Ticker

6/recent/ticker-posts

Me Ya Sa Aka Boye Daren Lailatul Kadri?

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu Alaikum malam khamis shin me ya sa aka ɓoye daren lailatul ƙadri?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Sheikh Ibn Uthaymeen Allah ya yi masa rahama Yana cewa:- "Allah ya ɓoye ilimin daren Lailatul Ƙadri ga bayinsa, dan rahama ga bayinsa dan su yawaita aiyuakan ɗa’a a cikin kwanaki goma na karshen watan Ramadana cikin neman wannan daren, da an sanya a wata rana ɗaya sananniya kamar ranar arfa to da sun yi ibada kaɗai Saboda ibadar dare ɗaya kaɗai za su yi, amma da yake ya ɓoye hakan sai su yawaita ibada a daren goma gaba ɗaya suna neman dacewa da shi hakan ya fi falala da Yawaita ibada da samu lada da matsayi mai yawa da girma a wajen Allah.

Dan haka ake so su yawaita yin waɗannan manyan ibadun a cikin waɗannan dararen don dacewa da daren Lailatul Ƙadri.

Ibadun sun hada da:- Sallah, Zikiri da Addu'a da Karatun Al-Ƙur'ani

@ﻣﺠﺎﻟﺲ ﺷﻬﺮ ﺭﻣﻀﺎﻥ 173]

Ibn al-Jawzi, Allah ya yi masa rahama, mai albarka da daukaka Yana cewa:- Ayyub ya ruwaito daga Abi Ƙulabata yana cewa:- "Daren Lailatul Ƙadari yana chanchanzawa a kwanakin goman karshe na Ramadana, a cikin mara, hikimar ɓoye wannan dare kuwa shi ne dan mutane su dage da Yawaita ibada a karshen watan Ramadana suna neman dacewa da wannan daren mai albarka, ibadar su da aiyukan ɗa’a na su ya karu tare da samu falala mai girma........ "

@زاد المسير

Ibn al-Jawzi, Allah ya yi masa rahama, mai albarka da daukaka Yana cewa:- "An ɓoye daren Lailatul Ƙadri ne Saboda da manyan dalilai guda biyu:-

1- Rahama ga bayin Allah dan su dage da aiyuakan ɗa’a a kwanakin goman karshen Ramadana suna raya daren da ibada dan karshen wata ya zama sun yi aiyuakan masu yawa fiye da farkon Ramadana.

2- Dan su dage da aiyuka masu yawa Saboda ba su da tabbas ko za su kara riskar wani Ramadan nan gaba, kila wannan shi ne Ramadan nasu na karshe a rayuwar su".

@التبصرة (٤٩٣/٢)

Allamat Abdul Hamid bn Badis Allah ya yi masa rahama, albarka da daukaka Yana cewa:- An ɓoye daren Lailatul Ƙadri ne dan wanda zai neme shi kaɗai sai wanda yake neman lahira fiye da duniya sai ya nace cikin neman sa cikin kwanaki goman karshe dan ya dace da wannan dare..... "

@آثار ابن باديس

 Allah ne Mafi sani

ME YA SA AKA ƁOYE DAREN LAILATUL QADRI?

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu Alaikum Malam Khamis da fatan ka sha ruwa lafiya. Tambayata ita ce shin meyasa aka ɓoye daren lailatul qadri?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa'alaikumus Salam Warahmatullahi Wabarkatuhu.

Allah Madaukakin Sarki ya ɓoye sanin daren ne ga bayi don hikimarsa, da kuma rahmarsa ga bayi, don su dage da Ibada cikin dukkannin kwanaki goma na karshen watan, sai aikinsu na Ibada ya yawaita, ladansu ya yi yawa, su rabauta da yawan ibada; Sallah, Zikiri, Karatun Alkur'ani da Addu'o'i a cikin daren, sai su kara samun kusaci da daukaka a wajen Allah Madaukaki, su samu lada masu yawan gaske. Kuma ya ɓoye sanin daren ga mutane don yin jarabawa ga bayi, don masu kasala su bayyana daga masu himma da kokarin ibada. Don idan mutum yana neman abu to bai kamata ya zama mai kasala a neman ba, kamata ya yi a ga yana da himma da kokari mai yawa wajen nemansa.

Sheikh Ibn Uthaymeen Allah yayi masa rahama Yana cewa:- "Allah ya ɓoye ilimin daren Lailatul Qadri ga bayinsa, dan rahama ga bayinsa dan su yawaita aiyuakan ɗa’a acikin kwanaki goma na karshen watan Ramadan cikin neman wannan daren, da an sanya a wata rana ɗaya sananniya kamar ranar arfa to da sun yi ibada kaɗai Saboda ibadar dare ɗaya kaɗai zasu yi, amma da yake ya ɓoye hakan sai su yawaita ibada a daren goma gaba ɗaya suna neman dacewa da shi hakan yafi falala da Yawaita ibada da samu lada da matsayi mai yawa da girma a wajen Allah.

Dan haka ake so su yawaita yin waɗannan manyan ibadun a cikin waɗannan dararen don dacewa da daren Lailatul Qadri. Ibadun sun hada da:- Sallah, Zikiri da Addu'a da Karatun Al-Qur'ani.

Ibn al-Jawzi, Allah ya yi masa rahama, mai albarka da ɗaukaka Yana cewa:- Ayyub ya ruwaito daga Abi Qulabata yana cewa:- "Daren Lailatul Qadari yana chanchanzawa a kwanakin goman karshe na Ramadana, acikin mara, hikimar ɓoye wannan dare kuwa shine dan mutane su dage da Yawaita ibada a karshen watan Ramadana suna neman dacewa da wannan daren mai albarka, ibadar su da aiyukan ɗa’a na su ya karu tare da samu falala mai girma........ "

Ibn al-Jawzi, Allah ya yi masa rahama, mai albarka da ɗaukaka Yana cewa:- "An ɓoye daren Lailatul Qadri ne Saboda da manyan dalilai guda biyu:-

1. Rahama ga bayin Allah dan su dage da aiyuakan ɗa’a a kwanakin goman karshen Ramadana suna raya daren da ibada dan karshen wata ya zama sunyi aiyuakan masu yawa fiye da farkon Ramadana.

2. Dan su dage da aiyuka masu yawa Saboda ba su da tabbas ko zasu kara riskar wani Ramadan nan gaba, kila wannan shi ne Ramadan nasu na karshe a rayuwar su".

Allamat Abdul Hamid bn Badis Allah ya yi masa rahama, albarka da ɗaukaka Yana cewa:- An ɓoye daren Lailatul Qadri ne dan wanda zai neme shi kaɗai sai wanda yake neman lahira fiye da duniya sai ya nace cikin neman sa cikin kwanaki goman karshe dan ya dace da wannan dare..... "

'Yan'uwa, a cikin daren Lailatul Qadr Allah yana saukar da rahma, yana 'yanta bayi daga wuta, yana gafarta zunubai, yana rabon falala da arziki da lada mai yawa a kan ibada a cikin daren, ibada a daren ya fi ibada a wata dubu. Ku yi kokari wajen neman wannan alheri da albarka mai yawa mai girman gaske. Kwanaki ne kadan, ku dage a cikinsa kar ku yi kasala.

Allah Ya karɓa mana Ibadunmu, Ya gafarta mana zunubanmu, Ya taimake mu a kan kiyaye Azuminmu, Ya nufe mu da yawaita aiyukan ɗa'a a cikin wannan wata, ya shiryar da mu hanya madaidaiciya. Ya sa mu dace da daren Lailatul Qadr. Ya jikan iyayenmu, Ya yaye mana matsaloli da fitintinu da suke damun kasarmu, na kuncin rayuwa da rashin tsaro da aminci, Ya ba mu shugabanni nagari, masu tsoron Allah da kishin al'umma da tausayin talakawa. Ameen Ya Hayyu Ya Qayyum.🤲

WALLAHU A'ALAM.

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/Du5LNx31U9hDi6RƘbbrzgW

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments