𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum wa rahmatullah. Ina yiwa mlm fatan alkhairi, Allah ya kara budi. Wasu ne suke neman fatawan a kan wannan mas'alar "musulmine yake auren Christian, to wai idan zai fidda zakkar fidda-kai itama zai fitar mata?"
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikum assalam
Hadisi ya tabbata daga Ibnu Umar cewa: "Annabi (SAW)
ya farlanta zakkar fidda-kai a kan kowanne
musulmi Ɗa ne ko bawa" kamar yadda Bukhari
da Muslim suka rawaito.
Hadisin da ya gabata yana nuna musulmi ake fitarwa zakkar
fidda-kai, amma kafiri ba'a fitar masa, kuma ba'a ba shi in an fitar.
Allah ne mafi sani
DR. JAMILU YUSUF ZAREWA
Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta
Links ɗin mu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/DSdbBS8RZVoIKYG5exOuZE
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.