𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum malam shin mata za su iya zuwa masallaci
sallar Tahajjud?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Hadisai masu yawa sun zo kan zuwan mata masallaci don
sallar Tahajjud ko Tarawihi. Sayyidina Umar Allah ya ƙara masa
yarda ya sanya limamai guda biyu : Ubayyi ibn Ka’ab da Tamimud Dari daya na
maza limanci ɗaya nama mata. Kuma duk sallar da ake yi mata na halarta,
kuma raka’a goma sha ɗaya suke yi (Muwatta) Hakanan ma Tuhajjudi da ake zuwa
cikin dare suma mata ya halasta suje amma da izinin mazajensu ko iyayensu in ba
su da aure iyayensu za su tambaya kafin su fita zuwa masallaci, amma in ana
tsoron fadawa cikin fitina to babanta ya kaita ko mijinta ya kaita ko kuma ta yi agida in za ta iya yi, baba ko miji kar yahana ‘‘yarsa ko matarsa zuwa
masallaci sallar Tahajjudi koTarawihi tun da ya zo a cikin Bukhari wanda manzon
Allah (s.a.w) ya ce ‘‘Kar ku hana mata bayin Allah zuwa masallaci in matar daya
daga cikinku ta nemi izinin zuwa masallaci to kar yahanata. (Bkhari).
Amma kuma duk da haka da za ta yi agidanta ya fi lada haka hadisi ya tabbatar ko da ko a Makka
take ko Madina ta yi a gida ya fi da
ta je masallaci.
Ita kuma matar ko yarinyar dolene ta nemi izini kafin ta
fita zuwa masallaci in ta je bada izinin uba ko miji ba ta saɓama Annabi
(s.a.w) kuma ana ji mata tsoron fadawa cikin halaka na saɓama Manzon Allah
(s.a.w) Kuma da mata za suyi sallarsu a gida yafi
lada da suje masallaci haka hadisai suka tabbatar mace ta yi sallah a gida ya fi da ta je masallaci.
Hadisi ya tabbata Ummu Humaidi ta zowajen Manzon Allah
(s.a.w) ta ce ‘’ Ina son in riƙayin sallah tare da kai a masallacin ka sai Manzon
(s.a.w) ya ce mata ‘’’ Nasan kina son
kiyi sallah tare dani to amma kiyi sallarki adakin ki ya fi maki alheri da kiyi sallah a masallaci. (’’ Ahmad 6/371 da ibn
Khuzaimah 3/95.
Gaskiyar labari dai shi ne mace ta yi sallarta agida ya
fi lada da daraja da mutunci da ta je masallaci. ya kamata mata su gane cewa
sallar su a uwar dakinsu ya fi lada da
ta yi afalo, haka hadisi ya nuna.
Duba Attamhid na ibn AbdulBar 23/398 ya
yi bayini sosai da ke nuna sallar mace adakinta ya fi lada da ta je
masallaci.
Mutane yanzu sun
mai da addini yayi, ba shara’a ba ya dai kamata Malamai su nuna ma mata abin da
ya ke daidai ba ya yi ba. A duba
littafin Ahkamun Nisa’i na Amru bn Abdul Mun’in shafi na 20.)
Allah kasa mu gama lafiya.
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/CƘ9TMXMrWDx1y7sYye2znU
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.