Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalmu alaikum, malam Allah ya karamaka lafiya
da imani, tambaya ta shine adu'ar da akeyi bayan la'asar a ranar juma'a
za'a iya lafila ne Sai ayi adu'ar ? na gode
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Ba'a yin sallar nafila bayan sallar la'asar har zuwa faduwar rana. Abin da mafi yawan mallamai suka fassara wannan hadisin Daga Abu Huraira (R), Manzon Allah (SAW) ya ambaci ranar Juma'ah, sai yace: "a cikinta akwai wata sa'a, ba wani bawa musulmi da zai dace da ita yana sallah yana rokon Allah wani abu face sai Allah Ya bashi shi",shine, Sallah da aka ambata a hadisin yana nufin: Zaman jiran sallah, kamar mutum ya zauna bayan la'asar yana jiran magriba tayi, manzon Allah (SAW) yace: Dayan ku ba zai gushe ba yana cikin sallah; matukar yana zaman jiran sallah" Bukhary
Ko kuma wanda ya shiga masallaci bayan sallar la'asar
zaiyi tahiyyatul masjid (gaisuwar masallaci) kafin ya zauna shima sallah ne.
Ko kuma sallah a hadisin ana nufin ma'anarta ta lugar
larabci, wato addu'a da kaskantar da kai ga Allah
والله أعلم.
SHAIKH NASIR ABUBAKAR SALIH
Ku Kasance Damu Cikin Wannan Group Domin Ilimantarwa
Tare Da Fadakarwa a Sunnah.
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/DVpHjgfRdK9IRWvkB23lbE
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.