Ticker

6/recent/ticker-posts

Bambancin Sha'awa Da Soyayya (Kashi na 22)

Wannan na ɗaya daga cikin jerin rubuce-rubucen da Zauren Markazus Sunna ke samarwa kan batutuwa daban-daban da suka shafi rayuwar al’umma. A wannan karon rubutun ya shafi “Bambancin Sha’awa Da Soyayya” wanda Baban Manar Alƙasim ya rubuta.

Bambancin Sha'awa Da Soyayya (Kashi na 22)

Baban Manar Alƙasim

Lura da inda ya dace mutum ya miƙa diyarsa shehin malami Algazali RL yake cewa a cikin Ihya'ul Islam: Lura ta ƙarshe ga yarinyar ita ce ma fi dacewa, domin hidimar aure yakan maishe ta baiwa, ba yadda za ta yi ta kauce masa, ga shi kuma maigidan yana da damar yin saki a kowani lokaci, in mutum ya aurar da 'yarsa ga azzalimi, ko fasiƙi, ko dan bidi'a, ko mashayi, haƙiƙa ya yi wa addininsa illa, ya kuma fada cikin fushin Allah AW sabo da yanke zumuntarta da kuma mummunan zabinsa. Da wannan dole a nemo ma ta miji na ƙwarai, mace mutuncin namiji ce, wajibi ne mutum ya tsare mutuncinsa, kamar yadda yake tsare dukiyarsa, mai hankali shi ne yake yi wa 'ya'yansa mata tattalin inda za su zauna, da irin mazan da za ta yi mu'amalla da su, a ƙalla dai in aka ce "Wane ne sirikinka" ba zai damu ba, koda yake mu a wajemmu babban abin kunya ne ka ce wa mutum "Ga 'yata ko za ka aura?"

Umar bnl Khattab RA da haibarsa da matsayinsa a duniyar muslunci, ya ajiye komai ya tallata wa manyan sahabban Annabi SAW diyarsa, ba faduwar girmansa ya duba ba, darajar wadan da ya je wurinsu ya kalla, a ƙarshe dai Annabi SAW ya aure ta. Yanzu dai bari mu gani, wace mace ce ya kamata a nema? 1) Ya zama dole a nisanci wace take ƙarƙashin wani, ba a neman matar aure, shi ya sa nake ganin hatta hanyoyin sadarwa na zamanin nan ana mugun kwabawa a ciki, don matar aure takan saki jiki da wasu mazan ta yi ta hira da su, har sha'awa ta gindaya tsakani, dole a guji fushin Allah, macen da take ƙarƙashin wani ta haramta ga wani ƙato matuƙar tana cikin wannan halin, a bayyane yake Allah SW ya hana wace take iddar wani mamaci ta yi zancen aure da wani, har sai ta gama idda, to ina ga wace take ƙarƙashinsa kuma yana da rai? 2) Ta biyun ita ce wace muka fada, wato wace mijinta ya sake ta, ko wace ya mutu ya bar ta, matuƙar suna cikin idda bai halasta wani ya neme ta ba, ina da wani babban lekcara na ji shi yana gunaguni kwanaki, wai wata da yake bala'in son ta ta fito daga gidan miji, wai ya dan yi irin kawaicin addini dinnan har ta gama idda, kawai sai ya ji wani ya shiga gabansa, ya zagi saurayin ba kadan ba, ya fadi rashin dacewarsa da bazawarar, da sauran maganganu irin na kishi, tabbas ba a neman mace a cikin idda, kamar yadda ba a ziga mace ta rabu da maigidanta don a aure ta, Annabi SAW ya la'anci mai yin haka. 3) Ta ƙarshe ita ce wace wani ya fara nemanta, a muslunci in dai wani ya fara neman aure, to bai halasta ba wani ya shiga, irin wannan kuskuren da yawammu muna fadawa ciki, kuma kowa yana da na sa kason gwargwadon hali.

i) Iyayen yarinya suna sane da cewa diyarsu tana da saurayi amma suka zuba ma ta ido don ta yi abin da ta ga dama, ta kawo musu kudi. ii) Yarinya kwadayi ya yi ma ta yawa, wani lokaci ba ta son mutum amma ba za ta iya haƙuri da abin hannunsa ba, sai ta riƙa ririta shi kafin wani ya zo. iii) Sai kuma mu ( ko na ce su ) samari, da gangan muke shiga neman yarinya bayan muna sane da cewa tana da saurayi kuma ta shaƙu da shi, sau da yawa ma sai an kwashi dauki ba dadi da yarinyar kafin a fara magana da ita, na taba raka wani sai iyayen suka ce tana da saurayi amma ita mace allura ce a cikin ruwa, mai rabo ne ke dauka, ko tana da saurayi bai nufin shi ba zai aura ba tun da har ba a daura auren ba, to ko uwayen yarinyar ba su fadi wannan ba dama abin da yake cikin ƙwaƙwalwarmu kenan, sai dai yanzu alhamdu lillahi da muka fara zuwa makaranta, wasu abubuwan mun san ba kyau mun bari, bai dace ba wani ya fara neman aure kai ma ka je ka shiga. Duk da haka fa ba laifi in mace tana idda misali iddar rabuwa kwata-kwata ko ta mutuwa mutum ya dan yi shagube, kamar ka ce "Wance ashe abin da ya faru kenan? Gaskiya mace kamarki bai dace a bar ki da wani abu a zuciya ba!"

Ko namiji zai iya gano irin wannan to bare mace, masamman in haka ya faru sau biyu ko sau uku, na taba jin wai wani ya dauki yaron wata mata yana masa wasa yana cewa "Ina ma a ce na zama babanka!" Uwar tana kallon su tana murmushi, saƙon dai ya kai, sai dai dole a ji tsoron Allah, neman mace a cikin idda abu ne mai matuƙar hatsari tunda Allah SW da kanSa Ya haramta haka.

Daga cijin ababai masu ban sha'awa da muslunci ya halasta wa mutum ya kalli mace kafin ya fara nemanta, don dai ƙauna da soyayya su sami matsuguni mai kyau, in mutum yana neman mace ya san wa yake nema, ba sai ranar budan kai ya ga abin da bai zata ba, a baya mun fadi cewa Annabi SAW da kansa ya ce wa wani sahabi ya je ya gan ta tukunna, to sai dai a Hausa akwai bambanci a tsakanin gani da kallo, kar wani ya fake da wannan kullum ya kama hanyar gidan yarinya da sunan zance. Mace ma yana da matuƙar amfani ta san wa zai neme ta, mai yuwuwa saurayin mummuna ne, ko barkeke ba kamar yadda ta zata ba, ba shakka mace ma tana da irin na ta zabin kamar yadda namiji ma yake da shi, yau in ka kasa mutane za ka taras sun kasu gida biyu ko fiye, wasu daga cikinsu sun yi sakaci wurin rashin dubawa da kansu, sai su ce in dai ta gamsar da wane shi kenan, wasu kuma sai su ce sai sun ga ƙwal uwar daka, abin da yake daidai shi ne tsayuwa a tsakiya, to meye tsakiyar? A nan zan dakata. Sai mun haɗu a rubutu na gaba.
 
Bambancin Sha'awa Da Soyayya (Kashi na 22)

Post a Comment

0 Comments