Ticker

6/recent/ticker-posts

Limamin Ɗan Luwaɗi

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu Alaikum. Limamin masallaci ake zargi dayin luwaɗi sannan anzo antabbatar da yanayi sannan kuma ba canza shiba haryanzu shi ne limami shin ya kamata mubishi sallah kokuwa?

𝐀𝐌𝐒𝐀👇

Toh asali dama duk mutumin da be kafirtaba toh ya halasta a bi shi sallah. Toh dan luwaɗi matukar be halasta yin luwaɗinba toh shi musulmine ya halasta a bi shi sallah amma be kamata ba ana da shi ya zama limami ratibi wannan shi ne malamai suka ce makaruhine sannan kuma tun da ku ba ku da ikon cire shi toh kawai seku cigaba da binshi sallar musamman idan ya zamana cewa kuna da yawa ko kuma kuna da fada aji domin ba a so kauracewarku ya haifarda rabuwar kai tsakanin musulmi, amma in har kuna da tabbacin cewa kokun kaurace ba za a samu rabuwar kaiba toh kawai seku koma wani masallacin idan akwai, in kuma babu wani masallacin toh sekuyi hakuri kucigaba da zama a nan har Allah yakawo lokacin da za a canza shi.

Allah ya sa mu dace

Ku Kasance Da mu Cikin Wannan Group Domin Ilimantarwa Tare Da Faɗakarwa a Sunnah.

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/BXjuXb1WxX99NV3OsXPnLV

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

************************************** 

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments