Ticker

6/recent/ticker-posts

Neman Afuwa Saboda Ramadan

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Mene ne hukuncin yaɗa irin wannan saƙonnin???

👇🏼👇🏼👇🏼👇🏼👇🏼

SALAMU ALAIKUM

Yana daga sunna Na ma'aiki kanemi gafarar kowa kafin shigar watan RAMADAN, dan Allah idan nataba bata maka/miki asane ko arashin sani, ina neman Yafiyarka/ki,  ki/ka yafemin

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Toh wannan akwai nau'ine na ganganci babu shakka acikinsa. Domin nidai ban taɓa jin inda akace Annabi Muhammad (s.a.w) ko sahabbansa suna neman afuwar junaba saboda kusantowar ramadana kokuma saboda shigowarsa. Toh amma ita wannan tace wai sunnar Annabinema mutum yanemi afuwar mutane toh kaga wannan inhar babu jahilci acikin lamarin toh akwai ganganci domin kuwa a ƙa'ida baka kiran abu sunnah se wanda ya tabbata. Idan abu ya tabbata cewa tabbas Annabi (s.a.w) yafaɗa kokuma ya aikata toh shine se ace sunnah amma idan akwai shakku akwai ko be ingantaba toh sedai acemai hadisi amma badai ace sunnah ba.

Toh amma ita wannan kaga saboda ganganci da taƙama kai tsayema tace wai yin hakan sunnah ne. Amma ƙila batada labarin cewa Annabi (s.a.w) yace duk wanda ya yi masa ƙarya da gangan toh ya tanadi wajanda ze zauna a wutar jahannama. A wata ruwayar kuma yace duk wanda yace nafaɗi abu alhali kuma ban faɗa ba toh haƙiƙa ya girmma ƙarya ga Allah seya tattali wajanda ze zauna a wuta. Toh kaduba irin wannan bala'i da Annabi ya ajjiye akan wanda ya yi masa ƙarya toh tayaya zakizo kina yiwa Annabi ƙarya da sunan kina neman afuwar mutane? Shin wacce riba zakici idan mutanen suka yafe miki Annabi kuma shi da kikaiwa ƙarya be yafe mikiba??? Na'am babu shakka neman afuwa abune mekyau amma ware wani lokaci ace se a wannan lokacin shine za'a nemi yafiya toh wannan kodai bakacema abun bidi'a ba toh be kamataba acemai sunnah domin sunnah tanada ƙa'idoji awajan malamanta.

Allah Ya sa mu dace

Ku Kasance Damu Cikin Wannan Group Domin Ilimantarwa Tare Da Fadakarwa a Sunnah.

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/BJikpGm7VXV1vEVVGcNH5J

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

Post a Comment

0 Comments