Wata budurwa ce ana sauran sati guda aurenta, sai mijinta ya turo mata saƙo cewa: "Ki yi haƙuri, ba zan samu damar aurenki ba. Yanzu haka nan da sati biyu za a ɗaura mini aure da Laraba." Ita kuwa larabar babbar ƙawar budurwar ne.
Ba a jima da yin haka ba sai aka aiko wai ana kiran ta a waje. Fitar ta ke da wuya sai ta tarar da baban saurayin ne ya zo wurinta. Kuma ya zo ne damagar yana so ya aure ta. Ta koma gida domin ta yi shawara.
Jimawa kaɗan kuma sai aka sake kiran ta daga waje. Da ta fito sai ta ga baban ƙawarta Laraba ne ya zo. Shi ma yana so ya aure ta.
Idan ke ce yaya za ki yi? Za ki auri baban saurayinki da ya guje ki ne, ko za ki auri baban ƙawarki da ta ƙwace miki saurayi?
Za ku iya rubuta ra'ayoyinku a sashen comment da ke ƙasa.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.