𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum malam fatan an wayi gari lafiya, ya
akaji da jama'a? Allah ya taimaka.
Malam don Allah a taimaka amin Ƙarin haske game da lamarin nan. Nice nasha azumin Ramadan na shekara biyu ma'ana na farko nasha guda tara sanadin juna biyu da nake dauke da shi lokacin na kusa haihuwa sai yake bani wahala shi ne nasha guda tara da niyyar idan Allah ya saukeni lfy sai na biya. To bayan na haihu sai Allah ya jarrabeni da wata irin jinya mai wahala nakai tsawon lokaci a cikin wannan hali to Malam har wata ramadan din ta dawo ban iya biya ba. A cikin azumin bara sai abun ya ƙara tabani sosai ban samu na yi azumi ko daya ba, to har zuwa yanzu Malam lafiyar dai sai a hankali ce. shi ne nake so amin cikakken bayani game da wadannan azumi da suke kaina ta yaya zan biyasu?
𝐀𝐌𝐒𝐀👇
Wa alaikis salam wa rahmatullahi wa barakatuh.
Da farko ina fatan Allah shi baki lafiya, ya sa kaffarah
gareki cikin jinyar da ke damunki.
1. Akwai saɓanin malamai game da
hukuncin matar da tasha azumi sanadiyyar goyon ciki. Amma saboda larurar da
kike ciki sai ki dauki fatawar Sayyiduna Abdullahi bn Abbas (Allah ya yarda
dashi) shi awajensa idan mace mai jun biyu tasha azumi, za ta ciyar da miskini
guda ne bisa kowanne azumin da tasha. Don haka za ki ciyar da miskinai tara ke
nan.
2. Azumin da aka sha ta dalilin zafin jinya, babu
makawa sai an ramashi da zarar an samu lafiya. Sai dai idan likitoci masanan
jinyar sun duba sun tabbatar da cewa majinyacin ba zai warke ba (wato ba a tsammanin
warkewarsa) to shi ke nan wajibcin yin ramukon ya sauka daga kansa. Sai a ciyar
da miskini maimakon kowanne wuni guda da aka sha.
Don haka za ki jira duk lokacin da Allah ya baki
lafiya sai ki rama. Idan kuma likitocinki sun tabbatar miki da cewa ba sa tsammanin
warkewar jinyar, to ciyar da miskini za ki yi bisa kowanne azumi guda. Wato
miskinai talatin ke nan.
WALLAHU A'ALAM.
Ku Kasance Da mu Cikin Wannan Group Domin Ilimantarwa
Tare Da Faɗakarwa a Sunnah.
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/GhLY39kRlZEIdcZUmGchEm
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.