𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum Dafatan An Wuni lfy Malam dama tambaya Nike a kan Hukuncin Zinar ido ta hayar kallon abin da yake na haramu, Kuma da Banbancin da ke tsakanin Zinar jiki data ido.
𝐀𝐌𝐒𝐀👇
Zinar ido (wato kallon abin da Allah ya haramta) da
kuma zinar jiki da jiki, dukkaninsu laifuka ne masu girma. Domin kuwa Allah ya
haramtasu a cikin Alƙur'ani da kuma hadisai ta
harshen Annabinsa ﷺ.
1. Zinar ido tana daga manyan hanyoyin da Shaiɗan yake bi domin jan mutane
zuwa ga aikata zinar jiki da jiki. Shi ya sa ma Allah ya ce wa Annabinsa ﷺ "Ka gaya wa muminai
maza su runtse idanuwansu kuma su kiyaye farjojinsu, wannan shi ya fi tsarkakewa
gareku. Hakika Allah masani ne game da abin da suke aikatawa".
Imam Ibnu Katheer ya ce: "Wannan umurni ne daga
Allah (SWT) zuwa ga bayin sa Muminai cewa su runtse idanuwansu daga kallon duk abin
da ya haramta musu. Kada su kalli komai sai abin da ya halatta musu
kallonsa".
Manzon Allah ﷺ ya faɗa a cikin wani hadisi cewa
"Kallo, wani kibiya ne mai dafi (poison) daga kibiyoyin iblees. Duk wanda
ya barshi (wato ya bar kallon) domin tsorona, zan chanza masa da wani imani,
zai ji ɗanɗanonsa a cikin
zuciyarsa".
(Tabaraniy ne ya ruwaitoshi).
2. Ita kuwa zinar jiki da jiki, ai Manzon Allah ﷺ ya ce "Bayan yin
shirka da Allah, babu wani zunubi mafi girma kamar maniyyin da wani mutum ya
sanya a cikin mahaifar da ba ta halatta gareshi ba". Kuma ya ce
"Mazinaci ba zai yi zina alhali yana mumini ba". (Wato sai bayan an
cire masa imani).
Zinar ido babu haddi a kanta. Amma zinar jiki da jiki,
in dai shaidu suka tabbata a kan masu laifin, ko aka samu Iƙirari tabbatacce daga masu laifin, ana yi musu haddin bulala ɗari (100) idan basu taɓa aure ba. Idan kuma sun taɓa yin aure hukuncin rajamu
ake musu (wato jefesu da duwatsu har sai sun mutu).
Kuma Manzon Allah ﷺ ya bada labarin da ke nuna
cewar ko da a cikin wuta, mazinata wajen azabtar da su ya bambanta, ya fi muni
fiye da na sauran 'yan wuta. (Allah shi kiyaye mu da aikata zina, kuma ya kiyaye
mu daga shiga wuta).
Allah ta'ala ya sa mu dace
Ku Kasance Da mu Cikin Wannan Group Domin Ilimantarwa
Tare Da Faɗakarwa a Sunnah.
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/DTrJJCF04ƘpACEtA7hyu4R
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.