Idan mutum yana Azumi sai ya ci ko ya sha abin sha da mantuwa, azuminsa ingantacce ne, babu ramuwa a gareshi bare kaffara.
Abu Huraira
(R.A) ya ce:
Manzon ALLAH
{s.a.w} ya ce:
Wanda ya manta ya ci ko ya sha lokacin da yake Azumi,
to ya ci gaba da azuminsa, hakiƙa, ALLAH ne ya ci da shi ya
shayar dashi.
[Bukhari ne ya rawaito].
Idan mutum yana Azumi sai amai ya zo masa ya amayar
dashi, to babu komai a gareshi.
Saboda faɗin Manzon ALLAH {s.a.w} da
ya ce:
Wanda amai ya
zo masa lokacin yana Azumi ya amayar ba komai a gareshi, idan kuwa da gangan ya
jawo aman to, ya rama Azumi.
[Tirmizi ne ya rawaito].
ALLAH shi ne mafi sani.
ALLAH ka gafarta mana zunubanmu baki ɗayanmu Ameen.
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.