𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Salamun alaikum, Dr. Tambaya ce aka jefa mani ina gabatar da darasi wa mata a garin Firji: mace ce mijinta bai yarda ya ɗauki azumi ba sai ya ga wata da kansa (bai yarda da sanarwar Sarkin Musulmi ba), to inda mushkilar take shi ne, ita matarsa ta yarda da sanarwar Sarkin Musulmi amma sai ya ce kada ta kuskura ta dauki azumin, to shin minene matsayinta? Domin ta ajiye azumin saboda tsoron kada ya wulaƙanta ta.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikum assalam A Zahiri ba za ta masa biyayya a
nan ba, Tun da Azumi rukuni ne daga cikin ginshikan musulunci.
Annabi SAW yana cewa:
إنما الطاعة في المعروف
Ana yiwa jagora biyayya ne idan ya yi umarni da abin
da ya dace da sharia"
Sannan yana cewa: "Ana yin azumi ne ranar da
mutane suke yin azumi"
Allah ne mafi sani
Amsawa✍🏻
DR. JAMILU YUSUF ZAREWA
Ku Kasance Damu Cikin Wannan Group Domin Ilimantarwa
Tare Da Fadakarwa a Sunnah.
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/FmJ5Ojsns1KFolTP8ƙu9GT
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.