𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum malamina ina da tambaya, mace ce ba ta da lafiya, ciwon ko da ya fara tsananta gare ta, sai satinnan likitoci suka ba ta shawara duk bayan minti talatin ta ci wani abu daga Abinci amma kar ta ƙoshi, to malam yaya za a billowa maganar Azumin da ta sha, ciyarwa za a cigaba da yi ko jira za a yi sai ta warke ta rama?
𝐀𝐌𝐒𝐀👇
Wa alaikum
assalam, in har tana tunanin samun sauƙi kafin wani azumin ya zo,
ba za ta ciyar ba, za ta bari ta rama bayan ta samu dama, saboda aya ta: 184 a
suratul Baƙara ta nuna cewa: wajibin
mara lafiya shi ne rama azumin da bai yi ba na Ramadan bayan ya samu dama a
wasu kwanakin.
Matukar likitoci sun tabbatar ba za ta samu sauƙin da za ta rama azumi daga baya ba, ya halatta ta ciyar a
maimakon kowacce rana.
Allah ne mafi sani.
Wa alaikum assalam, in har tana
tunanin samun sauqi kafin wani azumin ya zo, ba za ta ciyar ba, za ta bari ta
rama bayan ta samu dama, saboda aya ta: 184 a suratul Baqara ta nuna cewa:
wajibin mara lafiya shi ne rama azumin da bai yi ba na Ramadan bayan ya samu
dama a wasu kwanakin.
أَيَّامًا مَّعْدُودَاتٍ فَمَن كَانَ مِنكُم مَّرِيضًا أَوْ عَلَىٰ
سَفَرٍ فَعِدَّةٌ مِّنْ أَيَّامٍ أُخَرَ وَعَلَى الَّذِينَ يُطِيقُونَهُ فِدْيَةٌ طَعَامُ
مِسْكِينٍ فَمَن تَطَوَّعَ خَيْرًا فَهُوَ خَيْرٌ لَّهُ وَأَن تَصُومُوا خَيْرٌ لَّكُمْ
إِن كُنتُمْ تَعْلَمُونَ
Kwanuka ƙidãyayyu. To, wanda ya kasance daga gare ku majinyaci ko
kuwa yana a kan tafiya, sai (ya biya) adadi daga wasu kwanuka na dabam. Kuma a
kan waɗanda suke yin
sa da wahala akwai fansa; ciyar da matalauci, sai dai wanda ya ƙãra alhẽri to,
shi ne mafi alhẽri a gare shi. Kuma ku yi azumi (da wahalar) ne mafi alhẽri a
gare ku idan kun kasance kuna sani. (suratul Baqara aya ta 184)
Matukar likitoci sun tabbatar ba
za ta samu sauqin da za ta rama azumi daga baya ba, ya halatta ta ciyar a
maimakon kowacce rana.
Allah ne mafi sani.
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da
Sunnah. Ku kasance Damu...
Ku Kasance Da mu Cikin Wannan Group Domin Ilimantarwa
Tare Da Faɗakarwa a Sunnah.
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/GhLY39kRlZEIdcZUmGchEm
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.