

Baban Yasira na gode,

Baban Mahadi a gaishe ka kai komai,

Baban Sadiya a jaɓɓama,

Amadu mun biyo hanyar fillanci.

 

Baban Hodiyo na gode,

Ban raina ma da girma ba kai komai,

Domin Alu gwamnan Sakkwatawa.

 

Baban Momi a gaishe ka,

Alhaji Bello Koc namu ɗan girma,

Albarkar Momi a ban mota ta yi.

 

Sakkwatawa an yi ta ƙare,

Ko gobe Aliyu ne gwamna sabo hul.

 

Sakkwatawa an yi ta ƙare,

Ko gobe Aliyu ne gwamna ya dawo.

 

Aliyu jarumi,

Ban raina da girma ba kai komai,

Allah shi tsare ka na roƙa har kullum,

Allah shi tsare ka na roƙa har kullum.

 

In dai Alu shina gwamna,

Aman ni ba ni jin kunya ohƙ!

 

Alhaji Bello Koc namuuu,

Domin babanka ag gwamna,

Mun sami babak ka ag gwamna ɗan girma,

Nuna mana to Alu gwamnan Sakkwatawa,

Ka ban Makka ta hi min,

Iii Alu gwamnan Sakkwatawa,

Kare na tsula ɗan she, a’a.

 

To dai a bar zagi,

Kare na tsula na gan shi,

Biri na gan shi can jeji,

Mun gano muntansa ta heƙe ta yo ja,

Sai na ce mai kwashe kayanka,

Je can,

Wai birin Tawa zai koma,

Ya ce min Tawa zai koma,

Buzun Tawa an tsere,

Hag gobe Aliyu ne gwamna,

Don shi aka so kuma yad dawo.

 

Allah mun gode ma,

Ka ba mu jarumin gwamnaa,

Sadauki mai cikonnn,

Mai cikar magana,

Mai cika da faɗi ohƙ!

 

Alu in ya ba ka ya baka,

Halaye nai idan ka tuna,

Halin Sardauna ne garai,

Aliyu na gode,

Allah shi tsare ka mun roƙa har kullum.

 

Junaidu mu’azu na ode,

Allah shi tsare ka mun roƙa,

Sannan ga injiniya namu,

Alhaji Aminu na gode,

Allah shi tsare ka mun,

Allah shi yi yi ma Sarkin Musulmi,

Amin!

 

Aliyu Aliyu Dogon Daji,

Na gwamna Alu,

Na gwamna Ali

Na gwamna Ali,

In na kamo waƙar Sarkin Yamma,

Da kuɗɗi yake ba ni,

Allah shi biya ka na gode,

Dogon Daji mai kirki.

 

Mu komaaa sashen maigida,

Kuma sashen mai dubun jama’a,

Kuma ah! Mai dubun nasara,

Aliyu na gode,

Angon Murja a gaishe ka,

Angon Arziki mai dubun nasara,

Ko gobe Aliyu ne gwamnan Sakkwatawa,

Mai gurmi muna waƙaaa,

Ga Aliyu ag gwamna sabo hul.

 

Masu farin ciki,

Ku taya guɗa Alu gwamna ya dawo,

To ku kuwa ‘yan baƙan muƙura,

Allah shi tsare mu sheɗaniya ohƙ!

Allah shi tsare mu sheɗani,

Kai Aliyu ag gwamna sabo hul,

Baban Madi a gaishe ka,

Baban Hodiyo mai dubun nasara kai komai,

Sannan baban Bello Koc,

Allah shi biya ka naa gode,

 

Ah Alhaji Bello koc namu,

Allah shi biya ka na gode kai komai,

Don ban raina ga girma ba,

Angon Indo a gaishe ka,

Alhaji Bello Koc namu,

Angon Indo dattijo,

Angon Indo dattijo,

Allah shi biya ka nagode kai komai.

 

Baban su Yasira na gode,

Baban su Yasira na gode,

Baban Madi a gasihs eka,

Baban Sadiya a gaishe ka,

Baban Sadiya da ranarka kai komai,

Babn Hodiyo na gode,

Ban raina ma da girma ba,

 

Ka yo ɗa,

Ka yo min ɗa,

Baban Momi,

Baban Momi,

Momi

Allah ƙara girmanki,

Allah shigwada mana ran auren Momi,

In kwashi dau,

Allah shi gwada mana ɗaurin auren Momi,

To muna murna har fata,

Alabarkar Momi na roƙa,

Kai min mota ake ba ni,

To albarkar Alu gwamnan Sakkwatawa,

To albarkar Alu gwamnan Sakkwatawa,

 

Sakkwatawa an yi ta ƙare,

Ko gobe Aliyu ne gwamana sabo .

 

Canjin kiɗa da rauji

 

Allah dogaran Musulmi,

Mai sama dogaran Musulmi,

Allah ka ba mutum sa’a ko a ina yake,

Alu Magatakarda,

Ɗan Barade jaɓi,

Alun Magatakarda,

Angon Arziki a gaishe ka,

Godiya nike yi,

Angon Murja a gaishe ka,

Dattijo Ali babana,

Aha!

 

Angon Arziki masu arziki da yawa,

Na yaba da ƙauna,

Baban su Hodiyo,

Hana-ƙarya Aliyu baba,

Sannu farin cikin Musulmi,

Farin watan mutane Ali,

Ga aljanna mai masoya da yawa a duniya,

 

Iiii Alu ba!

 

Aljanna mai masoya da yawa a duniyan nan,

In rana ta futo gabas,

Tafin hannu ba zai tare ba,

Mahassada kullum,

Ƙaryarku mahassada,

Kul ɗinku mahassada,

Domin Aliyu namu shi ag gwamna.

 

Cikin jahar nan esko haka,

Amadu na ba da kyauta,

Baban su Yasira Aliyu babana,

Baban su Yasira Aliyu babana,

Baban A’isha godiya nike yii,

Baban Bello Koc a gaishe ka,

Aliyu magatakarda.

Baban Bello Koc a gaishe ka,

Aliyu magatakarda.

Bello Koc a gaishe ka,

Godiya.

 

Ina angon Hindu na yaba mai,

Angon Hindu mun yaba maka.

 

Allah shi ƙara ƙauna,

Baban su Yasira da kai mu kai,

Baban Momi godiya da ƙauna,

Baban Sadiyya, Aha!

Baban Halimatussa’adiya,

Baban su Hodiyo,

Baban Momi farin masoyi,

Baban Momi farin masoyi,

Alhaji Bello Koc gaishe ka,

Ga ɗan Maradu gurmi,

Farin watan Musulmi,

Farin cikin mutane Ali,

Alun magatakarda,

Tauraruwar gabas da harke,

Cikin Musulmi,

Icen agwara a bar matsa mai,

Don ka san ba ya son garaje,

Ba ya son garaje,

Alun magatakarda,

Ga rijiyar cikin daji,

Magatakarda,

Bayin Allah su zo su,

Su ɗiba,

Kuma tsuntsayen dawa su kurɓa,

Su sha ruwansu sosai.

 

Amadu godiya nake yi,

Angon Arziki a gai da mai dubun jama’a,

Kuma angon Arziki,

Mai arziki da yawa,

Angon Murja da kai muke yi,

Sannu farin watan mutane esko,

Sannu farin watan mutanen birni da ƙauyukansu,

Haba!

 

Yadi Ilela mai kiɗa,

Shi ma ga shi nan da ganga,

Mu dai gaisuwa muke miƙawa ga ɗan Barade,

Ku ja mu je kiɗanmu,

Sannunku maga Aliyu Aliyu Dogon Daji,

Ga shi zaune,

Allah shi yi ma sarki Musulmi,

Albarkar magatakarda,

Ya ba ni ya daɗa min,

Albarkar magatakarda,

Ya ba ni ya daɗa,

Ban raina da arziki nai ba,

Kai dai ko ba ka yin Alu,

To babanka na matsa mai,

To ko ba ka son Alu,

To babanka na kan so nai,

 Koko ba ko ba ka son Alu,

Babanka na matsa shi,

Idan uban ba ya son Alu,

To ɗan ɗanshi na matsa mai,

Iii!

 

Alu ikon Allah,

Ka wuce gaban mamaki,

Baban Hodiyo a gai da kai,

Alu farin watan Musulmi,

Ga aljanna mai masoya da yawa a duniya,

Alun magatakarda,

 

Alhaji Bello Koc a gaishe ka,

Godiya nike yi,

Angon Hindu da kai muke yi,

Angon Hindu da kai muke, Bello Koc,

Baban, baban su Yasira da kai ake,

Baban su Yasira da kai muke yi,

Baban Mahadi na yaba,

Ban raina da arziki ba,

Baban Halimatussa’adiya,

Da kai muke yi,

Baban Hodiyo a gaishe ka.

 

Bello Koc masoyi,

Baban Momi,

Baban Momi,

Baban Momi,

Allah biya ka amin,

Amadu ya yaba da kyauta,

To Allah shi ƙara ƙauna,

Mun ce tafiyar biri ga lilo,

Yaro ba zai iya ba,

To ko ya iya,

Mu nai masa gyara da namu gurmi.

 

Canjin sauti da rauji

 

Allah Sarki Zuljalali,

 

Allah taimaki mai gidana,

Allah ka ba shirarre,

Ala shi biya ka kullum,

Ban raina mar da duk, ohƙ!

Aliyu ka ba shirarre,

Tun farkon farin Aliyu,

Mun san ya danne ‘yan maza,

Aliyu to ya danne ‘yan maza,

Saboda gwamnanmu ɗan gari na gode,

Angon Arziki jarumi,

Mai arziki da yawa na gode,

Baban hodiyo jarumina,

Allah hi biya jarumina,

Baban Mahadi ban gama da kai ba,

Baban su Yasira jarumi,

Lillahi ya taimaka shi raba ka da ‘yan,

Shi raba ka da ‘yan-‘yan-‘yan,

‘ya’yan tcegumin banza,

Shi raba ka da ‘ya’yan tcegumi Alu.

 

Baban A’isha A’i,

Ban raina da kai ba.

Baban A’isha A’i,

Ban raina da kai ba.

 Sannan kuma baban Bello Koc,

Sannan kuma baban Bello Koc,

Shi kuma Bello Koc,

Kuma angon Hindu ne shi,

Kuma angon Hindu ne shi,

Allah shi biya ka na gode,

Baban su Yasira,

Bello Koc a gaishe ka,

Ya Allahu shi taimaka ma,

Baban su Yasira jarumin maza.

Baban Mahadi a gaishe ka,

Baban Sadiyya shirarre,

Baban Hodiyo jarumina,

Jarumi,

Gaishe ka baban Hodiyo jarumina,

Baban Momi a gaishe ka,

Amadu bai raina da girma ba,

Dogon DFaji na gode,

Aliyu Aliyu ka biya.

 

Idan na ga waaƙar gwamna,

Ya ba ni kuɗi ƙwarai-ƙwarai,

Har riga da yawa ya aiko,

Allah shi yi ma sarkin Musulmi,

Aliyu Aliyu Dogon Daji,

Allah shi biya ka na gode,

Domin Ali Wamako ya ban riga,

Ɗai-ɗai-ɗai-ɗai-ɗai,

Has sau goma sha huɗu.

 

Alhaji Bello Koc,

Kai ko albarkar Momi ƙilan,

Mu samo kasaya,

Ko sabo dal ko,

Da ni da yarana guda biyu,

Domin Bello,

Alhaji Bello Koc,

Albarkar gwamna Ali,

Kasiya nike so ka bayar,

Da ni da yarana guda biyu,

Domin Ɗan Barade jikan Ummaru,

Domin gwamna farin cikin masoya,

Allah taimaka,

Allah sa addu’ar da niy yi,

Idan kuma ta karɓe mu mun ji daɗi,

Allah shi tsare ka na roƙa,

Alu shirarre,

Sabon gwamnanmu ɗan karimɗa,

Sabon gwamnanmu ɗan karimɗa,

Sakkwatawa na farin ciki,

Zamfarawa na farin ciki,

Kabawa na farin ciki,

An ce kuma Ali ya dawo.

 

Amadu Ɗan Maradun,

Mamakin Ɗan Maradun nay yo,

A dauri dai ban bayyana ba,

Amma sai na bayyana shi,

Har ga tumaki ɗan Maradun,

Idan Alu ya dawo,

Su ma,

Mun ga suna murna,

Suna kaɗa bindi,

Ga Ali har gida.

 

To tsuntsaye suna murna,

Na gida kuma har da daji,

Balle mu,

Ban raina ma da girma ba,

Allah taimaka Wamako,

Domin Aliyu ya dawo.

 

Alhaji Bello Koc,

Haji Bello Koc,

Albarkar Aliyu sabo,

Da ni da yarana guda biyu,

Da ni da yarana guda biyu,

Allahu shi taimaka ma,

Ban raina ma da girma ba,

Mai dubun jama’a a gaishe ka,

Gaishe ka Aliyu sabo,

Angon Arziki mai gidana,

Angon Murja jarumina,

Baban Hodiyo,

Baban Mahadi a gaishe ka,

Baban su Yasira,

Yasira Yasira,

Idan kin ji ni Yasira,

Mota nake so ki sai min,

Idan kin ji ni Yasira,

Ni mota nake so ki sai min,

A’isah Ala taimaka A’i,

Wajen A’i ko,

Amadu na yi mafalki,

An ce haure na,

An ce haurena ya ɗan rawa,

Na ce haurena ka bar rawa,

Ga A’isha, A’isaha,

To wataƙil bana Makka nay yi,

Tunda dai ga A’isha,

To wataƙil bana Makka nay yi,

Sannu Alhaji Bello Koc,

Amadu ya gode da girma Bello.

Post a Comment

0 Comments