𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Shin idan na yini da niyyan yin azumi toh idan akaga wata
dolene kuma zanyi wata niyya ayayinda naji labarin ganin watan???
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Toh ai Waccan Niyyarda ka yini da ita ba a cikin Watan Ramadan kayitaba, kayitane a
cikin Watan Sha'aban wanda a wannan Lokacin Azumi be wajaba akankaba idan da
ace zaka Mutu a wannan lokacin Allah baze Tambayeka meyasa bakayi Azumiba. Toh
kaga ashe Niyyarda ka wuni da ita ba ta da wani amfani tun da ta gabaci Sababi.
Kamar Mutuminda ya yi Niyyar Sallah
ne tun kafin lokacin Sallar ya yi Misali
a cikin dare sekace kayi Niyyar Sallar Azahar toh wannan Niyyar ba za ta
amfanekaba harse lokacin Sallar ya yi ka
sake ƙulla Sabuwa. Sannan kuma akwai Buƙatar a
fahimci abunda ake kira Niyya ɗin. Ai dazarar akace anga Wata a cikin Dare toh duk me Hankali a wannan lokacin zeji a ransa cewa zeyi
Azumi gobe kokuma bazeyiba.
Kamar waɗanda ba sa yin
Azumi sesunga wata to in aka sanarda ganin wata zakaga kowa yanata shirye
shiryen tanadar abunda zeyi Sahur amma su waɗannan babu wani
Shirinda suke yi to kaga wannan sune basuda Niyya amma shi me Niyya zakaga
yanata kaikomo a kan abunda zeyi
Sahur. Sannan kuma cewarda ake yi ayi Niyya a cikin dare bawai can irin ƙarfe Goma ko Sha Biyun dare kawai ake nufiba. A'a Matuƙar Afajir be Bayyanaba toh a wannan Lokacin shima darene
ana iya ƙulla Niyyar Azumi a
cikinshi. Kuma inhar Mutum ya ci abincin Sahur toh indai me Hankali ne to ya yi Niyya tun da yasani cewa
Abincinnan da nakeci ina cinshi ne danufin inyi Azumi toh kaga wannan aishima
Niyyace. Bawai wani magana ake yi dabakiba wanda za'ace shi ne Niyya A'a inhar
Mutum yasan abunda yake yi toh shikenan ansamu Niyya.
Allah ya sa mudace
✍🏼Jameel Alhasan Haruna Kabo (ABU ZULAIKHA)
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/BSA30hdZD7V3WSJF8WVwUj
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
No comments:
Post a Comment
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.