Ticker

6/recent/ticker-posts

Bambancin Sha'awa Da Soyayya (Kashi na 27)

Wannan na ɗaya daga cikin jerin rubuce-rubucen da Zauren Markazus Sunna ke samarwa kan batutuwa daban-daban da suka shafi rayuwar al’umma. A wannan karon rubutun ya shafi “Bambancin Sha’awa Da Soyayya” wanda Baban Manar Alƙasim ya rubuta.

Bambancin Sha'awa Da Soyayya (Kashi na 27)

Baban Manar Alƙasim

g) Akwai babbar gudummuwa da maigida zai ba wa iyalinsa wajen ganin gida ya ginu sosai yadda ake buƙata, galibin aurarrakin da ake yi yau za ka taras ko dai hadawa aka yi, ko kuma a kan hanya ya gani kuma ya dauka, amma akwai wasu 'yan daidaiku da ba a rasawa wadan da a makaranta aka hadu ko a wajen aiki, irin wannan gamuwar ta daidaitacciyar wayewa ta fi sauƙi nesa, sama da wata, in ya kasance akwai tazara mai girman gaske ta ilimi ko wayewa a tsakanin maigida da uwargida zai yi kyau shi ma ya jefa ta makaranta, ko ba za ta yi aiki ba za ta dan sami damar da za ta riƙa yi masa hirar da yake so, ko ta fahimci abubuwan da yake buƙata da lokacin da yake buƙatarsu, in ta yi nesa da shi ba dole ba ne su riƙa fahimtar juna. Sau tari za ka ga dan boko zalla wanda bai da wata wayewa a karatun muslunci sama da karatun sallah, in ya ga wata yarinya kamammiya ko kyakkyawa sai ya auro don tarbiyyar yaransa, galibi akan dan sami matsala don ita tana yi masa kallon jahili ne tuburan, wasu lokutan ma takan kai ga sai ta dan yi masa wa'azi, shi kuma ba dole ne ya fahimce ta ba, masamman idan ya gano cewa tana raina ƙoƙarinsa a addinance ga shi kuma shugaba, kyau dai ya saka ta a makarantun bokon, shi ma ya dan koma wata islamiyyar manya don ya gyara yanayin zamantakewar. A binciken da muka dan yi da wasu 'yan uwa marubuta mun gano cewa galibin matan da suke da karatu ba a wurin mazansu suka koya ba, karatun miji da mata bai cika ƙarko ba, shi yana ganin shi malami ne, ita kuma ta san maigidanta ne kawai, dan abu kadan zai nemi yin fada, ita kuma ba za ta jure ba, da ma wani ne ba shi ba, to in ba a yi dace ba sai ka ga ana ta samun sabanin fahimta, in ka lura da kyau galibin matan malamai ba malaman ba ne, to amma da mazan za su kai su makaranta tabbas za su yi karatun a can. h) Kamar dai nuna ƙauna da fadi a baki galibin mata suna son haka, in namiji ya ga ba zai iya ta sa matarsa a gaba ya ce "Wallahi kina bala'in burgeni" ba, to ya dace ya namo wata hanyar da za ta maye makwafin wancan, kamar dai 'yan wasanni, ko ba-kan-zata, wato ya dan riƙa siyo mata wasu abubuwan da ba ta yi tsammanin samunsu a daidai wannan lokacin ba, kamar sarƙoƙi, kayan shafe-shafe, da na fesawa, sai kuma 'yan kayan ƙwalama gwargwadon yadda Allah ya hore wa mutum, wani lokaci har irin bugo wayannan ka tambaye ta halin da take ciki yana da dadi.

i) Wasu lokutan fa dole sai an sai da rai kafin a sami abin da ake so, wasu matan suna da wahalar sha'ani, in suka gan ka da waya ka hau yanar gizo sai su fara ƙirƙiro maka wasu abubuwa, kamar dai karatun yara ko na su, ko su ce ka watsar da su ka shiga wata saugar, sau da yawa maza kan zaci cewa kishi ne, wata ƙila tana zaton cewa yana hira da wasu ne, sai ya yi watsi da ita, alhali ita tana neman hankalinsa ne gaba daya, in za mu lura wata ko talabijin kake kallo ka riƙa haduwa da irin waɗannan tsirfaffakin kenan, idan ka fahimci yadda za ka shawo hankalinta yana da kyau, don dai a dawo da nashadin cikin gida. j) Yakan zama wajibi kuma maigida ya dan riƙa yaba wa uwargida kan ayyukan da take yi a cikin gida, ba shakka abubuwa ne da suka zama wajibi a kanta, amma tana da buƙatar a riƙa yaba ma ta, wata ko kwalliya ta yi, ko lalle, ko kitso tana son ta ji ra'ayin maigidanta a kai, in za mu lura mace ba ta son kashe kudinta, lura da ƙarancin hanyoyin samo shi, amma in za ka yi maganar gyaran kai, ko nawa ne za ta iya kashewa, don dai kawai ta burge maigida, sabo da wannan shi ma ya kamata ya nuna gamsuwarsa, in ta dan yi kuskuren da ba ta saba yi ba ya dan daga ma ta ƙafa, ya tuna ƙoƙarin da take yi daga lokaci zuwa lokaci. k) Lokacin da wasu abubuwa da suka shafi gida suka taso, a kanta ne ko shi ko yara, ya kamata ya saurare ta tukun ya ji ra'ayinta, in bai yi masa ba to kar ya musanta kai tsaye, ko ya ƙaryata, ko kuma ya nuna ba ta da tunani, ya yi ƙoƙarin gamsar da ita ne da wani ra'ayin da yake ganin shi ya fi dacewa, lamurran da suka shafi gida da zumunta, in dai aka sami mace ta gari to ta fi kowa gwanancewa wajen tafiyar da su, in mutum ya fahimci cewa iyalinsa tana da matsala da uwayensa ko 'yan uwansa kar ya taba yarda matsalar ta ci gaba, ya yi ƙoƙari ne ya gano asalin matsalar, kuma ya magance ta, kar ya aibanta matarsa a gabansu, kar kuma ya goyi bayanta alhali suna wurin, ya dage wajen kyautata tsakaninsu.

Ta ɓangaren shugabanci kuwa, ba ja maigida shi ne jagora, kuma ba a samun jagorancin sarakuna biyu a kan lardi daya, kuma suna yin aiki iri guda, ƙarshe sai dai a haifi dan da bai da idanu, amma in har ya bar gidan to uwargidansa ita ce shugaba har sai ya dawo, to in dai zai riƙe shugabanci bari mu ga abubuwan da suka lazimce shi:- a) Shi ne mai riƙe da linzamin gidansa, mai sakawa a yi ko ya ja linzamin a dakata, ya yi ƙoƙarin sanin kowa da yake ƙarƙashinsa, kuma ya riƙa bincike in kowa yana samun abin da yake buƙata. b) Ciyarwa da shayarwa na iyali, 'ya'ya da uwaye abu ce da Allah SW Ya daura a wuyar maigida, don haka ya riƙa kallon wanda ya sanya ta a uwarsa, kar ya riƙa kallon wanda yake kyautata masa din, wani lokacin in iyali suka munana wa maigida sai ka ga yana ƙoƙarin daukar mataki, ta wajen ƙuntata wa wanda yake ci a ƙarƙashinsa, wani lokaci ma in yana fushi da matarsa, hatta 'ya'yansa da duk mai ci a ƙarƙashinsa yana iya aukawa cikin matsalar da bai ji ba bai gani ba, dole a riƙa jin tsoron Allah, ba horo da ƙuntata abin da Allah SW ya yi umurni da a kyautata ba. c) Sanin yadda za a riƙe gida a muslunce shi ne babban manhajin samar da yalwataccen gida cikin farin ciki da annushuwa, Annabi SAW ya zauna da mace guda, shekarunsa Talatin da wani abu da aure, ya kwashe mafi yawancin shekarunsa ne da mace guda, wato Khadija RA, ya yi sama da shekara 20 tare da ita har sai da ta rasu, to ya mu'amallarsa da ita? In kuma kana da mata ne daga biyu zuwa sama waiwaya ka ga rayuwarsa da matansa, shi a matsayinsa na Annabi ya ajiye mata tara a lokaci guda, yaya ya zauna da su? Tabbas akwai ababan koyi a wurinsa, don ya auri wace ta haife shi (in maganar ta inganta) ya auri yarinya danya sharaf, kuma kowacce ta fi son sa sama da kowa. A nan zan dakata. Sai mun haɗu a rubutu na gaba.

Bambancin Sha'awa Da Soyayya (Kashi na 27)

Post a Comment

0 Comments