𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Idan mace ta yi tsarki da rana a watan Ramadan, ko matafiyi ya dawo gida da rana a watan Ramadan, shin yana wajaba a kansu su kame bakinsu??
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Shaikh Ibnu baaz Allah ya masa rahama yana cewa
"yana wajaba a kansu su kame
bakinsu, wannan shi ne zance mafi inganci cikin zantukan malamai, domin uzurin
da ya ba su damar ajiye azumin ya kauce, kuma za su rama azumin wannan yinin.
Haka da ace bayyanar watan Ramadan zaizowa Musulmai da rana da ya wajaba musu
su kame bakunansu, sannan kuma su rama azumin wannan ranan kamar yadda jumhurin
malamai suka tafi akai, haka shima matafiyi idan ya dawo da rana zai kame
bakinsa saboda gushewar hukuncin tafiya akansa kuma zai rama azumin wannan ranan".
سبعون مسألة مهمة في الصيا.
WALLAHU A'ALAM
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/Du5LNx31U9hDi6RƘbbrzgW
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
No comments:
Post a Comment
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.