Ticker

6/recent/ticker-posts

Gudale Wakar Soyayya: Misalin Gazal (Ghazal) Cikin Rubutattun Wakokin Hausa

Gazal, kamar yadda wannan muƙala ta Hausance kalmar ghazalɓangare ne ko wani nauin waƙa wanda asalinsa daga adabin Larabci yake. Farkonsa wani ƙaramin gutsure ne na wani nauin waƙar da ake kira ƙasiidah. Sannu a hankali gazal yana jan hankalin mawaƙa har dai a ƙarni na bakwai (Miladiyya) ya samu babban tagomashi a sanadin bunƙasar ilmi wanda Musulunci ya haifar. Wannan gutsuren ƙasida ya ci gaba da bunƙasa har sai da ya samu zama mai cin gashin kansa, ya zama waƙar gazal, wadda ba yar rakiya ba. Waƙar ta samu tagomashi babba har wasu alummomi suka sadu da ita suka maishe ta tasu. 

Gudale Waƙar Soyayya: Misalin Gazal (Ghazal) Cikin Rubutattun Waƙoƙin Hausa

Abdullahi Bayero Yahya
Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya
Jami’ar Usmanu ƊanfodiyoSakkwato
Email: 
bagidadenlema2@gmail.com 
Phone: 
 07031961302

 TSAKURE

Gazal, kamar yadda wannan muƙala ta Hausance kalmar ghazal, ɓangare ne ko wani nauin waƙa wanda asalinsa daga adabin Larabci yake. Farkonsa wani ƙaramin gutsure ne na wani nauin waƙar da ake kira ƙasiidah. Sannu a hankali gazal yana jan hankalin mawaƙa har dai a ƙarni na bakwai (Miladiyya) ya samu babban tagomashi a sanadin bunƙasar ilmi wanda Musulunci ya haifar. Wannan gutsuren ƙasida ya ci gaba da bunƙasa har sai da ya samu zama mai cin gashin kansa, ya zama waƙar gazal, wadda ba yar rakiya ba. Waƙar ta samu tagomashi babba har wasu alummomi suka sadu da ita suka maishe ta tasu. Ganin yadda wannan naui na waƙa ya samu karɓuwa a faɗin duniya shi ya sa wannan muƙala ta yi ƙoƙarin ta gano ko akwai shi a rubutattun waƙoƙin Hausa, waɗanda tushensu daga na Larabci ne. Muƙalar ta lura cewa akwai shi har kashi biyu cikin waƙoƙin Larabci: gazal na cikin ƙasida da gazal mai cin gashin kansa. To amma dangane da rubutattun waƙoƙin Hausa, muƙalar ta keɓe kanta ga kashi na biyu da ta kira gazaliya ko gudale. Ta kawo waƙar Alƙali Alhaji Haliru Wurno mai suna Gudale, wadda ya yi ga Alhaji Giɗaɗo Ibrahim Yabo, a matsayin kyakkyawan misali na rubutattar waƙar gazaliya ta Hausa.

1.1 Gabatarwa

Rubutattun waƙoƙi ɓangare ne na adabin Hausa wanda tushensa daga rubutattun waƙoƙin Larabci ne. Kafin Hausawa su sadu da Larabawa da addinin Musulunci, ba su da irin wannan ɓangare cikin adabinsu. Da yake waɗanda suka ƙirƙiro rubutattun waƙoƙi cikin adabin Hausa malamai ne kuma masana a fannin addinin Musulunci da adabin Larabci, sai rubutattun waƙoƙin Hausa suka ɗauko nauoi da sigogi, har ma da salailai irin na waƙoƙin Larabci, musamman waɗanda a ganinsu za su dace da manufofinsu na addini. Saboda haka ne wasu daga cikin waɗannan suka fi saura yawa a adabin Hausa. Misali, akwai waƙoƙin Hausa na waazi da na madahu birjik, kamar wada ayyukan Hiskett da Ɗangambo da Yahya suka nuna.[i] Haka kuma akwai waƙoƙin addua da na furua da na nasiha da makamantan haka.[i]

Akwai kuma wasu nau’o’in da waɗannan malamai, magabata suka aro ma adabin Hausa. Sai dai waɗannan nauoi ba su cika yawa ba. Wasu kuma ba duk ɗalibin waƙa ya damu da su ba, watakila saboda rashin sanin tarihinsu da na tunanin da akan sa wajen tsara su.

To daga cikin irin waɗannan waƙoƙi da ma ɓangarorin tsarinsu akwai abin da ake kira ‘ghazal’ da Larabci. Wannan muƙala za ta tattauna ne kan wannan tsari ko naui na waƙoƙin Larabci da muƙalar take iƙirarin cewa lalle akwai shi a waƙoƙin Hausa, aƙalla daga mawaƙan da suka naƙalci adabin Larabci musamman waƙoƙinsa da tarihinsu. An kawo wannan nazari da bayani ne ba don begen jiya ba. Aa, sai dai don a fahimci mufari, a gane yadda wasu abubuwa suka faro domin kada a yi musu mummunar fahimta har a kai ga liƙa wa wannan nau’i da ake kira ghazal na waƙoƙin Hausa abin da ba nasa ba, har ruɗu ya kai ga shiga dangane da shi a nazari.[i] Haka kuma ghazal yana nan bai mutu ba a waƙoƙin Larabci, har ma a yau wasu alummomi kamar na Turai sun are shi. Kada watan wata rana a ɗauka cewa ghazal daga can tushensa yake!

2.1 Ghazal Da Asalinsa A Waƙoƙin Larabci

Kalmar ghazal, daga harshen Larabci tushenta yake wanda ke nufin bayyana so ko ƙauna ta hanyar magana ga wanda ko wadda ake so; musayar magana ta soyayya da wanda ko wadda ake so.[i] A fagen waƙa kalmar tana nufin, wani nauin waƙa ne da ke bayyana tsananin raɗaɗin ciyon rashi ko rabuwa a ɓangare guda, da kuma matsanancin kyawo na masoyi ko masoyiya duk a lokaci guda.[i]

Tarihin ghazal ya faro ne tun a wajajen ƙarni na shida (ƙ. 6), wato a zamanin Jahiliyyah. A lokacin shi ghazal kashi ko ɓangare ne na daɗaɗɗiyar irin waƙar nan ta cikin waƙoƙin Larabci wadda ake kira ƙasiida. Ƙasiida waƙa ce da ake tsarawa mai kashi uku, kowane kashi na bin wani ba tare da zaren tsarin ya tsinke ba, amma kuma kowane kashi yana ɗauke da saƙo ko jigo dabam. Waɗannan kashe-kashe su ake kira:

a) Nasiib

b) Rahiil

c) (ɗaya daga sanannun jigogi a wancan zamani na Jahiliyyah, kamar yabo <madiih> da darasi<hikam> da zambo <hija’> da alfahari ko wasa kai <fakhr>)

Za a lura da cewa ba a ambaci kashin ghazal ba. To shi bai cikin manyan kashe-kashe. A cikin kashin farko yake, wato nasiib. Akwai abubuwan da kashin nasiib kan ƙunsa. Da farko, a jumlace kuma cikin taƙaitawa, ana iya cewa ibn Ƙutaibah[i] ya bayyana ma’anar ƙasida a wurin Larabawa[i] kamar haka:

Mawaƙi zai fara waƙarsa ta ƙasiida yana mai ambaton ƙasarsa ta haihuwa da kuma abubuwan da suka shuɗe cikinta. A nan zai yi juyayin waɗannan abubuwa tare da yin kira ga abokan tafiya da su tsaya (su saurare shi ya ambaci mutanen da suka yi rayuwarsu a ƙasar). Daga nan ne mawaƙin zai tsunduma cikin nasiib inda yake juyayin raɗaɗin soyayyarsa, da raɗaɗin rabuwa da masoyi/masoyiya, da bege da matsanancin son da yake yi ga masoyinsa/masoyiyarsa. Dalilin yin wannan magiya dangane da masoyi/masoyiya shi ne, sanin cewa begen mata abu ne da ke manne ga zukatan maza…

Idan mawaƙi ya kai nan, ya san ya tattara hankalin masu saurare. Sai ya shiga cikin rahiil, inda yake juyayin wahalar tafiya, kamar rashin samun kwana na yawan darairai da kuma zafin rana.

A kashi na uku ne da ke biye, mawaƙi zai shiga cikin ainihin jigon waƙarsa. Idan yabo ne yake son ya yi ga wani to a wannan sashin ne zai fara shi. Idan kuma zambo ne ko wasa kai ko darasi, duk dai a wannan sashi ne zai fara shi.[i]

 

2.2 Bunƙasar Ghazal Da Yaɗuwarsa A Sauran Adubban Duniya

 

Da wannan tsari ne waƙar da Larabawa ke kira ƙasiidah ta ci gaba da kasancewa har sai bayan da Musuluinci ya bayyana kuma ilmi ya watsu a ƙasashen Musulunci sakamakon Alƙurani da hadissan Manzo (s.a.w.). Kafin zamanin bunƙasar ilmi da saduwar adabin Larabci da wasu alummomi kamar Farisa da Pakistan da Afirka da sauransu, ghazal bai tashi daga zama wani ɓari na kashin nasiib cikin waƙar ƙasiidah ba. To amma da ilmi ya bunƙasa sanadiyyar nazarin Alƙurani da Hadissai da kuma cuɗanya da wasu alummomin da Musulmi suka kai, sai waƙar ghazal ta samu zama mai cin gashin kanta. Hakan kuma ya auku ne musamman a zamanin Khilafar Umayyah (daga 661 zuwa 750) da farkon Khilafar Abbasiyyah (daga 750 zuwa 1258). A lokacin ne kowane kashi na waƙar ƙasiidah ya zamo nau’i mai cin gashin kansa. Cikin waɗannan kuwa har da nauin ghazal wanda ya samu tagomashi daga mawaƙa. A halin da ake ciki, ba a ƙasashen gabas ta tsakiya da na gabas mai nisa da na Afirka kurum waƙar ghazal ta kutsa ba, har ma cikin ƙasashen Turai da na Amerika waƙar ta miƙe ƙafa. Hasali, yadda ta samu karɓuwa ta bunƙasa a nahiyoyin Asiya da Afirka, haka ta samu a Turai da Amerika tun a ƙarni na 19, farko a Jamus sannan sauraan ƙasashe da harsuna kamar Ingilish.[i]

A tsawon zamani, tun daga ƙarni na bakwai har zuwa ƙarni na 13, waƙar ghazal ta ci gaba da samun bunƙasa, har ya kasance aka karkasa ta zuwa nauoi dabam daban, kama daga nauin da ya shafi yabon masoyiya wadda ta zamo hakin-sama ga mawaƙi har zuwa ga nauin da ke zayyana jikin mace. Waƙar ta kasance nauin da muhimmin jigonta shi ne, nuna matsananciyar ƙauna zuwa ga masoyiya ko masoyi. Malamai, musamman na zuhudu da sufanci su suka fi yin ghazal cikin waƙoƙin da suke yi na yabon Allah ko wani shugabansu. A ƙasar Hausa irin wannan ghazal aka fi yi tun cikin ƙarni na 18 da na 19.

3.1 Ghazal A Ƙasar Hausa

Za a lura da cewa a adabin Larabci, ghazal ya faro daga kasancewa wani ɗan rakiya cikin waƙar da ake kira ƙasida tun a zamanin Jahiliyya, har ya rikiɗe zuwa lokacin da likkafarsa ta yi gaba daga ƙarni na bakwai ya zamo mai cin gashin kansa a madadin ɗan rakiya.

To a wannan ɓangare ne wannan muƙala za ta Hausance kalmar ghazal zuwa ‘gazal’. Za ta kuma bambanta tsakanin gazal na cikin waƙar ƙasida da kuma gazal zunzurutunsa, wato mai zaman kansa wanda kai tsaye mawaƙi ya bayyana soyayya a matsayin babban jigon waƙarsa. Gazal na cikin ƙasida zai ci gaba da amsa sunan asali, wato gazal. Ita kuwa waƙar gazal mai cin gashin kanta ta amsa sunan gazaliya ko gudale. Ga taƙaitaccen bayani kan kowace waƙa:

a) Gazal: baitocin da ke nuna tsananin soyayya da raɗaɗin rabuwa da masoyi ko masoyiya, wadda aka saka cikin waƙar ƙasida a matsayin baitoci yan rakiya kamin shiga cikin babban jigon waƙar ta ƙasida.

b) Gazaliya/Gudale (ba ‘gazaliyyat’ ta harshen Larabci da ke nufin jumlar gazal ba!): waƙar da aka tsara gaba ɗayanta tana bayyana tsananin so ga masoyi ko masoyiya, wani lokaci har da bayani kan raɗaɗin rabuwa ko yin nisa da masoyi/masoyiya

Kamar wada sauran ƙasashen da suka rungumi Musulunci sai adabin Larabci ya yi tasiri kan nasu adabin, haka adabin Hausa ya samu. Abin nufi a nan shi ne, bayan da Hausawa suka karɓi Musulunci sai hanyoyin neman ilmi, da irin ilmin shi kansa, da kuma adabinsu, ko dai suka sauya ko kuma suka samu tasiri daga waɗanda zuwan na Musulunci ya kawo. Misali, karatu a makaranta da samuwar rubutattar waƙa duka Musulunci ya kawo su. Ya kawo juyin-juya-hali daga neman ilmi ta hanyar tatsuniya da barantaka gun mai sanaa, zuwa makarantar allo da makarantar sani har ma da barantakar.[i]

Lokacin da Hausawa suka yi zurfi ga samun ilmin addinin Musulunci, suka zurfafa cikin sanin adabin Larabci, musamman cikin ƙarni na 18 da na 19, a zamanin Shehu Usmanu ɗan Fodiyo, sai nauin gazal ya samu shiga cikin rubuce-rubucen mallaman zamanin, amma fa waɗanda suka rubuta cikin harshen Larabci. A binciken da mai muƙala ya yi sai a ƙarshen ƙarni na 19 ne aka fara samun waƙar gazal ko gazaliya cikin harshen Hausa. A sannan ɗin ma waƙa ɗaya tak manazarta suka gano. Waƙar gazal da baitocin gazal sun zauna daram cikin waɗanda waɗannan malamai suka rubuta da Larabci a duk tsawon ƙarni na 18 da na 19. Misali, a waƙar da Shehu Usmanu ɗan Fodiyo ya rubuta cikin Larabci yana yabon Sayyid Mukhtar al-Kunti, akwai gazal a baitocin farko. Haka kuma Sarkin Musulmi Muhammadu Bello ya rubuta gazal. Junaidu (1985) yana ganin cewa a ƙarni na 19, Muhammadu Buhari ne, (ɗan uwan Sarkin Musulmi Muhammadu Bello), daga cikin marubutan ƙarni na 19 ya fi kowa rubuta gazal. Rubuta gazal cikin harshen Larabci a ƙarni na 19, abu ne wanda, kamar yadda Sambo Wali Junaidu ya yi nuni[i], tabbas ya auku ne saboda babbar manufar da mallaman zamanin suka sa a gaba. Wato manufar jaddada addinin Musulunci a ƙasar Hausa. Ba su bukatar su cusa shaawar waƙoƙin soyayya ga zukatan mabiyansu a madadin samun ilmin addini. To da yake waƙoƙi cikin harshen Larabci a wancan lokacin sai waɗanda suka yi zurfi cikin harshen ke iya fahimtar waƙoƙin da aka rubuta cikin harshen, sai suka keɓe gazal cikinsa.

A iyakar binciken mai wannan muƙala, sai a ƙarni na 20 ne waƙoƙi gazaliya cikin harshen Hausa suka yawaita, duk kuwa da cewa a ƙarshen ƙarni na 19 an samu waƙar gazal ɗaya cikinsa.[i] Marubuta waƙoƙi biyu, Saadu Zungur da Muazu Haɗeja, duk sun rubuta gazal cikin wasu waƙoƙinsu, duk da cewa manazarta za su iya su kalli gazal ɗin a matsayin gabatarwa cikin waƙoƙi biyu na waɗannan marubuta. Waƙoƙin dai su ne Arewa Jumhuriya Ko Mulukiya[i] ta Zungur da ‘Tutocin Shehu Da Waninsu’ ta Haɗeja. Waƙoƙin duka biyu suna ɗauke da babban jigo na siyasar Nijeriya, amma a farkonsu sai marubutan suka kawo jigon da ke bayyana ɓurɓushin ƙauna ga sarakunan Arewa. Bayan wannan sai marubutan suka shiga babban jigon siyasar Nijeriya tare da nuna haɗarin da ke ƙalubalantar Arewa. To idan aka yi laakari da bayanin da ya gabata cikin wannan muƙala za a lura da cewa duka waƙoƙin nan biyu na Zungur da Haɗeja waƙoƙin da ake kira ƙasida ne. Baitocinsu na farko kuwa suna cikin nasib na tsarin ƙasida. Haka nan kuma cikin nasib ɗin ne gazal yake.

To amma a ra’ayin wannan muƙala, waƙar da kai tsaye za a iya a kira gazal ko gazaliya’ ita ce waƙar Alƙali Alhaji Haliru Wurno wadda ya kira Gudale.[i] Wannan waƙa ita ce za a gabatar a matsayin misali na yadda marubuta waƙoƙin Hausa, musamman masu zurfin ilmin waƙoƙin Larabci, suke sanya gazal cikin waƙoƙinsu. Sai dai shi Haɗeja waƙarsa muhammasa ce, ba ‘yar ƙwar bibbiyu ce saɓanin yadda ƙasida da gazal na Larabci suke ba.

4.1 GUDALE:Waƙar Yabon Alhaji Giɗaɗo Ibrahim Yabo

4.1.2Bayanin Diddigin Waƙa

Marubucin wannan muƙala ya samo wannan waƙa daga hannun marubucinta a shekarar 1986, kuma kamar yadda mawaƙin ya saba, ya rera ta a gabansa, a ƙofar gidansa cikin garin Wurno. A wannan lokaci yana mallamin Arabiyya da addini a makarantar Sakandare ta Wurno. Shugaban makarantar shi ne Alhaji Giɗaɗo Ibrahim Yabo. Haliru ya sheda wa marubucin nan cewa wannan shugaba ya nuna masa ƙauna da girmamawa ainun. Ya ba shi duk irin goyon bayan da malami ke bukata don ya gudanar da karantarwar da aka sa shi ya yi. Saboda haka ba abin mamaki ne ba a ga Haliru Wurno ya tsara waƙa musamman don nuna ƙauna ga wannan shugaban makaranta.

Babu tabbacin shekarar da aka yi wannan waƙa sai dai ana iya ƙiyastawa, cewa a cikin shekarun da Alhaji Giɗaɗo yake shugaban kwalejin horar da malamai ta garin Wurno ne aka tsara ta, kuma Haliru yana karantarwa a lokacin. Wannan lokaci kuwa shi ne, tsakanin 1981 da 1988.

Waƙar yar tagwai ce mai baiti ɗari cif cif. Tana da amsa-amon ciki da na waje. Wato ƙarami da babba wanda ba ya sauyawa tun daga baiti na ɗaya har zuwa na ɗari. Wannan babban amsa-amo kuwa shi ne, ni. Waƙar ta samo sunanta ne daga kalmar ‘gudale’ da aka yi salon kinaya da ita. Gudale dai ita ce nagge fara, kyakkyawa, mai babbar hantsa, wadda ta fi sauran shanu kyawon ƙira da lafiya. Cikin shanun ƙasar Hausa kaf, gudale ta fi kyawon jiki da babbar hantsa mai yawan madara. Ana yi mata kirari da, ‘Gudale karsanar shanu’. Idan kuwa aka ce mutum karsani ne, to, ana nufin ya fi sauran jama’a kyawawan halaye da ma ƙirar jiki. Saboda haka salon kinaya da Haliru ya yi da Gudale, yana nufin Alhaji Giɗaɗo Ibrahim Yabo. Ke nan a cikin mutanen da Haliru ya sani, Giɗaɗo ne ya fi yawan kyawawan halaye kuma mai kyawon halitta.

4.1.3 Bayanin Diddigin Mawaƙi

An haifi Haliru Wurno cikin shekarar 1925 a ƙauyen Ƙwargaba na ƙasar Wurno ta Jihar Sakkwato. Abin lura a nan shi ne, Haliru Basakkwace ne kuma Bagiɗaɗe. Sarauta ce ta kai kakansa a Wurno inda ya yi Sarkin Rima. Saboda haka Haliru Wurno, mai iya zama Wazirin Sakkwato ne da ya kasance a raye har yanzu.

Haliru Wurno ya tashi cikin zuri’ar da ilmi ne safararsu. Wato Giɗaɗawa, waɗanda suka samo sunansu daga Usman Giɗaɗo ɗan Laima. Shi kuwa Giɗaɗo shi ne wazirin Sarkin Musulmi Muhammadu Bello ɗan Shehu Usmanu ɗan Fodiyo, Allah ya yi musu rahama, amin. Bagiɗaɗe ba ya da wani abin tinƙaho da ya wuce ilmi da neman sa. Saboda haka Haliru ya buɗe ido da neman sani. Ya yi karatu a gida da kuma makaranta kamar sauran giɗaɗawa. Ya yi karatun allo da na sani a makarantar Liman Macciɗo a garin Sakkwato. Manyan malamansa na karatun sani sun haɗa da Liman Macciɗo da Malam Joɗi ɗan Waziri Abdulƙadir Macciɗo da Waziri Junaidu ɗan Waziri Muhammadu Buhari (ƙane ne ga waziri Macciɗo), duk a Sakkwato. A Wurno kuwa akwai Malam Bayero da Malam Abubakar Uban Lale. Haka kuma Haliru ya yi karatu a makarantun zamani na lokacinsa. Tsakanin shekarar 1943 da 1947 ya yi makarantar da ake kira “Sokoto Qadi School”. Malamansa a makarantar sun haɗa da Waziri Junaidu da Malam Ahmadu Ɗan Hannun Giwa.

Haliru yana sauka a wannan makaranta sai ya zarce zuwa makarantar nazarin ilmin Sharia ta Kano, wato ‘Kano Law School’. Ya shekara huɗu a can inda ya kammala a 1951. Malamansa a wannan makaranta sun haɗa da Shaikh Awad Muhammad Ahmad da Malam Nasiru da kuma Malam Abubakar Gumi. Haliru yana kammala wannan makaranta sai aka ɗauke shi aiki a matsayin malami mai karantar da ilmin addinin Musulunci da Larabci a makarantar Maru wadda a lokacin ake kira Elementary Training Centre (E.T.C.) Maru. To amma bayan shekara ɗaya da wata shida sai aka ɗauke shi aiki a maaikatar sharia ta lardin Sakkwato. Ya yi aiki nan a matsayin akawun kotu tun daga 1952 har zuwa 1965, lokacin da ya bari ya koma ga karantarwarsa. Ya zauna a makarantar Nizamiyya ta ‘Yar Akija a garin Sakkwato a matsayin malamin addini da Larabci. A lokacin ne ya rubuta ‘Waƙar Fanda ko Waƙar Danja wadda ta shahara a tsakankanin yan makaranta a Sakkwato da kewaye. Shekara biyu da yan watanni ya yi yana karantarwa a Nizamiyya kafin maaikatar sharia ta neme shi da ya koma ya yi alƙalanci. Ya karɓi wannan gayyata ya kuma ci gaba da aikin har zuwa 1981 lokacin da ya bari don ganin damarsa, ya sake komawa ga karantarwa.

A taƙaice dai Alƙali Haliru Wurno, karantarwa da alƙalanci ne ayyukan da ya yi. A sanadiyyarsu ya zauna garuruwa da dama a yankunan Sakkwato da Zamfara da na Argungu.

A Sakkwato ne Allah ya karɓi ran Haliru cikin gidansa na Kwalejin Fasaha Da Larabci ta Abubakar Gumi, ranar Alhamis 16 ga Oktoba na 2003 bayan sallar La’asar kuma kusan sallar magariba. Allah ya gafarta masa dukan kurakuransa, ya saka masa da aljannar Firdausi, amin.[i]

4.1.4Gudale: Gazal Na Waƙoƙin Hausa

An riga an yi bayani cewa gazal ɗin da ya fito cikin waƙar da ake kira ƙasida, shi ne zai riƙe sunan gazal, a yayin da wanda aka samu mai cin gashin kansa a mazaunin waƙa shi ne a nan za a wa laƙabi da gazaliya. To ita waƙar Gudale a wannan muƙala an ɗauke ta a matsayin gazaliya, ko ma a ba ta suna, Gudale, saboda laakari da yadda Hausawa ke son nagge gudale.

Za a iya raba waƙar zuwa kaso biyu kuma daidai wa daida. Kashi na ɗaya shi ne baiti na ɗaya zuwa na hamsin. Kashi na biyu kuwa daga baiti na 51 zuwa na 100. Kaso na ɗaya ya ƙunshi raɗaɗin da mawaƙi ya ji saboda rashin mai kula da shi, wanda zai ɗauki nauyinsa da shi da lalurorinsa. Shi kuwa kaso na biyu ya ƙunshi daɗin da mawaƙin ya ji saboda samun Giɗaɗo ya rungume shi, ya ɗauki kowane irin nauyinsa. Sharhin waƙar zai kasance a kan waɗannan ɓangarori biyu.

4.1.4.1Raɗaɗin Rashin Masoyi

 Alhaji Haliru Wurno ya buɗe waƙar Gudale da irin baitocin da ake kira basmala, yana cewa:

1. Na yi kiran Allah shi ishe ni

 Al’amarin ga da yad dame ni

2. Na yi salatu ga Hairil halƙi

 Ahmada ya zo man da Mubini

3. Na yi salatu dubu da salama

 Alaihi wa alihi ahlid dini 

A baiti na ɗaya Haliru ya cika wata ƙaidar waƙar da ake kira ƙasida, wadda ta bukaci mawaƙi yin amfani da amsa-amo mai kiɗa, wato inda amsa-amon ciki da na waje duk iri ɗaya ne, kuma hakan yana nuni da cewa wannan shi zai kasance amsa-amon waje a duk tsawon waƙar. Ba mamaki saboda gazaliya waƙar da ta samo yanci ce daga nasiib na cikin waƙar ƙasiida

Abu na biyu da za a lura da shi a nan shi ne, a ɗangon farko na baiti na ɗaya, mawaƙin ya fara shigar da nauin nasiib (nau’in da ke ɗauke da gazal). Roƙon da ya yi na Allah ya /ishe/ shi, manuniya ce ta irin raɗaɗi ko juyayin ciyon rashin masoyi ko nisansa daga Haliru. Kalmar tana nuni da cewa mawaƙin ya matsu, bai da ƙarfi bale ya fitar da kansa daga matsuwar. Yana roƙon Allah da ya tabbatar da ɗorewar soyayyar da ke tsakaninsa da masoyin da zai ambata cikin waƙar can gaba, masoyin da zai gabatar da salon kinaya, ya kira shi Gudale’

Bayan Haliru ya gama yin wannan addu’a a baiti na 4 sai ya faɗa mana cewa ƙara ce yake gabatarwa domin ya tabbata bai iyawa da annamimancin da ake yi masa don a raba shi da masoyinsa. Ya yi haka ne a baiti na 5,

5. Na zaka ƙara na kawo ta

 Jalla gare ka ka dai dube ni

To amma bai kawo cikon wannan tunani ba sai a baiti na 65 da na 66, inda ya yi amfani da ‘salon hira’[i] ya cusa cikon tunanin da ya kawo a baiti na 5 ɗin ga bakin ɗalibansa,

65. Nasiru ya ce Baba ka duba

 Ba a yi ma wani takin reni

66. Na san dauri kana makaranta

 Gulma akai maka don ka yi muni[i]

A tsakanin waɗannan baitocin ne Haliru ya shiga tumƙar jigon soyayyar da ke tsakaninsa da shugaban makarantarsa, ta hanyar kawo sunayen waɗanda ya tafi wurinsu don su rungume shi. To amma duk wanda ya nufa ko dai ya kore shi ko ma ya nufi cuta masa.

Mai karatu ko saurare ba zai yi saurin lura da wannan tumƙa ba sai ya kai inda mawaƙin ya ambaci gudalensa a can da nisa. Dalilin haka kuwa shi ne, Haliru ya yi amfani da salon laƙabi, inda mawaƙi kan tsara magana ta amfani da wasu abubuwa musamman dabbobi domin ya ɓoye haƙiƙanin manufarsa, ko kuma dangane da wasu mutane da bai son ya bayyana sunayensu. A wannan waƙar, ta amfani da salon shillo[i] Haliru ya bayyana yadda ya sha sheƙawa zuwa ga wasu dabbobi (mutanen da ya sani) domin ya samu agajinsu, ya ji sanyi saboda rashin da yake hange ya same shi (gulmar da yake ganin an sa tsakaninsa da masoyinsa), amma duk a banza. Ba dabbar (mutumin) da ta tausaya masa. Da farko, lokacin da Haliru ya ga haɗarin da yake ciki:

6. Na ga rashin abkin kayana

 Don haka tsoro ya ribce ni

7. Na ga dare da subahin haske

 Ga kuma rana ta dushe ni

8. Na yi farat na sheƙa inwa

 Na ga kwamarci ya kore ni

Wannan tsoro da ya kama shi ya sa Haliru ya ruɗe har ya rasa inda zai yi:

9. Na ga ruwan gulbi na zallo

 Na zo na shiga sun toye ni

10 Na tuma na koma can ganga

 Ba wani mai jinya ya fake ni

A nan laƙabin ruwan gulbi watakila yana nufin wani mutum ko wasu mutane da mawaƙin ya sani kuma yake hangen suna da hali da zarafin su rungume shi. To amma lokacin da ya je gun su sai ya tarar da (watakila) su ne suke neman raba shi da masoyinsa. Ruwan gulbi ne masu zafi da ƙuna. Saboda haka ne mawaƙin ya bar waɗannan mutane don ya sake shawara, duk kuwa da cewa yana cikin jin raɗaɗin abin da suka ƙara yi masa na cuta. A ƙarshe dai sai ya zaɓi ya je wurin waɗanda ya san masu hali ne don ya zama bara gare su. Wato dai ya kwaikwayi tsuntsuwar nan balbela wadda ke bin shanu don ta yi kiyo. Duk lokacin da tafiyar shanu ta tayar da fari sai balbela ta bi su ta kama. Sai ta samu abinci albarkar shanu. Haka Haliru ya zaɓi ya yi, albarkar masu hali ya samu nasa abinci.

Haliru ya nufi giwa amma sai ta zabura ta sheƙa da gudu ta bar shi. Sai Haliru ya nufi karkanda wanda nan take ya kore shi. Ya wuce zuwa gidan zaki sai ya tarar ba ya nan. Zaki a tunanin Hausawa sarki ne. Sarki kuwa mai ceton talakawa ne, mai taimakon mara ƙarfi ne. Saboda haka da mawaƙin ya ce zaki /bai nan/, watakila yana nufin ya je ne wurin wani mai riƙe da wani babban muƙami don ya taimake shi sai shi mawaƙin ya kasa samun ganin wannan mai muƙami bale ya taimaka masa.

Haka dai Haliru ya riƙa kai koke inda dabbobi (mutane) dabam daban waɗanda suke da irin nasu halin, don su taimaka masa. Kama daga masu iko zuwa ga masu ƙarfin yi, da waɗanda kome ba su iya taɓukawa, har zuwa ga waɗanda ta kansu kurum suke iya yi, da kuma masu biɗar wanda za su cuta:

24. Na ga barewa na tambai ta

 Inda gada take don ta riƙe ni

25. Na ce mat ta gwada mini hanya

 Inda gadar take ko ta rake ni

26. Na ga gada da gudu ta sheƙo

 Tac ce min tafi kar ka biyo ni

27 Na ga gudun da takai na ɓakita

 Na jaye mata ta hauro ni

28 Na yi ga zomo bawan Allah

 In shiga kurhinai ya fake ni

29 Na san zomo bai da mugunta

 Ko da gashin kansa ya ba ni

30 Na ishe kurhinai sai kashi

 Na ga kare yad dunfaro ni

31 Na riƙe sandata damana

 Kalbu iso in ɗebe reni

32 Na yi farat in mangare aura

 Kuba faƙyau yab bar ni anini

 

33 Na ga dila da biri ga kura

 Zaki na kusa yah haure ni

34 Na ce gawa ukku kuna nan

 Ba ni zama ƙura ta bito ni

 Kai har ma da masu ilmin addini waɗanda Haliru yake ganin cewa ƙarfin imanin da suke da, shi zai sa su taimaka masa. Haliru bai da abin da zai yi illa ya yi gaba! To amma duniya ta canza:

35 Na yi gabas wajjen yanyawa

 Kila dibaratai ta ishe ni

36 Na ishe limami yanyawa

 Ga ni mu’allimu zo ka daɗe ni

37 Na ga ashe shi ma tai zahi

 Sa’alabu ya ce tashi ka bar ni

38 Na yi zugum ya ce kai tashi

 Ba ka ganin inwa ta bar ni

39 Na yi zufa rana ga zafi

 Matata ita ma ta bar ni

40 Na ce Mallam ka san Allah

 Yac ce min ai shi yay yo ni

41 Na ce dubi hadisin tanyo

 Ba ka yi min girman addini

42 Na ga kamar maganar ta kammai

 Sa’alabu ya ce kai ka fi ni

43 Na ga kana iya kanka da kawo

Kwanana huɗu ban da sukuni

44 Na yi biɗar ƙannen matata

 ‘Ya’yana huɗu dut sun bar ni

45 Na ce assha na sa ƙaimi

 Kar ya tumam mini ko ya buge ni

 

A waɗannan baitoci ya yi amfani da salon laƙabi domin ya ƙirƙiro salon yanka. Wato ya yi kakkausar suka ga masu ilmi a wannan zamani. Baitocin suna nuni ne da cewa za ka ga muitum ya tara ilmi, yana sane da kowane umurnin Allah da Manzonsa kan yin taimako ga mabukata, amma kuma su ne kan gaba a bahilci, kamar yadda ’limami yanyawa’ ya yi da Haliru! Duk da girmamawar da Haliru ya ba shi, ya ce, /Ga ni mu’allimu zo ka daɗe ni/, muallimun kuma limami ɗin bai ji nauyin korar Haliru ba.

Hausawa sun ce, babu maraye sai raggo. Haliru ya ci gaba da neman wanda zai iya tausaya masa har dai Allah ya amshi roƙonsa, ya kai shi inda garken shanu. A cikin shanun ne ya samu jin sanyi kuma ɗayansu ta karɓe shi hannu bibbiyu, ya shiga daula:

46 Na fita na yi gudu bisa dutsi

 Na ishe shanu sun tarbe ni

47 Na ce shanu to don Allah

 Na zaka gun ku ku dai cece ni

48 Na ga farar ‘yan nagge gabana

 Ga ta fara sai tan nuno ni

 49 Na ga ta tunan shi taka niyya

 Na ja baya ƙafa tai duni

 50 Na sheƙa ga gijen hankaka

 Nij ji kiran baƙara ta biyo ni

51 Na koma ma gudale ga shanu

 Mai hantsa cike ta karɓe ni

A nan ne mawaƙin ya canza rawa, daga nuna ƙauna a kaikaice zuwa ga wanda yake wa waƙar, ya fito sarari ya bayyana wa masu saurare ko karatun waƙarsa wanda yake ƙauna yake kuma yabo. Ya kuwa gabatar da wannan bayani ne ta amfani da salon hira tsakaninsa da ɗalibansa:

52 Na yo zane yara ku gane

 Wagga gudale da taƙ ƙwasshe ni

53 Na san ɗana kila Basiru

 Zai iya ganewa ya rige ni

54 Nasiru ya ce na san naggen

 Ɗan Ibrahi na mai auni

55 Alhaji na kuma babban zaure

 Babu irinai bai son reni

56 Alhaji wanga Giɗaɗo tsayayye

 Shugaba na mai son addini

Haka Haliru ya ci gaba da nuna ƙauna da yin yabo ga wannan gudale (Giɗaɗo Ibrahim) har zuwa ƙarshen waƙar. Ya tabbatar ma ɗalibansa da cewar da suka yi ai ‘gudale’ da ya ambata ba kowa ba ne face Giɗaɗo, shugaban makaranta. Tsananin ƙaunarsa ga wannan Gudale ta kai ƙoli don kuwa Haliru ya ce,

70 Na ce yara ɗiya kun gane

 Giɗaɗo Faransafa yai ihsani

71 Na saki al’amarinsa gaba ɗai

 Ba ni da ja to mit tiƙo ni

72 Na yi biya na ba da amana

 Ban ga mutum ba da yaɗ ɗauke ni

73 Na san ba a yi mai fadanci

 Ya san Allah kowane fanni

Waƙar yabo ga masoyi ba ta rabuwa da zambo da zolaya. A kan haka ne Haliru ya soki ‘yan adawa waɗanda su ne watakila yake ganin su ne masu yi masa ƙullin sharri ga shugabansa kuma masoyinsa:

74 Na ga ƙudara da bai son hairi

 Ya game huskatai ya bar ni

75 Na ga maƙarhu ɗan mazari ko

 Ya yi ɗuminai ya soke ni

76 Na ga ƙudan tsando ya cizan

 Sai bararoji da yaz zole ni

77 Na manguwa ɗan zomo ya shura

 Wancan durwa baƙi ya ƙi ni

78 Noƙe da kai ƙarya yaka kaya

` Sai ƙazafi da ƙire yai shaini

79 Na gane ma macijin ƙaiƙai

 Ban da sane sai yac cije ni

80 Na ga zaman ga ga yau na shirya

 Ba ni bari kuturu ya buge ni

A waɗannan baitoci Haliru ya yi kusa da ya ambaci sunayen waɗanda yake yi wa zambo. To amma sai ya yi amfani da salon kinaya ya yi habaici. Ta haka da su ɗalibansa, da mallaman cikin makarantar da kuma shi kansa masoyin Haliru, duk za su iya su gane ko da wa yake. Dukansu suna iya gane mutanen domin suna zaune tare da su cikin makaranta kuma sun san su. A can baya mun ji wani ɗalibin Haliru yana cewa:

65. Nasiru ya ce Baba ka duba

 Ba a yi ma wani takin reni

66. Na san dauri kana makaranta

 Gulma akai maka don ka yi muni

 

A ƙarshe, Haliru ya rufe waƙarsa kamar yadda waƙoɗin gazal da na ƙasida na Larabci kan rufe. Wato a baitin ƙarshe na gazal ko ƙasida mawaƙI kan faɗI sunansa amma a kaikaice. Shi Haliru har da ƙarin cewa kowane mutum ya san shi, ba sai ya fito ɓaro-ɓaro ba. Ga yadda ya sakaya sunan nasa:

 

100. Na gama waƙata Alƙali

Alhaji Wurno mutum ya san ni

KAMMALAWA

Wannan muƙala ta yi ƙoƙarin ta bi diddigin tushen waƙar da ake kira ghazal. Ta bayyana cewa irin wannan waƙa ta Larabawa ce, su suka ƙirƙiro ta tun zamani mai tsawo, kafin zuwan Musulunci. Muƙalar ta nuna cewa a can farko ghazal wani ɗan gutsure ne cikin wata sigar waƙar da ake kira ƙasiidah. To amma bayan Musulunci ya bayyana, ilmi ya bunƙasa, albarkar Alƙurni da Hadissan Manzo (s.a.w), sai wannan gutsure na ghazal ya bunƙasa, ya samu yanci daga ƙasiidah musamman cikin ƙarni na bakwai (ƙ.7) da na (ƙ.8). Tun daga wannan zamani ghazal ya ci gaba da yaɗuwa a duk faɗin duniya cikin adubba dabam daban.

A ƙasar Hausa kuwa wannan nauin waƙa ya samu karɓuwa ga malamai musamman na ƙarni na goma sha takwas da na sha tara (ƙ.18/19). To amma waɗannan malamai, cikinsu har da Shehu Usmanu ɗan Fodiyo da yayansa, Muhammadu Bello da Muhammadu Buhari, da kuma ƙanensa Mallam Abdullahi, dukansu cikin harshen Larabci suka rubuta ghazal. Sai a ƙarni na 20 zuwa yau, ƙarni na 21, aka fara samun gazal cikin harshen Hausa. Hana-rantsuwa ita ce waƙar Lisanul Hali da ta zo a ƙarshen ƙarni na 19.

Muƙalar ta kawo shawarar rarrabewa tsakanin gazal ta cikin ƙasida da gazal mai yanci. Gazal ta cikin ƙasida ta tsaya da sunan na asali. Gazal kuwa mai cin gashin kanta a kira ta gazaliya ko ‘gudale’, wato ta amshi sunan waƙar Haliru Wurno.

Abu ne mai amfani a nazarin waƙoƙin Hausa a yi waiwaye zuwa ga rubutattun waƙoƙin ƙarni na 18/19, da kuma na marubuta waƙoƙin Hausa na ƙarni na 20, musamman waɗanda suka taso da ilmin addini Musulunci tun ƙuruciyarsu har suka girma. A waiwayen nan, manazarta su nazarci waƙoƙin waɗannan marubuta ta fuskar tasirin da rubutattun waƙoƙin Larabci suka yi a kan nasu waƙoƙi. Ta haka ne za a iya zaƙulo wasu abubuwa da ba a lura da su ba can baya. Waƙar gazal ta je al’ummomi da yawa ta shiga cikin adubbansu, ta yi zaune dangalgal. Ta shiga cikin adabin Hausa, kuma ga dukan alamu za ta yunƙura ta yi yadda ta saba. Ta hanyar yin aro mai kyau, mai amfani ne adabin kowace alumma kan bunƙasa, ya inganta.

MANAZARTA

 

Abdulƙadir, Ɗ. (1978) The Poetry, Life and Opinions of Sa’adu Zungur, Zaria: NNPC.

Ainu, A.A. (2007), ‘Rubutattun Waƙoƙin Addua Na Hausa:Nazarin Jigoginsu Da Salailansu, kundin dfigirin Ph.D., Sakkwato:Jamiar Usmanu Ɗanfodiyo.

Birnin Tudu, S.Y. (2002), Jigo da Salon Rubutattun Waƙoƙin Furua na Ƙarni na Ashirin kundin digirin Ph.D., Sakkwato: Jamiar Usmanu Ɗanfodiyo.

Ɗan Fodiyo, A (1383 H.), Tazyin al-Waraƙaat, Mallam Abdullahi ɗan Fodiyo ya rubuta wannan littafi cikin shekarar Hijira ta 1228 H. (1813/14 Miladiyya).

Ɗangambo, A. (1980), Hausa Waazi verse from C.A. 1800-C.A. 1970. A Critical Study of Form, Content, Language And Style, kundin Ph.D, Jamiar London.

Ɗangambo, A. (2007), Ɗaurayar Gadon Feɗe Waƙa (sabon tsari), Zaria: amana publishers ltd.

ƊUNƊAYE: Journal of Hausa Studies 1-5, Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya (2004-20-14), Sakkwato: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

Haɗeja, M. (1980), Waƙoƙin Muazu Haɗeja, Zaria: NNPC.

Hiskett, M. (1975), A History of Hausa Islamic Verse, London.

Junaidu, S.W. (1985), “The Sakkwato Legacy of Arabic Scholarship in Verse Between 1800-1890”, kundin digiri na Ph.D., London: University of London.

Malumfashi, I.M. (2009), Adabin Abubakar Iman, Kaduna: Fisbas Media.

Malumfashi, I.M. (2002), “Ƙagaggun Labaran Hausa: Abin da Muka Sani da Wanda ba Mu Sani ba Ta Fuskar Tarihin Adabi”, takardar da aka gabatar a taron ƙara wa juna sani, Sakkwato: Jamiar Usmanu Ɗanfodiyo.

Sa’id, B. (1987), Dausayin Soyayya,. Zariya: Gaskiya.

Yahaya, I.Y. (2008), Hausa a Rubuce: Tarihin Rubuce-Rubuce Cikin Hausa, Zaria: NNPC.

Yahya, A.B. (1987), “Hausa Verse Category of Madahu with Special Reference to Theme Style and Background of Islamic Sources and Belief, kundin Ph.D., Jami’ar, Sakkwato.

Yahya, A.B. (2001), Salo Asirin Waƙa, Kaduna: Fisbas Media.

Yahya, A.B. (2003)“Rubutattun Waƙoƙin Nasiha: Wani Ɓangare Ko Kuwa Sauyin Salo A Cikin Rubutattun Waƙoƙin Hausa Na Waazi?, cikin ALGAITA Journal of Current Research in Hausa Studies vol 1, No 3, Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya, Kano: Jami’ar Bayero.

Yahya, A.B. (2004), ’Tsattsafin Raha Cikin Waƙoƙin Alƙali Alhaji Haliru Wurno, cikin ZAUREN WAƘA:Mujallar Nazarin Waƙoƙin Hausa 1 (2013), Sakkwato: Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

Yahya, A.B. (2012), ‘Tsattsafi: Wani Ɗigo Cikin Gulbin Nazarin Salon Waƙoƙin Hausa, cikin ƊUNƊAYE:Journal of Hausa Studies 5, (2013), Sakkwato: Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo

Yahya, A.B. da Idris, Y. (2014), ‘Gyara Ko Ɓanna: Gurɓata Waƙar Arewa Jumhuriya Ko Mulukiya’, muƙalar da aka gabatar a Taron Yamai (Jumhuriyar Nijar) domin Tuna da Karrama Marigayi Farfesa Muhammadu Hambali Jinju.

Yakubu, A.M. (1999), SA’ADU ZUNGUR: An Anthology of the Social and Political Writings of a Nigerian Nationalist, Kaduna: Nigerian Defence Academy Press.

ZAUREN WAƘA: Mujallar Nazarin Waƙoƙin Hausa 1, Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya (2013), Sakkwato: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

https://www.wordnik.com/words/ghazal: to display love to the loved one via speech; to exchange talk of love with the loved one, 05/04/2014, 02.03 a.m.

http://en.wikipedia.org/wiki/Ghazal, 05/04/2014, 02.45 a.m.

www.ghazalpage.net/prose/notes/short Jalajel, D. (2007).

- Waƙoƙin Alƙali Alhaji Haliru Wurno da marubucin wannan muƙala ya mallaka.

Gudale Waƙar Soyayya: Misalin Gazal (Ghazal) Cikin Rubutattun Waƙoƙin Hausa

Post a Comment

0 Comments