Ticker

6/recent/ticker-posts

Yadda Ake Fitar Da Zakkar Fidda-Kai

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Don Allah tambayata ita ce kamar hatsin da ake badawa ranar Sallah na fidda-kai duk mutun ɗaya mudu nawa garai?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Sahabin Manzon Allah (SAW), Abdullahi Ibn Abbas ya ruwaito cewa: “Manzon Allah (SAW) wajbata Zakkar kono domin kankare kurakurai da yasassun maganganun da mai azumi ya yi, sannan sadaka ce ga miskinai.”

Daga cikin hikimar bayar da ita, akwai sanya wa miskinai farin ciki ta hanyar samar musu da abun da za su ci a lokacin Karamar Sallah

 YADDA AKE FITARWA:

Mutum zai fitar wa kansa da kuma waɗanda yake ciyarwa kamar mata, ’ya’ya da ma’aikata da sauransu idan Musulmai ne.

Manzon Allah Ya wajabta fitar da zakkar kono ga babba da yaro, ’yantacce da bawa, daga cikin waɗanda kuke ciyarwa,” kamar yadda Abdullahi bn Umar ya ruwaito a Hadisi.

Mai fitar da zakkar zai fara ne da fitar wa kansa, sannan sauran mutanen gwargwadon wajibcin ciyar da su a kansa.

 ADADIN DA AKE FITARWA:

Kowanne mutum ɗaya za a fitar masa da Sa’i ɗaya, wato Mudun Nabi Huɗu. Idan babu Sa’i ko Mudun Nabin awo, ana iya aunawa da hannu. Malamai sun ce Mudun Nabi ɗaya daidai yake da cikin tafin hannu biyu na matsakaicin mutum.

 ABIN DA AKE FITARWA:

Ana fitar da zakkar kono ce daga nau’in danyen abincin mutanen garin.

 Ana fitarwa ne daga abin da ya karu a kan abincin rana da yinin mai fitarwa da iyalansa a lokacin.

 LOKACIN FITARWA:

Malamai sun bayyana cewa ya halalta a fitar da zakkar tun daga ranar 28 ga Ramadan.

Hadisi ya nuna, “Abauullahi bn Abbas kan ba da ita da kwana daya ko kwana biyu kafin ranar Sallah.” Amma tana wajaba ne daga safiyar ranar Karamar Sallah, a kuma gama kafin Sallar Idi. Wanda ya bayar kafin sallah to zakka ce karbabbiya, wanda ya bayar bayan sallah kuma to sadaka ya bayar kamar sauran sadakoki.”

Malamai sun ce haramun ne a jinkirta fitar da da ita ba tare da uzuri ba.

 WAƊANDA AKE BA WA:

Hadisi ya nuna miskinai ake bai wa. Wasu malamai na ganin ana iya ba da ita ga sauran mutanen da ake ba wa zakkar farilla (bayi, matafiya, masu bashi a kansu, masu aikin karbar zakka, masu aikin fisabilillahi, waɗanda ake kwadayin su musuluntar).

Wanda aka ba wa zakkar shi ma zai fitar, idan har an samu ragowa.

WALLAHU A'ALAM

Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin mu...

ADADIN ZAKKATUL FITR

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu Alaikum, Nawa ne adadin zakkatul fitr?  Shin ya halatta a bayar bayan Sallar Idi?  Shin ya halatta a bada zakkar fidda kai da kuɗi?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa Alaikumus salam Warahmatulah, Godiya ta tabbata ga Allah.

 An ruwaito cewa, Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya wajabta zakkar fidda kai ga musulmi a kan sa'i ɗaya na dabino ko sa'i ɗaya na sha'ir, kuma ya yi umarni da a ba da ita kafin mutane su fita yin sallah (watau sallar idi). A cikin sahihaini an karɓo daga Abu Sa’eedul Khudriy (Allah Ya yarda da shi) ya ce: “A lokacin Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) mun kasance muna bayar da shi a lokacin da aka ba shi adadin sa'i ɗaya na abinci, ko sa'i ɗaya na dabino, ko sa'i ɗaya na sha'ir, ko sa'i ɗaya na cuku, ko sa'i ɗaya na zabibi...” Malamai da dama sun fassara kalmar ta’am (abinci) a cikin wannan hadisin da yake magana akan cewa alkama ce, wasu kuma sun bayyana shi da cewa yana nufin abinci mai gina jiki na mutanen gari, ko ma dai menene, alkama ne ko masara ko wani abu daban. Wannan shi ne mahangar da ta dace, domin zakka wani nau'i ne na taimako da masu hannu da shuni suke yi wa talakawa, kuma bai kamata musulmi ya ba da taimako da wani abu ba face babban abincin kasarsa. Abin da dole ne a ba shi shine sa’i na kowane nau’in abinci, wanda ya ninka adadin da aka diba da hannaye biyu, wanda ya kai kusan kilogiram uku. 

Idan musulmi ya ba da sa’i na shinkafa ko wani babban abincin kasarsa, hakan shi ne ya fi.

Bada zakkar fidda kai yana fara farawa ne a daren ashirin da takwas ga watan ramadan, domin sahabban Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) sun kasance suna ba da ita gabanin Idi da kwana ɗaya ko biyu, kuma watan ya cika ashirin da tara ko kuma  kwana talatin.

 Na baya-bayan nan ana iya bayar da ita a Sallar Idi, amma bai halatta a jinkirta ta ba har zuwa bayan sallar idin, saboda hadisin Ibn Abbas (ra) ya ruwaito cewa Annabi (Sallallahu alaihi Wasallam) ya ce: "Wanda ya bayar da ita gabanin sallah, zakka ce karbabbiya, kuma wanda ya bayar bayan salla, to sadaka ce."  (Abu Dawud ne ya ruwaito).

Bai halatta a bayar da kimar kuɗi ba a matsayin fidda kai, a wajen mafi rinjayen malamai, kuma hujjar wannan magana ta fi inganci. A maimakon haka sai a ba da ita ta hanyar abinci, kamar yadda Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) da Sahabbansa (Allah Ya yarda da su) da mafi yawan al’ummah suka yi.

Muna rokon Allah da ya taimake mu da sauran musulmi baki ɗaya don fahimtar addininsa da riko da shi.  Allah ka yi salati ga Annabinmu Muhammad (Sallallahu alaihi Wasallam) da alayensa da sahabbansa baki ɗaya.

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/Du5LNx31U9hDi6RƘbbrzgW

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments