𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Don Allah tambayata ita ce kamar hatsin da ake badawa ranar
Sallah na fidda-kai duk mutun ɗaya mudu nawa garai?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Sahabin Manzon Allah (SAW), Abdullahi Ibn Abbas ya
ruwaito cewa: “Manzon Allah (SAW) wajbata Zakkar kono domin kankare kurakurai
da yasassun maganganun da mai azumi ya yi, sannan sadaka ce ga miskinai.”
Daga cikin hikimar bayar da ita, akwai sanya wa miskinai
farin ciki ta hanyar samar musu da abun da za su ci a lokacin Karamar Sallah
YADDA AKE FITARWA:
Mutum zai fitar wa
kansa da kuma waɗanda yake ciyarwa kamar mata, ’ya’ya da ma’aikata da sauransu
idan Musulmai ne.
“Manzon Allah
Ya wajabta fitar da zakkar kono ga babba da yaro, ’yantacce da bawa, daga cikin
waɗanda kuke ciyarwa,” kamar yadda Abdullahi bn Umar ya ruwaito a Hadisi.
Mai fitar da zakkar zai fara ne da fitar wa kansa, sannan sauran mutanen gwargwadon
wajibcin ciyar da su a kansa.
ADADIN DA AKE FITARWA:
Kowanne mutum ɗaya za a fitar masa da Sa’i ɗaya, wato
Mudun Nabi Huɗu. Idan babu Sa’i ko Mudun Nabin awo, ana iya aunawa da hannu.
Malamai sun ce Mudun Nabi ɗaya daidai yake da cikin tafin hannu biyu na
matsakaicin mutum.
ABIN DA AKE FITARWA:
Ana fitar da zakkar kono ce daga nau’in danyen abincin
mutanen garin.
Ana fitarwa ne
daga abin da ya karu a kan abincin rana da yinin mai fitarwa da iyalansa a
lokacin.
LOKACIN FITARWA:
Malamai sun bayyana cewa ya halalta a fitar da zakkar tun
daga ranar 28 ga Ramadan.
Hadisi ya nuna, “Abauullahi bn Abbas kan ba da ita da
kwana daya ko kwana biyu kafin ranar Sallah.” Amma tana wajaba ne daga safiyar
ranar Karamar Sallah, a kuma gama kafin Sallar Idi. Wanda ya bayar kafin sallah
to zakka ce karbabbiya, wanda ya bayar bayan sallah kuma to sadaka ya bayar
kamar sauran sadakoki.”
Malamai sun ce haramun ne a jinkirta fitar da da ita ba
tare da uzuri ba.
WAƊANDA AKE BA WA:
Hadisi ya nuna miskinai ake bai wa. Wasu malamai na ganin
ana iya ba da ita ga sauran mutanen da ake ba wa zakkar farilla (bayi,
matafiya, masu bashi a kansu, masu
aikin karbar zakka, masu aikin fisabilillahi, waɗanda ake kwadayin su
musuluntar).
Wanda aka ba wa zakkar shi ma zai fitar, idan har an samu
ragowa.
WALLAHU A'ALAM
Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin
mu...
ADADIN ZAKKATUL FITR
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum, Nawa ne adadin zakkatul fitr? Shin ya halatta a bayar bayan Sallar
Idi? Shin ya halatta a bada zakkar fidda
kai da kuɗi?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikumus salam Warahmatulah, Godiya ta tabbata ga Allah.
An ruwaito cewa,
Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya wajabta zakkar fidda kai ga
musulmi a kan sa'i ɗaya
na dabino ko sa'i ɗaya
na sha'ir, kuma ya yi umarni da a ba da ita kafin mutane su fita yin sallah
(watau sallar idi). A cikin sahihaini an karɓo
daga Abu Sa’eedul Khudriy (Allah Ya yarda da shi) ya ce: “A lokacin Manzon
Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) mun kasance muna bayar da shi a lokacin da
aka ba shi adadin sa'i ɗaya
na abinci, ko sa'i ɗaya
na dabino, ko sa'i ɗaya
na sha'ir, ko sa'i ɗaya
na cuku, ko sa'i ɗaya
na zabibi...” Malamai da dama sun fassara kalmar ta’am (abinci) a cikin wannan
hadisin da yake magana akan cewa alkama ce, wasu kuma sun bayyana shi da cewa
yana nufin abinci mai gina jiki na mutanen gari, ko ma dai menene, alkama ne ko
masara ko wani abu daban. Wannan shi ne mahangar da ta dace, domin zakka wani
nau'i ne na taimako da masu hannu da shuni suke yi wa talakawa, kuma bai kamata
musulmi ya ba da taimako da wani abu ba face babban abincin kasarsa. Abin da
dole ne a ba shi shine sa’i na kowane nau’in abinci, wanda ya ninka adadin da
aka diba da hannaye biyu, wanda ya kai kusan kilogiram uku.
Idan musulmi ya ba da sa’i na shinkafa ko wani babban
abincin kasarsa, hakan shi ne ya fi.
Bada zakkar fidda kai yana fara farawa ne a daren ashirin da
takwas ga watan ramadan, domin sahabban Manzon Allah (Sallallahu Alaihi
Wasallam) sun kasance suna ba da ita gabanin Idi da kwana ɗaya ko biyu, kuma watan ya
cika ashirin da tara ko kuma kwana
talatin.
Na baya-bayan nan ana
iya bayar da ita a Sallar Idi, amma bai halatta a jinkirta ta ba har zuwa bayan
sallar idin, saboda hadisin Ibn Abbas (ra) ya ruwaito cewa Annabi (Sallallahu
alaihi Wasallam) ya ce: "Wanda ya bayar da ita gabanin sallah, zakka ce
karbabbiya, kuma wanda ya bayar bayan salla, to sadaka ce." (Abu Dawud ne ya ruwaito).
Bai halatta a bayar da kimar kuɗi ba a matsayin fidda kai, a wajen mafi
rinjayen malamai, kuma hujjar wannan magana ta fi inganci. A maimakon haka sai
a ba da ita ta hanyar abinci, kamar yadda Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam)
da Sahabbansa (Allah Ya yarda da su) da mafi yawan al’ummah suka yi.
Muna rokon Allah da ya taimake mu da sauran musulmi baki ɗaya don fahimtar addininsa
da riko da shi. Allah ka yi salati ga
Annabinmu Muhammad (Sallallahu alaihi Wasallam) da alayensa da sahabbansa baki ɗaya.
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/Du5LNx31U9hDi6RƘbbrzgW
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.