Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Miji ne ya ce da matansa ta je asibiti tasaka abin ƙanyade iyali sai tace masa a,a itakan tana tsoro gaskiya sai
mijin ya ce duk ranan da tasami juna biyu a bakin auranta Ana cikin haka sai
tasamu shi ne na ce ya matsayin auran nata?
𝐀𝐌𝐒𝐀👇
Toh Malamai sunada saɓani a kan wannan matsalar.
Daga cikin Malamai akwai waɗanda suka ce matar ta saku
saki uku. Wasu kuma suka ce A'a ta saku amma dai saki ɗaya ne. Wasu kuma suka ce ai
batama saku ba tukunna harse an tambayi Mijin shin ɗaya ce idan tasamu ciki
abakin aurenta mene yake nufi?? Idan ya ce saki yake nufi toh suka ce ta saku
saki ɗaya. Inkuma ya ce A'a shi yafaɗane kawai dan ya tsoratata
ta yi abun da yakeso amma baya nufin sake toh suka ce ba ta saku ba. Wannan shi
ne ra'ayinda muka zaɓa insha Allahu. Ana iya duba Alwajiz Fi fiƙhis sunnah a babin saki.
Allah ya sa mu dace.
Ku Kasance Damu Cikin Wannan Group Domin Ilimantarwa
Tare Da Faɗakarwa a Sunnah.
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/ECƘsg2ycfS0FUI3fHfIdjƙ
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
No comments:
Post a Comment
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.