Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Mlm ya aiki to ALLAH saka muku da alkhari. Mlm
tambayana shi ne don Allah an ce addu'a ranan Juma'a karɓebe ne shi ne nake so amun karin
bayani kuma dawani lokaci ne ya fi cancanta.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Ranar juma’a tana da wani lokaci na musamman da Allah
yake amsar addu’o’in bayinsa a cikinsa. Annabi s.a.w ya bayyana haka:
Annabi s.a.w ya ambaci ranar juma’a sai ya ce: (a
cikinta akwai wani lokaci da babu wani bawa musulmi da zai dace shi, yana
Sallah yana rokon Allah a cikinsa wani abu, face Allah ya basa). “Qudaibata ya
kara a cikin riwayarsa, sai Annabi s.a.w ya yi nuni da Hannunsa yana nuna
lokacin kaɗan ne”
@Bukhari da Muslim da Malik a Muwaddha da Ahmad.
Malamai sun yi saɓani akan wani Lokaci ne
wannan:
Ibn Qayyim R.A yana cewa: “Malamai sun yi saɓani akan wannan lokacin na
ranar juma’a,an sami maganganu guda goma”.
@Zadul Ma’ad.
Amma maganar da tafi karfi a cikin gomar magance guda
biyu:
1-Daga hawan Liman kan Mumbari zuwa kare Sallah.
Dalili akan wannan shi ne:
“Abinda Imam Muslim ya
ruwaito a cikin Littafinsa daga Hadisin Abi Buraidah bn Abi
Musa: Lallai Abdillahi dan Umar R.A ya ce da shi: Shin
kaji babanka yana bada Hadisi daga Annabi s.a.w akan Lokacin Amsa addua a ranar
juma’a??? Sai ya ce EH: Na ji shi yana cewa: naji Annabi s.a.w yana cewa: (Shi
ne tsakanin Zaman Liman akan Minbari zuwa kare Sallar juma’a).
@Mulim.
2-Bayan Sallar La’asar: Kuma Malamai sukace wannan
magana itace mafi rinjayen magana. Ita ce maganar Abi Huraira R.A da Abdillahi
Bn Sallam R.A da Imam Ahmad da sauran Malami da dama. Hujjarsu ita ce: Daga Abi
Sa’I’d da Abi Hurairata R.A suna cewa: Lallai Annabi s.a.w yace: (Lallai a
ranar juma’a akwai wani lokacin da babu wani bawa musulmi wanda zai dace da
wannan lokacin yana rokon Allah alkhairi a cikinsa face sai Allah ya bashi, shi
ne bayan Sallar La’asar).
@Ahmad
A hadisin Jabir bn Abdiilah R.A Annabi s.a.w yace: (Ku
nemi wannan lokacin a sa’ar karshe bayan SallaR La’asar).
@Abu Dauda da Nisa’I.
Allah ne mafi sani.
Ku Kasance Damu Cikin Wannan Group Domin Ilimantarwa
Tare Da Fadakarwa a Sunnah.
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/DVpHjgfRdK9IRWvkB23lbE
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.