𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum. Mallam mutum ne yana kallon hotunan mata a waya (hanset) kuma yana azumi, bayan yaje ya yi fitsari sai ya ga maziyyi ya fito masa, to ya matsayin azuminsa yake?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Mutum yana azumi kuma ya tsaya yana kallon tsaraici ai
baka kyauta ba, kuma dama shi ya sa malamai suka kasa azumi mataki-mataki akwai
azumi na gama gari akwai azumi na ke6antattu, akwai azumi na
ke6antattun-ke6antattu.
1- Azumin gama gari shi ne idan anayi ba za a ci ba ba
za a sha ba baza a yi jima'i ba amma kuma sauran shiririta ba za a kauracemishi
ba, kamar kallon hotana na batsa, ko kallan mata a kan hanya suna hucewa,
dai-dai sauran abubawa da suke haramun.
2- Azumin ke6antattu kuwa su ne wadanda suna azumin
bakinsu yana azumi, farjinsu yana azumi, idon su yana azumi, kunnansu yana
azumi, baza su saurari zance na batsa ba ko munmunan zance ba, haka nan
hannunsu ba zai ta6a haramun ba, haka nan kafar su bazata taka zuwa gurin da
yake haramun ba, wannan dai shi ne azumi na ke6antattu.
3- Shi kuma azumin ke6antattun-ke6antattu shi ne yanda
bakinsu yake azumi haka nan ga6o6insu suke azumi, tunaninsu ma azumi yake
zuciyar su azumi take, kai duk wani ga66ai nasu azumi yake.
Dan haka wai a ce mutum yana azumi, har yakai ga
kallon hotunan batsa a waya har takai ya zubar da maziyyi, a gaskiya hakan da
aka yi an yi ɓarna, saboda haka a hukuncin malikiyya dai idan har
haka takasance da mutum to zai rama wannan azumin, kuma bawai zai cigaba da cin
wani abu ba a'a zai cigaba da kamun bakinsa har a sha ruwa, sai kuma bayan
sallah ya rama.
Idan kuma kullum haka yake yi to duk zai ramasu bayan
an gama azumin, kuma idan har ya zo da tsautsayi aka zubar da maniyyi to wannan
sai ramuwa da kaffara, ma'ana za a rama wannan kuma a yi na kaffara guda 60 ba hutuwa.
WALLAHU A'ALAM
Ku Kasance Damu Cikin Wannan Group Domin Ilimantarwa
Tare Da Fadakarwa a Sunnah.
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/L8l4xHCd7wUG5xZEmvBbzB
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.