𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Malam Ina Matsalar Zakkar Fidda kai ga wanda ba shi da
halin fitarwa.?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Ba'a bin Mutum bashin Zakkar Fidda kai Ga wanda ba shi da
halin da zai Fitar ya bayar. Zakkatul Fidri ta Sauka a kansa. Asalima Shi ya kamata a dauka a Baiwa. hikimar yin zakkar
Fidda kai kamar yadda manzon Allah ﷺ ya Ambata shi ne. Domin a wadata Waɗanda ba
su da Abincin da zasu ci na wannan Ranar. Ke nan A Kame Hannuwansu daga Rokon
Mutane na tsawon Wannan Ranar Gabaki ɗaya. Kuma a Sanya Farin ciki a zukatansu.
Suma suke jin su a Wadace.
Allah shi ne Masani.
Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin
mu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/K7RkƘRMf2b57l3UENoJ1Or
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
Post your comment or ask a question.