Ticker

6/recent/ticker-posts

GININ ƘASA: Rundunar Waƙoƙin Hausa A Fagen Yaƙi Da Rashin Tarbiyya

 Daga tarkar Farfesa Abdullahi Bayero Yahya.

Abdullahi Bayero Yahya
Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya
Jami’ar Usmanu ƊanfodiyoSakkwato
Email: 
bagidadenlema2@gmail.com 
Phone: 
 07031961302

1.0 Gabatarwa

Rawar da adabin Hausa, musamman fannin waƙa, yake takawa wajen gina alummar ƙasar Hausa daɗaɗɗiya ce. Tun fari dai Hausawa sun yi amfani da waƙar baka cikin wasanni da tatsuniya domin su cusa wa yayansu tarbiyya da aladu. Wannan rawa ta ci gaba tsawon zamunna har zuwa yau cikin sigogi mabambanta. Lokacin da rubutacciyar waƙa ta shiga cikin rayuwar Hausawa, sai rawar da adabinsu ke takawa ta wannan fuska ta faɗaɗa ta kuma ƙarfafa. A wannan muƙala za a yi ƙoƙarin bayyana hanyoyin da za a iya amfani da rubutattun waƙoƙi domin aiwatar da yaƙi da rashin tarbiyya a wannan zamani cikin Nijeriya. Waɗannan hanyoyi kuwa za su ƙumshi na da da na yanzu.

Ƙumshiyoyin da ke bukatar bayani a wannan muƙala su ne, yaƙi da kuma tarbiyya. Saboda haka bari a yi bayanin tun yanzu.

Ƙamusun Hausa ya bayyana kalmar “yaƙi, da cewa, ‘far wa wasu mutane da faɗa domin a mulke su.

 Idan aka faɗaɗa wannan maana sai a ce, ɗaukar mataki ko matakai domin a kawar da wata ɗabia ko alada ko cuta daga rayuwar alumma.

“Tarbiyya” kuwa wannan ƙamus ya fassara ta da cewa,

Koyar da hali na gari; hali na gari[i]

Shi kuwa kalamin ‘rashin tarbiyya’, yana nufin babu hali na gari, a yayin da ‘yaƙi da rashin tarbiyya ke nufin ɗaukar mataki ko matakai na kawar da hali ko halaye marasa kyawo. Ya kamata a lura da cewa duk waɗannan bayanai suna jinginuwa ne ga alummar da ake magana a kai. Misali, sutura mai rufe alaurar mutum alada ce a wannan ƙasa tamu, muddin dai ba za a yi amfani da ita a mummunar hanya mai cutarwa ga alumma ba. Rashin sanya sutura mai rufe al’aura ga mutum rashin tarbiyya ne a Nijeriya. Amma an nuna wa wannan marubuci wani gida a wata ƙasa ba ta Afirka ba inda aka ce wurin shaƙatawa ne da kowa ke cire suturarsa ko suturarta. Kuma ba a yarda ka zauna da sutura ba! Tirƙashi! Bahaushe dai ya ce, ‘Abincin wani gubar wani’!! Bari dai muƙalar ta fara nomanta.

2.1 Hanyoyin Amfani da Waƙa a Ƙarni Na 17 Zuwa Na 19

A nan idan aka ambaci zamanin da, manufa ita ce, lokacin da ya shafi wajajen ƙarni na 17 zuwa na 19, amma musamman ƙarni na 18 da na 19. An kuwa mai da hankali kan ƙarnonin 18 da 19 ne saboda dalilai biyu: kasancewar tarihi ya fi taskace rubutattun waƙoƙin zamanin fiye da na kafin sa, sannan a zamanin ne waƙoƙin suka samu ranar shanya, suka bunƙasa suka kuma zama cikin al’adun Hausawa, jini da tsoka.[i]

A shekara ta 1754 ce aka haifi Shehu Usmanu ɗan Fodiyo wanda jamaar zamaninsa ba su yi kuren baki ba da suka kira shi nur al zaman, wato, “hasken zamani”. Da shi da ƙanensa da yayansa da sauran mabiyansa sun yi amfani da rubutattar waƙa don su aiwatar da wa’azi ga jama’arsu domin su jaddada addinin Musulunci. Su ne suka mai da waƙoƙi tamkar yadda a yau hukuma take amfani da kafafen watsa labarai domin faɗakar da jamaa game da manufofinta. Shehu ya lura da cewa Hausawa suna shaawar waƙa, waƙa kuwa ta kasance ɗaya daga cikin hanyoyin da mallaman addini ke amfani domin yaɗa addini tun bai iso ƙasar Hausa ba. Waƙar Larabci da aka fi sani da Ƙurɗaba, ta isa misali, domin kuwa har yau ana koyar da ita a nan ƙasar Hausa, duk kuwa da cewa ta yo tafiya tun daga ƙasar Andalus (Spain a turance) [i][i], kuma a zamani mai tsawon gaske.

Su Shehu Usmanu sun rubuta waƙoƙin ne don su ƙarfafa waazin da suke yi a makarantunsu da sauran wuraren da suke yin waazin. Misali akwai Waƙar Waazu[i] da “Waƙar Mai Dare Duk Da Safiya” da “Tsarn Mulki Irin Na Musulunci” waɗanda Mallam Abdullahi ƙanen Shehu ya rubuta. Akwai kuma waƙar Tabban Haƙiƙa da Waƙar Lalura waɗanda shi Shehu ya rubuta. Nana Asmau yar Shehu ita ma ta rubuta, kamar Waƙar Tsayin Alƙiyama da Kirarin Ahmada”. Haka shi ma Malam Isa, autan Shehu da aka haifa bayan rasuwar mahaifinsa, ya rubuta waƙar Haƙƙin Mumini A Kan Mumini. Ya kuma fassara wasu waƙoƙin mahaifinsa da na yayarsa Nana. Mallam Abdullahi Mai Boɗinga ya yi tahmisin waƙar Shehu wadda Malam Isa ya fassara da sunan da ta shahara da shi, wato “Ma’ama’are”.

Waɗannan waƙoƙi da sauransu masu yawa[i] sun kasance ga hannuwan almajiran Shehu da na Mallam Abdullahi da na mabiyansu. Haka kuma akan rera su a masallatai daga su almajiran, kuma akan karanta wa almajiran makarantun allo lokaci lokaci.[i] A fadar sarakuna ma akan rera waƙoƙin.[i] Misali, akan aiwatar da wannan al’ada a gidan wazirin Sakkwato.

Marubuta waƙoƙin ƙarni na 17 19 ba rubuta su suka yi suka ajiye kurum ba. Aa, sun rubuta su ne domin su ƙarfafa karantarwa da waazin da suka yi ga jamaarsu. Sun rubuta su ne a matsayin wata hanya da suka yi wa alummarsu tarbiyya mai kyawo, su kuma yaƙi rashin tarbiyya. A taƙaice, hanyoyi da aka bi domin yaƙi da rashin tarbiyya a wancan zamani na ƙarni 18 da na 19 su ne, rubuta da fassara waƙoƙi cikin harsunan gida, da yaɗa su cikin ƙasa ga alumma ta hannuwan yan makaranta, da rera su a masallatai da wuraren waazi da makarantu, da kuma karanta ko rera su a fadar sarakuna. Haka nan kuma matan aure kan gayyato mata dattawa da ke da baiwar rera waƙoƙin domin su yi musu hira ta tsawon yini a gidajensu. Kada kuma a manta da rawar da yan taru[i] suka taka. Wannan ƙungiya ce da Nana Asmau yar Shehu ta ƙirƙiro domin ilmantar da mata. Ƙungiyar ita ce za a iya a kira da sunan ‘Shiri na farko a wannan nahiya na bayar da ilmi kyauta ga duk ilahirin mata na daular da Shehu Usmanu ya kafa’. Ita ce makarantar tafi-da-gidanka domin a duk ƙauyen da yan taru suka biya a kan hanyarsu ta zuwa Sakkwato ko komawa zuwa ƙauyukansu, sukan tafi ne suna rera waƙoƙi. Idan ko a gida suke sukan je gida gida su rera su. A yau watakila a kira wannan a Turance da, Free Mobile Education For All Women!

3.1 Hanyoyin Amfani da Waƙa a Ƙarni Na 20 Da Na 21

Ƙarni na 20 ya fara da zuwan Turawan Ingila a ƙasar Hausa, suka yaƙi ƙasar gaba ɗaya har sai da suka shimfiɗa mulkin mallaka, lamarin da kuma ya assasa canjin hanyar rayuwa. A sakamakon haka sai amfani da waƙoƙi ya ɗauki sabbin manufofi ƙari kan waɗanda jamaa suka gada daga zamanin da ya gabata.

Tun da fari dai malaman addini sun faɗaɗa manufar yin waazi da ilmantar da mutane kan addini, wato yaƙi da jahilcin addini, zuwa yaƙi da baƙin da suka zo suka yaƙe su, suka kuma kawo aladunsu da ba su yi daidai da addinin ƙasar Hausa ba. Waƙar Zuwan Annasara[i] ita ce manazarta ke ganin ta fara wannan sauyi, wanda ya kasance yaƙi da alƙalami domin ba a iya yaƙar Turawa da takobi a lokacin. Malam Abubakar Maikaturu da ɗalibinsa Malam Ibrahim Halilu suna daga cikin malaman ƙasar Sakkwato da suka yi wannan ƙoƙari.[i]

Cikin shekarun da Turawa suka yi suna shimfiɗa mulkinsu da aladunsu, marubuta waƙoƙin Hausa sun ci gaba da amfani da waƙoƙin domin su tarbiyyantar da yara da manyan ƙasarsu. Wato sakamakon abubuwan da Turawa suka kawo sai aka samu malamai iri biyu: da waɗanda suka ci gaba da amfani da waƙa domin ƙarfafa tarbiyyar Musulunci kamar yadda malaman ƙarni na 18-19 suka yi; da kuma malamai waɗanda ke amfani da waƙa domin cusa tarbiyya mai tafiya tare da sabon zamani, wato Turawa da abubuwan da suka kawo. A cikin waɗannan malamai na kashi na biyu akwai marubuta waƙoƙi kamar Malam Saadu Zungur da Malam Muazu Haɗeja da Malam Umaru Nasarawa Wazirin Gwandu. Irin waɗananan malamai sun yi amfani da waƙoƙi domin su wayar da kai ko su faɗar ko su tarbiyyantar da jamaa kan abubuwan da zamani ya kawo. Akwai waƙoƙinsu kamar Arewa Jumhuriya Ko Mulukiya da Tutocin Shehu Da Waninsu da kuma Yadda Ya Kamata Najeriya Ta Zama[i]. Haka kuma akwai waƙoƙi kamar Gargaɗi Ga Yan Makaranta da Waƙar Nijeriya da Hausa Mai Ban Haushi’, duk suna cikin cusa tarbiyya a fannoni mabambanta[i].

Ya kamata a lura da cewa daga cikin abubuwan da Turawa suka kawo a ƙasar Hausa akwai naurori da kafafe waɗanda suka taimaka wajen amfani da waƙa domin cusa tarbiyya ko yaƙi da rashinta. Waɗannan kuwa sun haɗa da rediyo da talibijin da sauransu. Ko bayan hanyoyin da suka saba da su tun shekaru aru aru, malamai sun kuma yi amfani da waɗannan naurori da kafafen watsa labarai don cusa tarbiyya ko yaƙi da rashinta.

Abin da ya fito fili shi ne, waƙa dai ta taka rawa wajen cusa tarbiyya tun daga ƙarni na 18 har zuwa yau da take cikin takawar. Yanzu muƙalar za ta mai da hankali ga yadda za a inganta wannan rawa, da ma ƙarin wasu hanyoyin.

Ya kamata a tattara hanyoyin amfani da waƙa waɗanda aka ambata tun farkon wannan muƙala har zuwa nan. Hanyoyin kuwa su ne:

1. Rubuta waƙoƙi domin ɗalibai da sauran jamaa.

2. Rera waɗannan waƙoƙi a gaban shugabanni (kamar idan malamai suka ziyarci sarakuna suka nemi su yi musu waazi).

3. Rera su a masallatai.

4. Rera su a makarantun allo.

5. Rera su da ƙungiyar yan taru ke yi daga ƙauyuka zuwa birane, kamar daga ƙauyen Tcehe zuwa Sakkwato, musamman cikin watan azumi, lokacin da suke sauraren tafsirin Nana Asmau.

6. Rera waƙoƙin a gidaje ga matan aure.

7. Fassara wasu waƙoƙin manyan malamai daga wani harshe zuwa Hausa. Misali, Waƙar Begore ta Mallam Tukur Ɗan Binta wadda Nana Asmau ta fassara daga Fulatanci zuwa Hausa, da Waƙar Maamaare wadda Shehu Usmanu ya yi da Fulatanci ɗansa Malam Isa ya fassara zuwa Hausa. Waƙar Daliyya ta madahu wadda Shehu Usmanu ya yi da Larabci, Ɗangaladiman wazirin Sakkwato, Bello Giɗaɗawa ya fassara ta zuwa Hausa.

8. Yi wa wasu waƙoƙi tahmisi kamar Waƙar Maamaare da Malam Isa ya fassara, sai Mallam Abdullahi Maiboɗinga ya yi mata tahmisi.

9. Rubuta waƙoƙi domin rerawa a taron siyasa.

10. Buga waƙoƙi cikin jaridu.

11. Rera waƙoƙi a gidajen rediyo da talibijin.

12. Rera wa ‘yan makarantun Islamiyya da na Boko waƙoƙin da malamansu kan rubuta.

13. Sanya waƙoƙin cikin kase-kases da faifan konfuta.

3.2 Tsakuren Baitoci A Lokutan Labarai Da Jawaban Shugabanni

A yanzu ne ya fi dacewa idan aka hukumta cewa a duk lokacin da shugabanni tun daga Shugaban Nijeriya har zuwa shugabannin ƙananan hukumomi za su yi jawabi ga yan ƙasa, ko a fili ko cikin kafafen labarai, to lalle a tsakuro wani ko wasu baitocin da suka dace da jawabin da zai yi. Haka kuma za a yi idan za a karanta labarai. Da yake ana yaƙi ne da cin hanci da rashawa ana iya amfani da waɗannan baitoci ko ɗaya daga cikinsu a rera kamin shugaban ya soma jawabinsa ko kamin a fara karanta labarai:

3. Yaƙi da rashin yin tarbiya

Cin hanci rashwa shan giya

Sata da fashi Najeriya

Sun kinkima ba mu da lafiya

 Ƙuma cuta sai Najeriya

 

Doki koya mai taƙama

Aka yi da matsi mai gardama

Sa mai ƙaimi ka yi mai tsuma

In ka ƙyale har yat tuma

 Rame zai kai ka cikin ƙaya

 

5.Kai shugaba in ka hanƙure

Kuma kai shayi yaƙ ƙetare

In ka hora yah hinjire

In ka yi laho yas sandare

 Zai ɓata dubu Najeriya

 

Taushe haƙƙi na mutum shikai

Zalumci shi na ɗai shikai

Kowa ya san yi nai shikai

Wani bai cewa an taimakai

 Halin manyan Najeriya

 

Jinsin wasu in ya kangare

Aika musu soja su tsattsare

Ka hana su tudu su yi gangare

Mabuga karnai na nan tare

 Yi da gaske ka bar wani tausaya

 

8. Ji takaici ni kam ya isan

Sarkin sata mai son shi zan

Shi riƙe samu gona ta zan

Mulkinai mu ko duk mu zan

 Banzar banza Najeriya

 (Alƙali Alhaji Haliru Wurno:Yaƙi Da Rashin Tarbiyya Da Rashawa)

A nan Haliru Wurno yana magana ne da shugaban ƙasa ko gwamna. Ya kasance wanda ke yi wa shugaba tunatarwa ko ma ba shi labari kan yadda wasu yan ƙasar nan suka zamo da kuma manufarsu ga ƙasar da mutanenta. Haliru yana son shugaba ya tashi tsaye ya nuna halin ba sani ba sabo. Wannan tunatarwa za ta sa wa shugaba ƙaimi wurin tabbatar da cewa doka ta yi aiki sosai.

Akwai kuma baitocin da ke yin kira ga Shugaba da ya bi waɗannan masu cuta wa ƙasa guda guda don a hukumta su. Suna da yawa don Haliru bai bar kowa ba:

23. Sannan a biyo ga sarakuna

Da ciyamomi da akawuna

A bi hakimmai sanatotuna

A bi darakatoci ko’ina

 A tsare su tsaro Najeriya

 

24. Ka ba su amana ci sukai

Fasa-ƙwabri shina nan yi sukai

Doka ko ka yo ƙi akai

Doka ko ɗai yasat sukai

 Ta nakkasa mu mun sha wuya

 

Haliru bai tsaya nan ba sai da ya fito ƙarara ya bayyana mummunar rayuwar da wasu shugabanni da ke ƙarƙashin Shugaba ke yi. Haliru sai da ya ja kunnen Shugaba da kada ya saki fuska:

Ikon banza na shi akai

A ci rashwa hanci ci akai

Manyan nan su nay yad da kai

Fadar kowa yau shi akai

 Yi da gaske ɗumi bari dariya

 

35.Wac ce a yi mulki ba matsi

Iko na ko ko yamutsi

A gama da wuta ta yi tartsatsi

Ta game tawaye da tabbatsi

 Su lafa cilas su bi gaskiya

 

Cewa mulkin ga ka san na kai

Ba mulki na ba da za shi kai

Ga bukata kowa ba shi kai

In babu biyayya sariƙai

 Ka zama manya Najeriya

 

A yi sata bayyane an gani

An kam mai mai abu na gani

A hana mai ba shi da magani

Ko ya tafi ya yi ta gunguni

 Bai bai mai sata ya ƙiya

 

Amma gyara cilas akai

Ba don bisa son ran fasiƙai

In an ƙi a yo haka an sakai

In an bi bukatar sariƙai

 Wannan mulkin bai moriya

 

An ɗauki ƙaho an ƙarfafa

Ya gina gida ya kallafa

Ji haya shika yi ya yo ƙafa

Kangonai har yaƙ ƙarfafa

 A biɗe shi a binciki gaskiya

 

 40.Mai ɓaɓatu azzalumi

Doka ta yi mai takunkumi

Shaiɗanin nan algungumi

A rufe shi a bar shi shi sha gumi

 Shi bi dokokin Najeriya

 

Wannan waƙa da ire-irenta sun dace ainun da a riƙa amfani da su a kafafen labarai maimakon waƙe-ƙaƙe da raye-rayen Turawa da ake cika kunnuwan matasa da su dare da rana.

3.3 Sanya Baitocin Waƙa Kan Allunan Sanarwa

Lokacin da marubucin wannan muƙala yana ɗan makarantar sakandare ya sha karanta wata takardar yekuwa a titunan Sakkwato da na Birnin Kabi inda yake makarantar. Saƙon da wannan takardar yekuwa take isarwa shi ne, “a daina shan ƙwaya mai firgitarwa. A kan takardar sai aka yi zanen wani matashi mai yamutsattsen gashi a kansa, idanunsa turu-turu kuma jajir, ga shi kuma sanye da tsumma. Sai aka koma gefen wannan matashi aka rubuta ɓaro ɓaro:

ƊAN ƘWAYA GA ƘARSHENKA ! !

Wannan yekuwa ta yi tasiri ainun kan mai wannan muƙala domin ta hana shi shiga gungun 'yan makaranta mashaya ƙwaya!!!

Akwai tarin waƙoƙin da ke faɗakarwa irin wannan takardar yekuwa. Za a samu nasara mai girma idan Hukumar Labarai da Aladu ta tanadi waɗannan waƙoƙi, ta yi amfani da baitocisu ta rubuta takardun yekuwa ta kuma lilliƙa su ga allunan sanarwa cikin garuruwa. Dubi wannan misali:

25. Can a cikin gari ka gina masallaci daidai,

 Kuma bayan gari ka yo hotel, to kai ko dai,

 Ai hanya guda mutum shika bi, shi ad daidai,

 Ba shi zamo muzabzabi ba shi ce ya yo daidai,

 Wanga irin dagwalgwale ni kam ban gane ba.

 

 26. Namiji da macce na rawa haɗe shin, ko culture na?

 Tambayi Baba Soja mai culture ko mina na?

 Mu kam dai ga namu addini shi halɗi na,

 Halɗi ko ga namu addini ya zam ɓarna,

 Kuma Baba Soja ya yi kurum bai tanka ba.

 

27. Sai dai na ga Baba Soja shina son amsa min,

Harkaz zamani shina da saninta shi koya min,

Ni ban gane inda ake ba sai ya nuna min,

 Amma Baba Soja am bari dus son gyara min,

 Gyaran dud da kai yi don banjo ban amsa ba.

(Alhaji (Dr.) Umaru Nasarawa Wazirin Gwandu:Gargaɗi Ga Matasa)

 Ba lalle ne a rubuta dukan baitocin kan takardar yekuwa ɗaya ba. Hukumar Labarai da Aladu ita ce ta fi sanin yadda za ta yaɗa su, amma fa tare da shawarar manazarta waƙoƙi. Ga wani misali:

10. Don Allah Mallama am ji jawabina

Daɗa ko ki so shi ko ki ga aibi na

In na faɗe shi na san haƙƙan na

Ilminki babu amre shibci na

 

 11. Ilminki babu amre sharri na

Sheɗan ka ɗunguza ki cikin ɓanna

Ki yo ta ba ki dubin aibi na

Kullun faɗin kikai injoyin na

 

 12. Sai radda kig ga ke rasa mai son ki

Duw wanda kin nuhwa bai dubin ki

Mai son ki dauri ya bar shawak ki

Sannan ki sa kiran yo ni kaina

 (Sambo Waliyyi Giɗaɗawa: Waƙar To Da Ke Nike)

3.4 Rubuta Da Rera Baitocin Waƙa Cikin Azuzuwa Da Allunan Sanarwa

Makaranta ita ce mai gina tarbiyya ta biyu bayan iyaye. Dalili ke nan da ya sa ba a wofintar da ita ba a duk tsawon zamani, tun daga lokacin jihadi har zuwa yau. Yadda za a iya inganta wannan hanya ita ce a ƙarfafa rubuta da rera waƙa ko baitocinta cikin azuzuwa da allunan sanarwa na makaranta. Malamai musamman na fannin ilmi su suka kamata su ba da shawara kan ina ne za a yi amfani da wane irin salo. A ganin wannan muƙala a ƙananan makarantu ya fi dacewa a rubuta a kuma rera waƙoƙin. Za a lilliƙa takardu masu baitocin waƙa a bangunan cikin aji. Haka kuma zai dace a riƙa rera baitocin ko ma dukan waƙoƙin cikin aji tare da yara a duk lokacin da aka ga ya dace. Dabarar Alhaji Shehu Shagari wadda ya kwaikwayi malaminsa babbar dabara ce a nan. Yakan rubuta baitoci domin yin bita da ƙarfafa darussan da ya karantar da yaransa. Ya shiga aji ya rera tare da su.[i] Haka kuma zai dace idan malamai suka riƙa rera wa ɗalibansu ire-iren waɗannan waƙoƙi. Waƙar GargaɗI Ga Yan Makaranta ta Wazirin Gwandu ta dace ainun ga ‘yan makarantun furamare. Ga kaɗan daga baitocin wannan waƙa:

4. Ku 'yan uwana duk ku zo,

 Ku ji gargaɗi in na faɗai.

 

 

 5. Zancen ga ba ni naf faɗe-

 shi ba, Mallamina yaf faɗai.

 

 6. Almajirai muke ni da ku,

 Gun malami muke tun daɗai.

 

 7. Malam ka yo mana gargaɗi,

 Mu tsaya mu ji shi mu ko riƙai.

 

 8. Ahnajiri ɗan malami,

 Don shi ka renonai daɗai.

 

 9. Ya ce ɗiyana duk ku zo,

 1n ba ku jalli kwat tsarai.

 

 10. Shi zai ci riba duk da riba

 Arziki sai an faɗai.

 

 11. Ba dukiya zan ba ku ba,

 Jallin da baki zan faɗai.

 

 12. Wada naf fi so ku taho ku ji,

 Ku tsare da kyau in na faɗai.

 

 13. Kowat tsare shi shi tabbata,

 Babban rabo na nan garai.

 

 14. Wada anka so almajiri,

 A ishe hali mai kyau garai.

 

 15. Duka lokacin sallah shina-

 Tsare, duk da tasbi ag garai.

 

 16. Mai hankali mai girmamawa,

 Har a san ladabi garai.

 

 17. Shi fake amanam malami,

 Shi tsare umurninai garai.

 

 18. Na gabansa ko ba malami-

 Ba, shi zan tsaron girma garai.

 

 19. Tsararsa duk shi fake mutum­-

 cin nasu har irli, tsarai.

 

 20. A ishe shi ba shi da twakara,

 Kuma hanƙurewa ag garai.

 

 21. Da cikin aji da cikin gari, ­

 A ishe haIin girma garai.

 

 22. Kyawon hali shi am mutum,

 Sannan a so ilmi garai.

 

 23. A cikin aji in an shiga,

 A ishe akwai himma garai.

 

Bayan da Wazirin Gwandu ya bayyana yadda ya kamata ɗan makaranta nagari ya kasance, sai kuma ya kawo halayen ɗan makaranta mara halaye nagari. Ga kaɗan daga ciki:

 36. Ibi1isu na shaiɗanu na,

An gane taurin kai garai.

 

 37. Mutakabbiri na, makiri,

An gane girman kai garai.

 38. Ga fakon amana shi da ɓe-­

 ra ɗai, yawan ɓarna garai.

 

 39. Ko an yi foro ba shi ji,

Halin batsalci ag garai.

 

 40. Babba da yaro ɗai garai,

 Duk babu mai girma garai.

 41. Tsararsa bai da tagomashi,

A cikinsu don fitina garai.

 

 42. Ga twakara da yawan faɗa,

 Haka nan yawan ƙara garai.

 

 43. Tcintce gare shi da tsegumi,

 Haka nan yawan ƙarya garai.

 

 44. Ko ya fadi, mu ba mu amsa,

Tun da kissoshi garai.

 

 45. Da cikin aji da cikin gari,

Kowa shi nemi tsari garai.

 

 46. Mugun hali ɓarnar mutum,

Ko da akwai ilmi garai.

 

 47. Balle daƙiƙi na balidi,

Babu amfani garai.

 

 

 48. A cikin aji in an shiga,

Abada yawan barci garai.

 

 49. Ai gwamma kwananai, zama,

 Falken yawan yaya garai.

 

 50. Fashi shi kai bai zakkuwa,

Bisa lokaci makara garai.

 51. Da fita aji ya garzaya,

Wajjemmu ba matsaya garai.

 

 52. In son ganin samnan kakai,

Tafi can tashar mota tarai.[i]

Ya kamata a ƙarfafa nazarin ire-iren waɗannan waƙoƙi da suka ƙunshi saƙonnin tarbiyya cikin manyan makarantunmu.. Baya ga haka zai dace a riƙa kakkafa allunan sanarwa a wurare daban daban cikin makaranta. Waɗannan allunan sanarwa za su kasance ɗauke da baitocin da ke ƙunshe da saƙonnin tarbiyya. Ga misalin irin waɗannan baitoci:

28. Jami’a ban barin ta sai na taɓe ta

Don sanin martabam mazauna cikinta

Masu ilmi da hankali ag gare ta

Bincikawa da gaskiya sai ɗiyanta

 Hece tarke sukai da ƙaiƙai ga tsaba

 

29. Na ji kumyag ganin kaɗan za su ɓata

Martabaj jami’a da hallan zamanta

Sheɗanad dud da za ta taso gwaninta

Jami’a yaf fito sani ya mugunta

 Bai da rana gare mu in ban da ruba

 (Alhaji Garba Gwandu: Gaskiya, Bulaliya Ta Biyu)

Waɗannan baitoci misali ne na ire-iren baitocin da suka dace a kafa allon da ke ɗauke da su a kan hanyar malamai ta zuwa azuzuwan makaranta da wuraren tarukansu, kamar majalisar jamia. Ga wani misali:

13. Akwai wasu malammai na tauye maki[i]

 Ga ɗalibbansu ko da sun yi kirki

 Su ja wani can su isammai da aiki

 Amana kun ga tun nan ta yi miki

 A iske malami na ƙuntatawa

 

 14.Sanina mallami matsayin uba na

Ga su ko ɗalibai manyan ɗiya na

Su duka nashi na haka za mu zamna

Malam sad da ya ƙi tsaron amana

 Sani yaka wa jafa’i bai tunawa

 

15. Abin da ka girgiza ni ga lokacinmu

Ga malammai masoya shiryuwarmu

Amana ta ƙaranta bale gare mu

Abin ga wane wuri na za shi kai mu

 Ganin ulama’u sun shiga barkacewa

(Alhaji Garba Gwandu:Amana Hanyar Shiriya)

 

3.5 Ƙarfafa Gasar Rubuta Waƙoƙi Kan Tarbiyya

Daga cikin hanyoyin da suka shigo na amfani da waƙa don bunƙasa ta da kuma shirye-shiryen hukuma, akwai shirya gasar waƙoƙi a inda kuma manazarta waƙoƙi kan gabatar da muƙaloli don tattaunawa. Waƙoƙin da irin wannan shiri kan haifar suna da matuƙar amfani saboda ingacinsu da kasancewarsu wata hanya da ke buɗe ido ba ga alumma ba kurum, har ma da su mawaƙan kansu. Ta nan ne za su goge ga shirya waƙa. Ta nan ne za a samu waƙoƙi masu nagartattun jigogi, ciki har da na tarbiyya. Ya kamata Hukumar Labarai da Aladu ta ƙarfafa wannan hanya. Ta wannan hanya gwamnati za ta iya samar da waƙoƙin da ke cusa tarbiyya ga al’umma. Haka kuma hukuma na iya kwaɗaita ma jamaa yin amfani da shafukan sada zumunta na yanar gizo don yaɗa baitoci masu amfani.

A ƙarshe, mai karatu na iya cewa muƙalar nan ta yi kira ga Hukumar Labarai da Aladu, alhali kuwa Gwamnatin Tarayya take da wannan hukuma kuma tilas ta rungumi dukan ƙabilun Nijeriya. Wannan batu haka yake, kuma ba lalle ne wasu ƙabilun Nijeriya su kasance suna da rubutattun waƙoƙi ba, sai dai na baka. A wannan fuska, matsalar mai sauƙi ce. Hukumar Labarai da Aladu da makamantanta na jihohin, da ma sauran hukumomi kamar makarantu, na iya amfani da waƙoƙin baka don yin yaƙi da rashin tarbiyya da karɓar rashawa. Hikimomin da ke cikin rubutattun waƙoƙi akwai su cikin na baka domin da waƙar baka da rubutatta duk sunansu waƙa kuma bori guda suke yi wa tsafi. Dukansu da ire-iren salo ɗaya suke isar da saƙonninsu ga jamaa, salo kuwa shi ne asirin waƙa.

KAMMALAWA

Wannan muƙala ta yi ƙoƙarin bayyana yadda aka sha yin yaƙi da rashin tarbiyya a ƙasar Hausa ta yin amfani da rundunar rubutattun waƙoƙin Hausa. An fara kai farmaki da wannan runduna aƙalla tun a ƙarni na 17, kuma tun daga lokacin rundunar ba ta karaya ba. Dubarorin da kuwa ta yi amfani da su sun haɗa da almajirai da ke nazarin waƙoƙin, da rera su a masallatai da fadar sarakuna, da cikin gidajen ma’aurata da kuma kafa ƙungiyoyin yan taru. Amfani da waƙoƙin ya ci gaba musamman ta fuskar miƙa su ga almajirai, su kuwa su rera wa jamaa ko a ƙofofin gidaje ko kuma a masallatai. Haka kuma akan rera waƙoƙin a tarukan siyasa kamar yadda muka ga su Sa’adu Zungur da Mu’azu Haɗeja da Aƙilu Aliyu suka fara yi, har zuwa rera su a gidajen watsa labarai kamar rediyo da talibijin da shafukan zumunta na yanar gizo da naɗiyarsu cikin kases-kases ko faifan konfuta.

MANAZARTA

 

1. Abdulƙadir, Ɗ. (1979), Zaɓaɓɓun Waƙoƙin Da Da Na Yanzu, Lagos: Nijeriya.

2. Adamu, S. A.S. (babu kwanan wata da maɗabaa), Bassu al- Aɗaai: Sharh Ƙurɗabi, Dutse: Jigawa, Nijeriya.

3.                  Ahmad, A. S. (1983), ‘Rayuwar Marigayi Abubakar Maikaturu Alƙanci Sakkwato Da Waƙoƙinsa, kundin digiri na farko, Sokoto: Jamiar Sakkwato.

4.                  Ainu, H. A. (1984), ‘Malam Ibrahim Khalilu Marina Tsamiya Sakkwato Da Waƙoƙinsa, kundin digiri na farko, Sakkwato: Jamiar Sakkwato.

5. Aliyu, A.A, (2007), Fasaha Aƙiliyya, Zariya: NNPC.

6. Al-Qurtubi, Y.I.Y.A.Y. (r. 303H.), Manzuumat al- Qurtubiyy fi al- Ibaadaat ala Mazhab al- Imaam Maalik, Sokoto: babu sunan maɗabaa da shekarar bugawa, amma wanda ya ɗauki nauyin sake bugun shi ne, Alhaji Muhammadu Mahi ɗan Malammai Kanwuri Sakkwato.

7.                  Boyd, J. (2000), The Caliph’s Sister: Nana Asma’u 1793-1865- Teacher, Poet and Islamic Leader, London: Newbury House, 900 Eastern Avenue.

8.                  Bunza, A.M. (2002), Yaƙi Da Rashin Tarbiyya, Lalaci, Cin Hanci Da Karɓar Rashawa, Lagos: Ibrash Islamic Publications LTD.

9. Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya (2006), Ƙamusun Hausa, Kano: Jami’ar Bayero.

10. Ɗangambo, A. (2007), Ɗaurayar Gadon Feɗe Waƙa, Zariya: amana publishers ltd.

11.              Department of Nigerian Languages (2013), Zauren Waƙa: Journal of Hausa Poetry Studies vol.1No 2, Zariya: Ahmadu Bello University Press.

12.              Department of Nigerian Languages, ƊUNƊAYE: Journal of Hausa Studies vols. 1-5, Sokoto: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

13.              Department of Nigerian Languages ALGAITA: Journal of Current Research in Hausa Studies vol. 1 No 1-4, Kano: Jami’ar Bayero.

14.              Department of Nigerian Languages (2013), Zauren Waƙa: Journal of Hausa Poetry Studies vol. 1, Sokoto: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

15.              FAIS Journal of Humanities vol. 3/I (2004), Kano: Jami’ar Bayero.

16. Giɗaɗawa, A.M.B. (2006), Bargon Hikima, Sokoto: Cibiyar Nazarin Hausa, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

17. Haɗeja, M. (180), Waƙoƙin Muazu Haɗeja, Zariya: NNPC.

18.              Junaidu, S. (1990), ‘Resistance to Western Culture in the Sakkwato Caliphate: a Lesson to Generations Yet Unborn’ cikin A.M. Kani da K.A. Gandi (editoci), State and Society in the Sokoto Calphate (1990), Sokoto: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

19. Kani, A.M. da Gandi, K.A. (editocin, 1990), State and Society in the Sokoto Calphate, Sokoto: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

20.              Muhammad, Ɗ (edita) (1990), Hausa Metalanguage, Ibadan: University Press Limited.

21.              Omar, Dr.S. (2014), ‘Yantarun Nana Asma’u Ɗanfodiyo: Tsarinsu da Taskace Waƙoƙinsu, Lagos:Zeetma Investment Limited.

22.              Omar, S (2013), Fasahar Mazan Jiya: Nazari a kan Rayuwa da Waƙoƙin Malam Muazu Haɗeja, Kaduna: Garkuwa Media Services LTD.

23. Sa’id, B (1978), ‘Gudunmawar Waƙoƙin Masu Jihadi, kundin digiri na biyu, Kano: Jamiar Bayero.

24. Shagari, A.S. (1978), Waƙar Nijeriya, Zariya: NNPC.

25.              Sokoto, I.J. (2007), Tsarabar Waziri Buhari da Waziri Junaidu ga Manazartan Waƙoƙin Hausa, Sokoto: Al-Amin Printing LTD.

26. Talata Mafara, M. I. (1999), Daular Usmaniyya 1-3, Abakwa, Kaduna: Nadabo Print Production.

27. Usman, B. B. (2006), ‘Hikimar Magabata:Nazarin Ƙwaƙƙwafi a kan Rayuwar Malam (Dr.) Umaru NasarawaWazirin Gwandu (1916-2000) da Waƙoƙinsa, digiri na uku, Sakkwato: Jamiar Usmanu Ɗanfodiyo.

28.              Yahaya, I.Y. (1988), Hausa A Rubuce:Tarihin Rubuce-Rubuce Cikin Hausa, Zariya:NNPC.

29.              Yahya, A.B. (1986), “Tattalin Zaɓen Rubutattun Waƙoƙin Hausa Domin Yara, hukumar Nigerian Book Development Council ta shirya a Kaduna, an buga cikin FAIS Journal of Humanities vol. 3/I (2004), Kano: Jami’ar Bayero.

30.              Yahya, A. B. (1990), ‘The Significance of the 19th Century Poetry Teachingss’ cikin, A.M. Kani da K.A. Gandi (editoci), State and Society in the Sokoto Calphate, Sokoto: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

31.              Yahya, A.B. (1997), Jigon Nazarin Waƙa, Kaduna: FISBAS Media Services.

 32. Yahya, A.B (2001)“Dangantakar Waƙa Da Tarbiyyar Yayan Hausawa cikin Harsunan Nijeriya xix, Centre for The Study of Nigerian Languages, Bayero University, Kano, p.94-109, Kano.

33.              Yahya, A.B. (2001), Salo Asirin Waƙa, Kaduna: FISBAS Media Services.

34. Yahya A.B. da Ainu, H.A. da Idris, Y. (editoci) (2015), SAI ALU:Sharhi Kan Waƙoƙin Da Aka Yi Wa (Dr.) Aliyu Magatakarda Wamakko, Zariya:ABU Press.

35.              Yakubu, A.M. (1999), Sa’adu Zungur: An Anthology of the Social and Political Writings of a Nigerian Nationalist, Kaduna: Nigerian Defence Academy Press.

36. Zungur, S. (1968), Waƙoƙin Saadu Zungur, Zariya: NNPC.

Post a Comment

0 Comments