Sheikh Dr. Isa Garba Nayaya
Ya yaɗu tsakanin jama’armu a nan Arewa “Ni zaben ma
ba zan yi ba”, za ka ji mutum ya na fadan haka da zimmar bawa wasu haushi ko
huce haushi, amma shi wawan naka bai san cewa hakan da ya ke fada yana daɓawa kansa wuka ba ne.
Na’am lallai yana daɓawa kansa wuƙa,
amma bai sani ba, kaito zai fahimci abubuwa masu zuwa:
- Samar da shugaba wajibi ne a
addinance, da lalura ta rayuwa, a addinance Manzo SAW ya tabbatar mana cewa:
“Duk wanda ya mutu ba shi da shugaba da ya yi masa mubaya’a, ya mutu mutuwa
irin ta jahiliyya”, domin kuwa su ne suke fariyar tafiya babu jagoranci.
Kamar yadda ya umarci matafiya
idan sun kai uku da su nada jagora a tsakaninsu; to, yaya idan lamari da ya
shafi dubunnan jama’a!? A'a, miliyoyin ake magana, haka nan buƙatar
rayuwa ta buƙaci
haka.
A duniyar mu ta yau: kowa ya na
da damar zaɓowa kansa
shugaba cikin tsarin da shi ne abin da ya iya sauwaƙa ga Musulmi; a yanayi na
rauni da yake rayuwa a yau, don haka ko mutum ya yunƙura ya yi amfani da
damarsa, ko a zabo masa wanda zai iya danne masa wasu haƙƙoƙinsa, wanda da ya motsa
ya iya samuwa ko kuma wasu daga ciki.
- Quri’a a yau makami ce na yaƙi da
tafi bakin bindiga a duniyar yau, da ita za ka ƙwatowa kanka ƴanci. Yaƙi kuwa
idan ya zama dole ba za ka zauna a ɗaka
ka na zaton za ka tsira ba; domin har cikin ɗaka
(ɗaki) za a
cimma-domin ka kare kanka da al’ummarka da addininka, dole ka futo ka yi abin
da za ka iya, sai Allah SB Ya dubi gazawarka, Ya ba ka nasara ko faduwa mai
dauke da izna.
- A addinance duk yayin da
shugaba ya shelanta yaƙi a kan kowa da kowa, babu mai uzuri ko iyaye ba su da damar
hana wanda ya isa futa fagan fama, idan lamarin haka yake, lallai ko a yau zabe
yaƙi
ne na ƙuri’a, kuma shugabanni sun
shelanta, kuma maslahar addini ya na wajabta maka ka futo ka yi zabe, musamman
idan ka duba yadda abokan zamanka su ka ɗau
himma, suke ƙoƙarin
haɗewa waje daya a
lokacin da muke a tarwatse.
- Zabe alƙalanci ne, don haka kai
mai zaɓe raba gardama
za ka yi da abin da ka sani na zahiri tsakanin mutanen da suke rigima na cewa
su suka cancanci jagorantar ka, abin da ke baɗini
kuwa sai ka barwa Allah.
- Zabe sheda ce, sheda kuwa idan
an nemi mutumin da ya ɗauke
da ita, ya zama wajibi ya isar da ita, domin ba ya halatta a musulunci ka san
abu, kuma a neme ka ka zo ka bada sheda sai ka ƙiya kamar yadda Allah SB Ya hane ka.
- Don haka idan ka ƙi yin
zabe kanka da al’ummarka
da addininka da ƴaƴanka ka cuta, kuma ka ha’inci makomarsu.
- Addu’a makami ce, don haka a
yunƙura
a yi addu’a, Annabi
SAW zai futa yaƙi, kuma ka gan shi cikin filin daga ya dage da addu’a.
- Kada Allah Ya bar mu da
wayonmu, ko dabarar mu, ko ƙarfinmu, ko aikatau na wawayen cikinmu, gare KA muke kai
kukanmu, Ka zaɓa mana
na-gari ba don halinmu ba, kuma Ka agaje shi da ludufin Ka da Ya Ladeefu. Amin.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.