𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum. Allah ya Kara ma malam ililmi da basira. Ana bi na azumi(20) sabida ban Sami daman ramawa sabida ciwo Kuma bana iya ciyarwa sabida iyayena ba suda Hali. Mm ya zan yi yanzu?
𝐀𝐌𝐒𝐀👇
Wa alaikumus salam wa rahmatullahi wa barakatuh.
Alhamdu lillahi rabbil alamin wassalatu wassalamu ala rasulillah wa ala alihi
wa sahbihi ajma'in.
Bawan Allah wace amsa kake so a baka? Ka zo da zantuka
da ke nuni zuwa ga amsar da kake so a baka, ka karanta mani ita a baki ne kaɗai ya rage baka yi ba.
Kafin na baka amsa ga tambaya, kana nufin watanni goma
sha ɗaya da suka wuce, dukan su, kana kwance baka lafiya ne?
Na biyu: wa ya ce da kai, maras lafiya zai ciyar ne?
Bayan haka waye ya baka fatawar iyayen ka ne za su ɗauki nauyin ciyarwar da ke kan
ka, ballantana ka fara gabatar da uzurin talaucin su.
Kana nufin yanzu haka maganar da muke, kwance kake
baka da lafiya?
Ƙa'ida ita ce, duk maras
lafiya, Allah ya ɗauke mashi azumi, har sai lokacin da ya warke. Idan
kuma har ya mutu bai warke ba, babu laifi a kan sa, kamar yadda babu ramako a
kan shi ko a kan waliyyan sa.
Don haka za ka zauna har zuwa lokacin da Allah ya baka
lafiya, sannan ka rama azumi ashirin da ka sha a sanadiyyar waccan rashin
lafiyar, wannan shi ne a kan ka.
Allah ya ce da maras lafiya da matafiyi, su rama azumi
bayan ya warke daga ciwon shi, matafiyi kuma a lokacin da ya dawo gida
(.. وَمَن كَانَ مَرِیضًا أَوۡ عَلَىٰ سَفَرࣲ فَعِدَّةࣱ مِّنۡ أَیَّامٍ أُخَرَۗ یُرِیدُ ٱللَّهُ بِكُمُ ٱلۡیُسۡرَ وَلَا یُرِیدُ بِكُمُ ٱلۡعُسۡرَ..... )
[Surah Al-Baƙarah 185]
Wallahu ta'aala a'lam.
Amsawa:
Malam Aliyu
Abubakar Masanawa
Ku Kasance Da mu Cikin Wannan Group Domin Ilimantarwa
Tare Da Faɗakarwa a Sunnah.
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/GhLY39kRlZEIdcZUmGchEm
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.