Ticker

6/recent/ticker-posts

Mu San Hukunce-Hukuncen Fiƙhu [20] - Bambancin Maniyyi, Maziyyi, da Wadiyyi

Maziyyi shi wani ruwa ne fari, bashi da kauri kuma yana da danƙo/yauƙi, yana fita ya yin da mace da namiji suka gabatar da wasa, ko kuma tunanin jima'i, ko kallon batsa ko karanta wani rubutu na batsa.

 Sannan ba a jin mutuwar jiki bayan fitarsa, wani lokacin ma ba a sanin lokacin da yake fita.

Manzon ALLAH {s.a.w} ya ce:Da Aliyyu ɗan Abu Ɗalib (R.A) lokacin da ya yi masa tambaya game da Maziyyi, ya ce masa: Ka wanke gabanka, ka sake alwala

[Bukhari da Muslim].

WADIYYI: Shi wani ruwa ne fari kamar farau-farau, mai kauri, yana fita bayan fitsari.

Amma mafi akasarin dalilin fitowarsa ciwo ne, sanyi ne yake kawo shi, shi ma yana ɗaukar hukuncin tsarkin fitsari.

MANIYYI: Wani ruwa ne fari, mai kauri, yana fitowa tare da sha'awa, yana tunkuɗar juna, ana samun mutuwar jiki bayan fitarsa, yana wari irin warin bara-gurbin ƙwai.

Sannan kuma maniyyi mai tsarki ne, domin da najasa ne da Manzon ALLAH {s.a.w} ya yi umarni a wanke shi.

Ana wanke shi idan yana ɗanye, idan ya bushe kuma, to kawai sai a kankare shi.

Saboda hadisin Nana A'isha (R.A) ta ce:

Manzon ALLAH {s.a.w} ya kasance yana wanke maniyyi, sannan ya fita zuwa sallah da wannan tufar, ina ganin gurbin wurin da ya wanke.

[Bukhari da Muslim].

A ruwayar Muslim kuwa cewa tayi: Na ganni ina kankare shi maniyyin daga tufar Manzon ALLAH {s.a.w} sannna ya yi sallah da wannan tufar.

[(Bukhari da Muslim].

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments