𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Asssalamu alaikum malam. Waɗanne nau'in abunci
ne ake yin zakkar fidda-kai da su?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Zakkar fidda-kai ana fitar da itane daka dukkan wani
nau'in abuncin damutane suke ci, kamar alkama da masara da shinkafa, da gero da
dangoginsu, danama da wake da makaroni, dama kantansu, hakika manzan Allah sallallahu alaihi wasallam y afarlanta
ta sa'i ɗaya na abunci, sahabbai yardar Allah takara tabbata
agaresu sun kasance suna fitar da ita daka abuncin dasuka saba suna ci
agaruruwansu.
Imamul bukhari yaruwaito hadisi (1510) da muslim(985)
Daka Abu sa'idul kudri yardar Allah takara tabbata agareahi ya ce: (Munkasance muna fitar da zakkar
fidda-kai ranar idin karamar sallah azamanin Annabi ﷺ sa'i ɗaya na abunci, Abu
sa'idul khudri ya ce: abuncinmu ya
kasance shi ne azzabib da accah, da dabino, da Al'aƙdi, Nonone
ake alkintashi yakoma gyararre ana hadashi da dabino aci.
Malamai dayawa sun fassara abunci a cikin hadisin dacewa: (Alkama ake nufi) wasu sukace: Abunda ake nufi
da abunci shi ne wanda mutanan gari suka saba shi ne abuncinsu, kowanne irine,
alkamace ko masara ko makamantansu, Majmu'u fatawa bin baaz (14/200).
Shaikul islam ibnu taimiyyah a cikin majmu'u fatawa (68/25) ya ce: Idan mutanan gari sun kasance sun
saba da cin ɗaya daka cikin jerin wadancan nau'ikan abunci yahalatta
sufitar da zakkar fidda-kai a cikinsu
babu kokwanto a kan wannan, shi ne maganar mafiya rinjayen malamai.
Ibnul ƙayyem a cikin littafinsa I'I LAMUL MUWAƘƘI'EEN (3/12)
ya ce: Mutanan garin da su abuncinsu
ba acca bane ko alkama ko dabino kamar waɗanda abuncin
garinsu shi ne shinkafa dasuransu zasu fitar da sa'i ɗaya daka nau'in
abuncin, kamar wanda abuncinsu shi ne nama ko kifi, ko nono, zasu fitar daka
cikinsu kowanne irin nau'ine na abunci indai shi ne abuncinsu dasuka saba dashi
zasu fitar daka cikinsa, wannan shi ne maganar jamhur din malamai kuma shi ne
dai-dai wanda baza a fadi sabanin hakaba,.
WALLAHU A'ALAM.
Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta
wannan Links...
NAU'IN ABINCIN DA AKE YIN ZAKKAR FIDDA-KAI DA NAU'IN MUTANEN
DA ZA A BA WA
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Asssalamu alaikum Malam. Wadanne Nau'in Abuncine ake Yin
Zakkar Fidda-Kai Dasu? Kuma Wadanne Nau'in Mutanen ne Daza'a Bawa zakkar fidda
kai ?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus Salam Warahmatullahi Wabarkatuhu.
Zakkar fidda-kai ana fitar da itane daka dukkan wani nau'in
abuncin damutane suke ci, kamar alkama da masara da shinkafa, da gero da
dangoginsu, danama da wake da makaroni, damakantansu, hakika manzan Allah
sallallahu alaihi wasallam ya afarlanta ta sa'i ɗaya
na abunci, sahabbai yardar Allah takara tabbata agaresu sun kasance suna fitar
da ita daka abuncin dasuka saba suna ci agaruruwansu.
Imamul bukhari yaruwaito hadisi (1510) da muslim( 985) Daka
Abu sa'idul kudri yardar Allah takara tabbata agareahi yace: ( Munkasance muna
fitar da zakkar fidda-kai ranar idin karamar sallah azamanin Annabi (Sallallahu
alaihi Wasallam) sa'i ɗaya
na abunci, Abu sa'idul khudri yace: abuncinmu yakasance shine azzabib da accah,
da dabino, da Al'aqdi, Nonone ake alkintashi yakoma gyararre ana hadashi da
dabino aci.
Malamai dayawa sun fassara abunci acikin hadisin dacewa: (
Alkama ake nufi) wasu sukace: Abunda ake nufi da abunci shine wanda mutanan
gari suka saba shine abuncinsu, kowanne irine, alkamace ko masara ko
makamantansu, Majmu'u fatawa bin baaz ( 14/200).
Shaikul islam ibnu taimiyyah acikin majmu'u fatawa ( 68/25)
yace: Idan mutanan gari sun kasance sun saba da cin ɗaya daka cikin jerin wadancan nau'ikan abunci
yahalatta sufitar da zakkar fidda-kai acikinsu babu kokwanto akan wannan, shine
maganar mafiya rinjayen malamai.
Ibnul qayyem acikin littafinsa I'I LAMUL MUWAQQI'EEN ( 3/12)
yace: Mutanan garin dasu abuncinsu ba acca bane ko alkama ko dabino kamar
wadanda abuncin garinsu shine shinkafa dasuransu zasu fitar da sa'i ɗaya daka nau'in abuncin,
kamar wanda abuncinsu shine nama ko kifi, ko nono, zasu fitar daka cikinsu
kowanne irin nau'ine na abunci indai shine abuncinsu dasuka saba dashi zasu
fitar daka cikinsa, wannan shine maganar jamhur ɗin
malamai kuma shine dai-dai wanda baza'a faɗi
saɓani hakaba.
NAU'IN MUTANEN DAZA'A BAWA ZAKKAR FIDDA KAI
Wannan mas'ala akwai saɓanin
malamai akanta, shafi'iyyah suntafi akan waɗanda
ake bawa zakkar fidda kai sune jinsin mutane takwas da Allah yalissafa waɗanda za'a bawa zakkar kuɗi ko dukiya.
Malikiyya suntafi akan waɗanda
za'a bawa zakkar fidda-kai sune talakawa da miskinai, kuma shine ra'ayin da
shaikul islam ibnu taimiyyaj da dalibinsa ibnul qayyeem suka zaɓa, cikin malaman wannan
zamanin kuma shaik bin baaz ya zaɓi
wannan maganar.
yazo acikin hashiyatul dasuqi ( 1/508) " Ana bayar da
zakkar fidda kai ga ɗa
musulmi talaka wanda ba dangin Annabi ba,
banda mai aikin zakkar ko wanda akesan ya musulunta ko wanda yake
matafiya ko bako, kawai ana bawa talaka ne.
Ibnu taimiyyah yace: " wannan zancen shine yafi karfi
wajan dalili, majmu'u fatawa ( 25/71).
Ibnul qayyeem acikin zadul ma'ad ( 2/23) yace: yana daka
cikin shiriyar manzan Allah sallallahu Alaihi wasallam keɓance talakawa da ita, bai
kasance yana rabata ga jinsi takwas danki danki ba, kuma bai umarni da hakaba,
babu wani cikin sahabbai daya aikata hakan, ko waɗanda
suka biyo bayansu, daya daka cikin zantukan awajanmu, shine ta keɓanta ne kaɗai ga miskinai datalakawa,
bai halatta rabata tsakanin jinsi takwas ba.
WALLAHU A'ALAM.
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/IƙsWWSpUkwk6b8hWJ6vXOO
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
No comments:
Post a Comment
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.