𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Mene ne ingancin hadisin: “Duk wanda ya sanar da mutane watan ramadan, za a haramta masa shiga wuta”?
𝐀𝐌𝐒𝐀👇
Dukkan Godiya ta tabbata ga Allah.
Hadisin da ake jingina shi ga Annabi, tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi wai cewa "Duk wanda ya sanar da mutane game da
watan Ramadana to ba zai shiga wuta ba" wannan hadisin ba ya cikin
litattafan Sunnah kaf!!
Kuma babu wani ɗaya daga cikin malamai da ya
yi rubuce-rubuce a kan falalar watan Ramadan da har ma ya gargaɗi mutane a kan zuwan
ramadan, kamar yadda babu wanda ya ambace shi a cikin ko da hadisai raunana ko
cikin wanda aka ƙago. Don haka bai inganta
ba!
Imam Al-Suyuti
ya ce a cikin “Tadrib Rawi” (1/327):
Ibnul Jawzi ya
ce: “Ya yin fadin wanda ya ce: “Idan kuka ga hadisin da ya saɓa wa hankali, ko ya saɓa wa abin da aka (saba)
ruwaitowa, ko ya saɓa wa ƙa’ida, to ku sani ƙagaggen hadisi ne.
Sai ya ce: Abin
da ake nufi da saɓa wa ƙa’ida shi ne kasancewar
hadisi ya kasance a wajen Musulunci daga sanannun isnadi da littafai.” 👌
Don haka bai
halatta a tura ko yaɗa wannan hadisin ba sai dai don manufar a gargadi
mutane akansa cewa karya ne yana da illa bai inganta ba. Domin faɗin Manzon Allah tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi cewa "Karya a kaina ba ta zama kamar
yi wa kowa karya ba, duk wanda ya yi min karya da gangan, to ya nemi wurin
zamansa a cikin Jahannama" Bukhari (1229) ya ruwaito. Muslim ma ya ruwaito
shi a cikin gabatarwar littafin sa (3).
Haka a cikin hadisin Ibn Abbas a cikin Tirmizi: “Ku kiya
yi magana daga gare ni sai dai abin da kuka sani, don haka wanda ya yi min
karya da gangan, to ya nemi wurinsa a cikin Wuta." Allah ya tsare mu
A rubututtuka
na, a baya na yi bayani kan falalar watan Ramadan, da azumi a cikinsa da tsayuwa
a cikinsa da sauran manyan ibadu masu lada a cikinsa, za a iya dubawa shafukan
mu don gani.
Allah ya sani.
✍️Abou Khadeejatu Assalafeey
Ku Kasance Da mu Cikin Wannan Group Domin Ilimantarwa
Tare Da Faɗakarwa a Sunnah.
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/GEahmrOpR4pA5TmW0ZW0cU
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.