𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Mene ne Hukuncin Ɗaukar Mace Aikin Soja?
𝐀𝐌𝐒𝐀👇
Ba ya halatta ɗaukar mace aikin soja, domin mace ba ta cikin masu (ɗaukar makami su yi) jihadi." "Wannan dai kallafa mata wani aiki ne wanda ba ta iyawa, sannan kuma bijiro da ita ne zuwa ga wata fitnah da kuma sharri." " Sannan kuma kamar ana so a fitar da ita ne daga matsayin ta na ɗiya mace ne; da kuma dora mata aikin da maza suka keɓanta da shi ne, wannan kuwa baya halatta." " Wannan aikin kafirai ne, amma ba aikin musulmi ba ne, domin su musulmi basu sanya mata aikin soja." " Waɗanda dai kawai suke irin wannan aikin su ne kafirai, ko kuma wasu kasashen Larabawa waɗanda suke kwaikwayon kasashen kafirai daga cikin (kasashen Larabawa) Yan Gurguzu ( Socialists), da kuma kasashen Larabawa wadanda Jam'íyyar Ba'ath ke mulkarsu, da dai sauran su."
ABUBUWAN LURA a nan:
Duk a cikin tarihin musulunci, babu inda aka nuna cewa
mata suna shiga aikin soja, tare da cewa suna fita zuwa jihadi tare da sauran
sojojin musulunci,
amma ba don su yi aikin soja ɗin ba. A'a suna dai bada
gudummuwa ne a wajen bada taimakon gaugawa kamar jiyar waɗanda suka samu raunuka da
sauran ayyukan jin kai idan akwai bukatar haka ɗin . Shi aikin soja, aiki ne
wanda a Sharí'ah ta musulunci ya keɓanta ne kawai ga maza, amma ban
da 'ya'ya mata. Ɗaukar mata aikin soja Saɓawa dokar Allah ne , domin
Allah Subhanahu wa Ta'ala Ya hana buɗe duk wata kafa da za ta kawo
cakudar maza da mata , wadda kuma za ta iya haifar da fitnah mai girma kamar
irin wannan aikin soja ga mata. Duk mutumin da ya goya wa ɗiyarsa baya ta shiga aikin
soja, ko kuma ya nema mata conscription (damar a ɗauke ta aikin soja) , to
babu ko shakka ya saɓawa umarnin Allah da Manzon Sa ﷺ Baya halatta musulmi su yi koyi
da kafirai a irin waɗannan wuraren , domin ko shakka babu sai sun haddasa
fitintinu na saɓon Allah waɗanda ba za su iya lisaftuwa
ba. Shi daukar mace aikin soja , ba komi ba ne ba face cin mutuncin ɗiya mace.
WALLAHU A'ALAM
Ku Kasance Da mu Cikin Wannan Group Domin Ilimantarwa
Tare Da Faɗakarwa a Sunnah.
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/GcU1I5wjOB18K4PA6eURƘƘ
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.