Wannan ɗaya ce daga cikin jerin waƙoƙin da aka yi wa Alhaji Aliyu Magatakarda Wamakko (ALU). A hasashen manazartan Amsoshi, ALU shi ne gwamnan ƙasar Hausa da ya fi kowane gwamna yawan waƙoƙi da aka yi masa.
Alu
Sarkin Yamma garkuwa ga sahabbai,
Fari
ahalissunna ne na Allah wutiri.
Da
sunan Allah nake yabon sayyadina,
Ta’ala,
mulkinsa shi ya mamaye ko’ina,
Huwal
ƙadiru muƙtadir
Jazah bul hasana,
Tabaraka
Allah Maɗaukaki
mai ji na,
Ka yaye mana wahhala a dukkan
lamari.
Aminci
tsiranka ya Ilahis samadi,
Ka ƙara shi ga Ɗaha wanda shi ne sanadi,
Ga
dukkan bayinka gunka shi ne mahadi,
Wasila
ya Rabbana daɗo ba adadi,
Maƙamal
Mamudu sai imamul Mamadi.
Da
dukkan matansa Sidi Abdul Fɗima,
Kamar
A’ishatu da Zainab Ummul Salma,
Da
Sayyada Khadijatu da Maimunatu ita ma,
Da
dukkan matansa Ummahatul ulama,
Da ‘ya’yansa dukansu masu hali na
gari.
Da
dukkan assahabu masu tsantsar ilimi,
Kamar
Sidi Abubakar da Umar jarumi,
Da
Usman Affan da Ali ƙofar
ilimi,
Dukan
kulafa’ur rashidina taskar ilimi,
Da dukkanin wanda an ka wa alƙarari.
Da
dukkan auliya’u masu hali na gari,
Kamar
Shehu Tijjani da shi da Abdul Ƙadiri,
Da
Shehu Ibrahimu mai yabo gun Bashari,
Da
Shehu Usmanu bini Fodiyo na wutiri,
Ala
zummatu Mustafa abin alfahari.
Salamu
alaikum ya’yan uwa tare da ni,
Da
wanda suke nesa hankalinku ku ba ni,
Nufina
ku taho mu ƙari junanmu sani,
Mu
laiƙa hadisai mu dubi Alƙur’ani,
A kan ƙaunar
ashabu za mui nazari.
Farillane
kan dukan Musulmi na gari,
Bauta
wa Rabbu babu kawo uzuri,
Da ɗa’a
ga gwani sannan ya zyo gun Bashari,
Son
Allah da Manzo da ‘yan gidan Aɗɗahiri,
Da karatun Ƙur’ani
ya kauce wa haɗari.
Sannan
ya iso ga waɗanda sunka yi yo dace,
Da
sun kai ladabi ga Ɗaha
sunka amincie,
Allah
ya yarda da su da yarda tasa ce,
Da
yai musu albishiri da aljannarsa ce,
Da yac ce sun sami tsira ran ashari.
Su
ne fa sahabbai a gun imamum Bashari,
Da ƙaunar manzo ta sa su kay yo katari,
Allah
ya shaide su kan ɗabi’a ta gari,
Da
Allah ya yabe su ɗahirai ne na gari,
Duk mai ƙyamar kowanensu ya shiga haɗari.
Dalilina
na gani cikin Ƙur’ani ne,
Inda
Allahu yake yabon sahabban Ɗaha
ne,
Da
yac ce sun tsira ran ƙiyama
haka ne,
Da
yai musu tanadi gida na aljannatu ne,
A dan haka ƙauna gare su bautan wuturi.
Allah
ya ce ga Mustafa majiya na arashi,
Da
waɗanda
su kai imani da ad tare da shi,
Sun
yi jihadi dukiyoyinsu ba ƙyashi,
Kuma
sun yi da rayukansu don ƙaunar
shi,
Suna da alkairi masu yawa inji
wutiri.
Ya
ce yai musu tanadi a ranar tsayuwa,
Yac
ce sun sami tsira ne da yawa,
Da
yab ba su gidan Aljanna domin taƙawa,
Da
yac ce shi ne rabo mafi girma kuwa,
Duk mai ƙaunar su babu shi ba garari.
Son
Allah shi ne son manzo ku yo nazari,
Son sahabban
Ɗaha so ga manzo Bashari,
Idan
ka ƙi sahabu ka warware alƙawari,
Da
kaɗ ɗauka
tun kana ciki ka yo ƙudiri,
Idan ka tuba Ilahu zai ma uzuri.
Dukan
hujja babu ita ban ganta ba,
Suka
ga sahabu ba hali mai kyau ba,
Da
auren mutu’a fa ba koyin Annabi ba,
Da ƙazafin da su kai ba za ni furta muku ba,
Zan ce yai muni su tuba domin
wuturi.
Dalilin
da na ce Aliyu sarkin Yamma,
Ya
zam garkuwar sahabu ba ƙarya
ne nai ba,
Domin
bai yarda a soki ko wanne ba,
Ya
ce da su kowat tuba Ilahu zai yafe mai,
Idan sun ƙi ba za shi ƙyale ko ɗai a
gari.
Jama’ar
Sokoto da duk su kay yo gangami,
Sun
ka zaɓi
mujahidi ƙwararre jarumi,
Sun
so mai gaskiya sahihin malami,
Da
ya hana ɓarna
ya sa magabta nai gumi,
Allahu ya ba mu shi sahihi na gari.
(Sokoto yake faɗa,
shi ya sa na rubuta haka).
Alu
ahlis-sunna ne fa ba ƙarba
ba,
Dalilina
zan faɗa ba
zan noƙe ba,
Da
yaz zam bautar Ilahu yas sa a gaba,
Ya
daidaita sahu ya yo fa in kun duba,
Da komai zai yo fa zai yi domin
Wuturi.
Alu
bai wasa da bautar Ilahu gwani,
Ma’abocin
salla ne ga shi mai imani,
Da
yas samu rabo da ba shi yin gunguni,
Sannan
ko da yaushe yana karanta Kur’ani,
Ba ya raina aikin lada akwai shi da ƙoƙari.
Yana
so domin Gwani ya ƙi
domin Gwani,
Yana
yarda don Gwani fa bai gunguni,
Yana
umurni da aikin alkairi ne masani,
Yana
hani ga dukkanin mai muni an sani,
Kyawun hali nai ya zaga ƙauye da gari.
Mai
halin ƙwarai da ba shi yin alfahari,
Da
ke girmama baƙi da mutanen gari,
Yana
girmama maƙwabta Alu mai nazari,
Mai ƙaunar jama’a da munka samu na gari,
Ba ya ƙwange
ko kaɗan
abin alfahari.
Alu
bai kibiri fa ko fushi don garari,
Mai
halin kyauta gwamnanmu mai alkairi,
Da
ba ya ƙyamar konannenmu mai haƙuri,
Abin
ƙaunar jama’a ta ƙauye
da gari,
Ƙwararre
mai juriya ga kowa jari.
Alu
rabbil mukazzibina ne ba mai ja,
Da
munka yi mubayi’a fa mun san hujja,
Da
yaz zam garkuwar sahabu ba ja-in-ja,
Yardadden
shugabanmu babbar hujja,
Allah yai baiwa gare shi mai kyan
sadari.
Amintacce
ba ka cin amana haka ne,
Amintacce
mai yawaita kyauta mani,
Mai
alkunya da laddabi da kamun kai ne,
Mai
tsantseni mai halin girma ga kowane ne,
Muna nan bayanka ba ka saɓa alƙawari.
Abin
so mai taimako ga kowa ne ma,
Da
ke kyautata rayuwarmu ne mai himma,
Da
ilmi da Rabbi yay da kowa ya nema,
Mutuntacce
ne Aliyu Sarkin Yamma,
A gai da na Allah na Mustaɓa na
Bashari.
Ba
ya wasa gun fitar da zakka ne shi,
Ya
sauke faralinsa ya yi aikin hajji shi,
Ma’abuci
na umara da ba ya ƙyashi,
Alu
ya sam albarkanmagabatanshi,
Sannan ya riƙi ‘yan
uwansa mui yo nazari.
Mijin
Hajiya Arziki da Murjanatu ne,
Baban
Mahadi da Fodiyo da Lamiɗo fa ne,
Mahaifin
Isa Alu da bai cara ne,
Abin
alfahari na Sarkin Musulmi ne,
Sa’ad
Abuabakar da ke da hali na gari.
Tamat
an nan zan dakata a wannan shiri,
Baban
Halima Kaduna ne fa marar fikiiri,
Da
sam ban da sani barai ya sa ai marari,
Shaiƙi yas sa ni baituka nai nazari,
Na yo don ƙauna ga gwamna ne kai nazari.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.