Ticker

6/recent/ticker-posts

Salon Kambamawa A Cikin Wasu Waƙoƙin Kassu Zurmi

Gudanar da rayuwar mai inganci tana buƙatar jagorancin mutane masu amana da sanin yakamata. Wannan takarda mai taken salon “ Kambamawa a cikin wasu waƙoƙin kassu zurmi” Takarda ce wadda take ƙoƙarin bayyana irin rawar da salon kambamawa take takawa ga rayuwar jaruman mutane, mutane suna son a riƙa zuga su, su yi wani aiki na mazantaka, wanda idan ba a kambamasu ba, ba za su iya aiwatar da shi ba saboda haka wannan takarda za ta mayar da hankali ga salon kambamawar kassu zurmi da yake amfani da ita cikin waƙoƙinsa na maza, domin ya ƙara ingiza wanda yake yi wa waƙa, su aikata abin bajinta.

Salon Kambamawa A Cikin Wasu Waƙoƙin Kassu Zurmi

RABI S. ZAMFARA

Kassu Zurmi

GODIYA

     Ina godiya ga Allah subhanahu wata’ala da ya ba ni damar gudanar da wannan binciken bisa ga ikonsa da taimakonsa. Haka kuma ina ƙara godiya ta ga shugaban halitta Annabi Muhammad (S.A.W).

    Haka kuma wannan aiki na da matuƙar wahala a aikatashi ba tare da an samu mataimaka ba. Don haka ya zama dole in miƙa godiyata ga malammaina waɗanda suka taimakamani musamman malamar da ta duba ni Malama Halima Mansur Kurawa Allah ya saka mata da mafificin alhairi Amin.

   Bugu da ƙari ina godewa iyayena da kuma musamman maigidana Alhaji Labaran Abubakar Zurmi wanda ya taimaka mani matuƙa wajen gudanar da wannan karatu har kawowa yanzu.

   Haka zalika ina miƙa godiya ta ga duk wanda ya taimaka mani wajen ganin na kammala wannan karatu kamar Aliyu S/ Zamfara, Shehu S/ Zamfara da kuma ƙaunata Binta Sani Nakwada, Asma’u S/ Zamfara da sauransu. Daga ƙarshe ina ƙara godewa Allah da ya gwada mani na kawo ƙarshen wannan binciken.

SADAUKARWA

Na sadaukar da wannan bincike ga mahaifina Alhaji Muhammadu Mainasara (Sarkin Zamfaran Zurmi) Allah ya jiƙansa da rahama Amin.

 

BABI NA ƊAYA

1.0 SHIMFIƊA                              

Hausawa na cewa “Tushiya mafarin dawa" Duk abin da za ka yi a duniya ya kamata ka gabatar da shi kafin ka fara bayani a kansa saboda haka dukkan lokacin da aka yi maganar kambamawa ga al'ummar Hausa sai ace abu ne bayyananne musamman idan aka yi magana a cikin wasu waƙoƙin Alhaji Kassu Zurmi.

A bisa ƙashin gaskiya makaɗa da mawaƙan Hausa na kambama ko zuga wanda ya basu kyauta da kuma wanda ya nuna bajinta ko ƙwazo domin ya yi wani abu da bai ta shi yi ba.

Saboda haka aka gabatar da wannan bincike mai taken salon kambamawa a wasu waƙoƙin Kassu Zurmi. An kasa wannan bincike akan babi-babi har zuwa babi  biyar.

Babi na farko an yi gabatarwa, da manufar bincike, hasashen bincike farfajiyar gudanar da bincike, matsalolin bincike, muhimmancin bincike, hanyoyin bincike, sai kuma naɗewa.

A babi na biyu za’a yi bayani akan bitar ayyukan da suka gabata, wato abin da ake kira waiwaye ga wasu ayyuka da suka gabata wanda ya ƙunshi bugaggun littattafai, da kundaye, da kuma maƙalu.

A babi na uku za a dubi tarihin rayuwar Kassu Zurmi, wanda ya haɗa da gabatar da tarihin rayuwarsa, iliminsa, koyo da fara waƙarsa, gadon kiɗansa, abin kiɗansa, da kawo bayani a kan yaransa, nau’o’in waƙoƙinsa da iyalansa, ƙarshe da rasuwarsa.

A babi na huɗu an yi gabatarwa da kawo salon kambamawa a wasu waƙoƙin Kassu Zurmi, kambamar zulaƙe, da kambamar yabo.

A babi na biyar wanda shi ne na ƙarshe a wannan bincike, an yi bayani akan sakamakon bincike, sai shawarwari, manazarta, da kuma ratayen wasu waƙoƙin da aka gabatar.

1.1 MANUFAR BINCIKE

Akwai manufar da ta sa aka gudanar da wannan bincike ga su kamar haka.

Dalili na farko shi ne, ina da matuƙar sha'awar sauraron waƙoƙin makaɗan Hausa musamman waƙoƙin Alhaji Kassu Zurmi, saboda haka nayi sha'awar gabatar da bincike a wasu daga cikin waƙoƙin. Dalili kuma daya sa aka gudanar da wannan bincike akan wannan makaɗi, shi ne domin a ƙara fito da wannan makaɗi a fili, duniya ta ƙara saninsa ta kuma ji irin fasaha da hikima da Allah (S.W.T) ya ba shi ta fuskar harkar, kiɗa da waƙa.

Maƙasudin wannan bincike shi ne don zaƙulo wasu daga cikin waƙoƙin Alhaji Kassu Zurmi don ayi nazarin salon kambamawa da ya yi amfani da shi a cikin wasu waƙoƙin nasa. Ta haka ne za'a zaƙulo salailan da mawaƙin ya yi amfani dasu domin nuna fasaha da Allah ya ba shi.

Haka zalika ya na daga cikin manufar wannan bincike a samar da wani kundin karatu wanda zai zama abin karantawa ga ɗalibai da manazarta.

1.2 HASASHEN BINCIKE

Hausawa na cewa “ Maiki mai hange ne sa” A bisa nawa hasashen da kuma tsinkaya da nayi ko kuma a bisa nawa kudirin da nayi domin bunƙasa ko haɓaka harshen Hausa naga ya da ce da nayi wannan bincike domin nazari da ni kaina da kuma raya matasa masu tasowa, ma’ana waɗanda zasu taso nan gaba.

Bugu da ƙari kuma na yi wannan bincike domin ganin cewa da na karanci littafai na Hausa musamman na adabi wanda ya shafi irin waɗannan shahararru mawaƙan namu na Hausa. To shi yasa nayi tunanin da hangen nesa na ganin cewa bari inyi bincike ko nazari a kan wannan shahararren mawaƙin wato Alhaji Kasu Zurmi domin bunƙasa adabin Hausawa.

Abu nagaba kuma duk a bisa wannan hasashen shi ne ina ganin cewa idan wannan bincike zai zama abin dubawa a makarantu na gaba da kuma na gaba da sakandare. Domin a saka shi a cikin ɗakin karatu don na baya su karanta kuma su karu wannan shi ne hasashe na dangane da wannan bincike da na gudanar.

1.3 FARFAJIYAR BINCIKE

Wannan bincike zai taƙaita ne kawai a wasu daga cikin waƙoƙin makaɗa Kassu zurmi, kuma binciken zai dubi ko zai zaƙulo salon kambamawa ne da mawaƙin ya yi amfani da su a cikin wasu waƙoƙinsa. Don haka duk wani abin da bai shafi salon kambamawa ba, ba za a kawo shi ba.

1.4 MATSALOLIN BINCIKE

          Na yi tattaki har garin kadawa domin in samu tabbataccen tarihin mawaƙin Kassu Zurmi, amma matarsa guda kawai na iske tare da ‘ya ‘yanta guda biyu, wadda tace min lallai ba ta da tabbacin shekarar da aka haife shi, amma tace ya rasu a lokacin da aka yi (idoji) sunan matar “Abu” wadda take zaune a gidan nasa a yanzu tare da ‘ya ‘yanta, watau Tunau, da Namakka waɗanda diyan nan nashi waɗanda suka zama malamai wanda a yanzu suna nan suna jagorantar Hizba a garin kadawa.

Tattaunawa da na yi da matarsa ‘ABU’ a garin kadawa a ranar littanin (07/02/2021) inda ta tabbatar mini bata da masaniyar shekara da aka haifeshi,Amma tace mini ya rasu a lokacin da ake yi idoji watau (1983).

Tattaunawa da na yi da matarsa ‘ABU’ a garin kadawa a ranar littanin (07/02/2021) inda ta tabbatar mini bata da masaniyar shekara da aka haifeshi,Amma tace mini ya rasu a lokacin da ake yi idoji watau (1983).

 

1.5 MUHIMMANCIN BINCIKE

Binciken zai taimaka wajen killace tarihin rayuwar Kassu Zurmi da salon kambamawa a cikin waƙoƙinsa domin amfanin masu nazari, da kuma adana wani ɓangare na adabin baka.

1.6 HANYOYIN GUDANAR DA BINCIKE

Wannan bincike ya dogara ne a kan wasu hanyoyin gudanar da bincike, wato ziyarar ɗakunan karatu don nazartar waƙoƙin baka na Hausa, ta hanyar duba bugaggun littattafai, da kundayen digiri na ɗaya, da na biyu, har zuwa na uku, da aka gudanar a fannin adabin Hausa. Sannan da duba takardu da maƙalu waɗanda aka gabatar a wurare daban-daban na ilimi.

Sannan an tattauna da masana na wannan fanni na waƙoƙin baka da neman shawarwari tare da jagorancin mai duba wannan bincike na ciki,duk dai don samun gamsassun bayanai. Haka kuma za a bi wata hanya ta yin amfani da rediyo domin sauraron kaset na waƙoƙin da aka yi nazari da kuma duk wata hanya makamanciyar wannan da zata taimaka wajen gudanar da wannan aikin.

1.7 NAƊEWA

A wannan babi an yi bayanin gabatarwa, ainahin manufar bincike, hasashen bincike, farfajiyar bincike, matsalolin bincike, haɗi da kawo mahimmancin bincike, duk a cikin wannan babi na ɗaya.

 

 

 

 

                                                                            

 

 

 

 

 

 

BABI NA BIYU

2.0 SHIMFIƊA: A wannan babi na biyu za a yi bitar ayyukan da suke gabata, haɗi da hujjar ci gaba da bincike, sannan da naɗewa duk a cikin wannan babi na biyu.

2.1 BITAR AYYUKAN DA SUKA GABATA

Babu shakka wajibi ne ga dukkan wanda ke son aiwatar da wani bincike ya waiwaya baya don ganin ayyukan da suka gabata, domin ya san inda aka kwana kuma ya san inda zai tashi. Saboda Hausawa na cewa “waiwaye adon tafiya". Shi wannan irin waiwaye ya zama tilas domin ta haka ne mutum zai nuna ya san inda ya dosa, wato yana da masaniya game da aikin binciken da zai gudanar, don haka sai ya ɗora a kansa ko ya rushesu ya gina nashi tsarin, ko ya ɗauki waɗansu abubuwa ya watsar da wasu gwargwadon yadda ya fahimta.

Akwai rubuce-rubuce da waɗansu manazarta suka gudanar wanda ya ƙunshi bayanai wanda yake kuma idan muka duba waka tana ciki. Saboda haka ire-iren waɗannan nazarce-nazarce da aka gudanar akwai bugaggun littafai, da muƙalu da kuma kundayen bincike.

2.1.1 BUGAGGUN  LITTATTAFAI 

Masana da dama da kuma manazarta sun rubuta littafai da yawa da suka shafi adabin Hausa, musamman na baka.

Ɗangambo, (2007) a cikin littafinsa mai suna Ɗaurayar Gadon feɗe waƙa, ya bayyana yadda ake nazarin rubutattun waƙoƙi a ciki ya yi bayanin salo da sarrafawa harshe da abin da ya ƙunsa da kuma bayanin waƙar baka, (zubi da tsari) da sauran su.

Aikin nasa ya yi kama da wannan sai dai inda suka bambanta shi ne wannan yana magana ne akan salon kambamawa a wasu daga cikin waƙoƙin Kassu zurmi.

Yahaya (2001) a cikin littafinsa mai taken Salo Asirin waƙa, marubucin ya yi bayanin ma'anar salo da ire-iren salo, da muhimmancin salo, haɗi da kawo nau'o’in salo. Saboda haka wannan aiki yana da alaƙa da na shi sai dai inda suka bambanta shi ne, wannan  aikin yana magana ne a kan salon kambamawa a wasu daga cikin waƙoƙin Alhaji Kassu zurmi.

Aikin ya yi kama da wannan saboda duk suna magana ne a kan mawaƙan baka na Hausa. Sai dai inda suka bambamta shi ne wannan aikin ya taƙaita ne a kan mawaƙi ɗaya ne kawai na yi nazarin salon kanbamawa a cikin waƙoƙinsa Kassu zurmi.

Gusau (2005) a cikin wannan littafi nasa mai suna maƙada da mawaƙan Hausa ya yi bayani yadda mawaƙan Hausa suka rabu, ya kasa littafin har kashi hudu. Kashi na daya maƙaɗan yaƙi, kashi na biyu makadan sarakuna , Kashi na , Kashi na uku makadan jama’a, kashi na hudu makadan sana’a.

Aikin nasa ya yi kama da wannan saboda duk suna magana ne a kan mawaƙan baka na Hausa sai dai inda suka banbamta shi ne wanga aiki ya takaita ne a kan mawaki daya ne kawai na yi nazarin salon kambamawa a cikin waƙoƙin sa.

2.1.2 KUNDAYEN BINCIKE

Masana da manazarta da dama sun rubuta kundayen bincike masu alaka da wannan bincike.

Bunguɗu. (1990) A cikin aikin binciken da ya gabatar don neman digiri na ɗaya a sashen koyar da Harsunan Najeriya, Jami'ar Usmanu Ɗan Fodiyo Sakkwato, mai suna Muhammadu Auwalu Isa Bunguɗu, da waƙoƙinsa, ya kawo gabatarwa da tarihin rayuwar Muhammadu Auwalu Isa Bunguɗu sannan ya kawo sharhin wasu waƙoƙinsa. Haka kuma ya nuna waƙoƙinsa a kan adabin Hausa, ya kuma kawo salo da zubi tsarin waƙoƙin.

Wannan aiki yana da alaƙa da wannan sai dai inda suka bambanta shi ne wannan aiki yana magana ne akan salon kambamawa a wasu waƙoƙin Kassu zurmi.

Ammani, (2009) ya gabatar da bincikensa don neman digiri na biyu a sashen koyar da harsunan Najeriya jami’ar Bayaro, Kano, mai suna “Nazarin maganganun Hikima a waƙoƙin Aliyu Ɗandawo” A cikin wannan aiki ya fara yin shimfiɗa da gabatarwa da ma’anar waƙar baka ta Hausa da ra'ayoyin masana dangane da ma’anarta. Sannan ya kawo ma’anar hikima da matsayinta a waƙa.Haka kuma ya bibiyi tarihin rayuwar makaɗa, Aliyu Ɗandawo a taƙaice.

Wannan aiki yana da alaƙa da wannan aikin, sai dai inda suka bambanta shi ne wanga aiki yana Magana ne akan salon kambamawa a wasu daga cikin waƙoƙin makaɗa kassu zurmi.

A wannan babi an yi bayani ne game da ayyukan da masana da sauran manazarta da suka gabatar a matakan ilimi daban-daban kundayen bincike da buggagun littatafai da muƙalu da aka gabatar, sannan aka yi bitarsu tare da bayyana dangantakarsu da wannan aiki.

2.1.3 MAƘALU

Masana da dama sun gabatar da maƙalu akan adabin baka wanda ya shafi waƙar baka.

Wannan aiki ya yi kama da wannan sai dai aikin yana magana ne akan salon kambamawa a cikin wasu waƙoƙin Kassu zurmi.

Gusau (2013) ya gabatar da maƙala mai taken "Dangantakar waƙoƙin baka da al’adun Hausawa; Bunƙasa ko koma baya" Wannan takarda cike take da ɗimbin bayanai akan al’adun Hausawa da matsayin waƙoƙin baka a wajensu, tare da misalan kaɗe-kaɗen Hausawa haka kuma, ya nuna irin bunƙasa da waɗannan waƙoƙi suka samu tun daga wancan lokaci har kawo yanzu, sannan kuma ya rufe takardar da kawo halaye da ɗabi’un waƙoƙi masu hikima da armashi waɗanda al’ummar Hausawa zasu amince.

Wannan aiki ya na da alaƙa da wannan sai dai inda suka bambanta shi ne wannan aiki yana Magana ne akan salon kambamawa a wasu daga cikin waƙoƙin Kassu zurmi.

Dunfawa (2005) A cikin takardarsa mai taken “ Zambo da Haibaici a cikin rubutattun wakokin addini” A cikin wannan mukala ya gabatar da kawo ma’anar zambo da ma’anar habaici, da halayen dan Adam,

Wannan aiki ya yi kama da wannan aikin domin duk muna Magana ne a kan adabi bangaren waka.Sai dai inda aikin ya sha banban shi ne shi yana Magana a kan rubutatcin adabi ni kuma ina Magana a kan adabin baka.

2.1.4  HUJJA CI GABA DA BINCIKE

Daga bitar ayyukan da aka yi a kundayen bincike, da buggaggun littafai, da maƙalu, babu wani aiki mai kama da wannan aiki kai tsaye, ta fuskar fito da salou kambamawa a waƙoƙin Kassu Zurmi, don haka binciken ya samu hujjar da za a   gudanar da shi.

 

2. 2 NAƊEWA

A wannan babi an yi ƙoƙarin kawo bitar ayukan da suka gabata, Bugaggun littattafai, kundayen bincike, maƙalu, Hujjar ci gaba da bincike duk a cikin babi na biyu.

 

BABI NA UKU

3.0 SHIMFIƊA

Wannan babi zai yi magana ne akan taƙaitaccen tarihin rayuwa Alhaji Kassu Zurmi. Wanda ya haɗa da bayani akan haihuwarsa da ƙurciyarsa, haɗi da neman iliminsa, da koyo da fara waƙarsa, da kuma gadon kiɗa da bayani akan abin kiɗansa, haɗi da  yaransa da salon kambama a cikin wasu wakoki Kassu zurmi.

3.1 TAƘAITACCEN TARIHIN RAYUWAR  KASSU ZURMI

   Magaji (2016) Ya ce Alhaji Kassu Zurmi sunan sa na yanka Abubakar an haife shi a wani gari da ake kira magarya ta ƙasar zurmi karamar hukumar Zurmi a jahar Zamfara ta yanzu nisan wannan gari lilo mita ashirin da hudu ne daga Zurmi, Kassu Zurmi ya zauna a kadawa Garin da nisan kamar kilo mita biyu kafin karasawa zuwa magarya wato mahaifarsa. Shi wannan garin wanda ake cema kwata kamar sabon gari ne, sunan mahaifin Kasu Zurmi Muhammadu mahaifiyarsa maimuna.

Kassu Zurmi

(Kassu Zurmi)

   Mahaifin Kassu Zurmi Muhammadu Ganga gadon farauta yayi, saboda haka Kassu zurmi gadon kiɗa ya yi bada rana tsaka ya fara ba ko da ya ke bai yi karatun zamani ba, amma Kassu Zurmi ya ɗan taɓa na alkur’ani tun kuwa lokacin da ya isa misalin mutum ne ya fara bin tsohonsa wurin kiɗin farauta. Allah maɗaukaki ya yi ma Kassu baiwa ta ya ya masu yawa a cikin manyan ‘ya’yansa akwai waɗanda suke tafiya tare shi wurin kiɗa. A ciki akwai Ummaru wanda a da ya yi kiɗin tauri wannan ya nuna a yanzu kassu Zurmi baya da mai gadonsa.

 

3.1.1. HAIHUWARSA DA KURUCIYARSA

Kamar yadda tarihi ya nuna Alhaji Kassu Zurmi dai mutumin garin Magarya ne kuma a nan ya yi har ya buɗe idanunsa. Sai daga baya ne da yai wayo ya koma a garin kadawa watau Kassu dai ko da ya tashi yana yaro hatsabibi ne a cikin tsaransa, domin ba da tsoro, kuma shi Kassu Zurmi mai kuzari ne kuma mai ƙarfi, saboda duk warinsa ba a samun mai buge shi a wajen faɗa.

Bugu da ƙari kuma Alhaji Kassu Zurmi lokacin da yake akan ƙuruciyarsa yaro ne mai kwarjini ga jama'ah tun daga yara abokanansa har zuwa manya. Saboda zaman Kassu Zurmi hatsabibi tun yana yaro yakan haɗa abokansa yara kokowa, yana zuga su. Kuma har takakka yake kaiwa abokansa a gidajensu (Dodo hari: juma'a 2021).

3.1.2  ILIMINSA

Kassu Zurmi bai samu yin karatun boko ba na zamani amma ya taɓa karatun Alƙur'ani. Kassu Zurmi ya yi karatunsa a wajen wani malami mai suna Ladan. Kuma a nan hannun malamin ya sauke alƙur'ani mai Girma sannan ya fara yin karatun littafai sai dai bai yi nisa ba, sai sha'anin kiɗa ya dauke masa hankali, inda yake tara yara samari yana yi masu kiɗa suna yin kokawa da junansu (Gusau 2005:225).

3.1.3 KOYO DA FARA WAƘARSA

Kassu Zurmi ya fara bin mahaifinsa wajen kiɗin farauta tun yana yaro ƙarami. Bayan koyon kiɗan farauta da yake yi daga wajen mahaifinsa, ya taɓa kiɗan noma, amma bai mayar da hankali sosai a kansa ba. Shi dai kiɗan farauta ya gada, ya tarar ubansa yana yi. Don haka ya himmatu a kansa, har Allah ya ba shi rabo mai yawa a ciki.

A matsayinsa na makaɗin farauta da yan tauri, bawai gidajensu kawai yake bi idan suna taron suna, ko biki ya kama ba, a'a tare da shi ake zuwa dajin farauta, duk abin da ake yi a farauta a gabansa ba wani mai bashi labari. Shi kansa a wasu  ɗiyan waƙoƙinsa ya nuna cewa da shi ake farauta dubi abin da yake cewa.

Tahiya madoka ko dajin kuna,

Ko waji yan kalangana na tashi an nan,

Sai da kai ake neman daji

(wakar garu-garu na maga),

(Gusau 2O05:225-226),

3.1.4 GADON KIƊANSA

Hausawa na cewa "Gado mala" Kassu Zurmi ya gaji kiɗin fawa a wajen mahaifinsa Amadu. Amadu makaɗin fawa ne, kuma yana kiɗan ‘yan bori. Daga baya sai ya koma yana yi wa mafarauta kiɗa. Saboda haka Kassu Zurmi ya gaji kiɗa ne a wajen mahaifinsa don haka waƙa a wajen Kassu gado ya yi ba haye ba, domin mahaifinsa ya yi.

3.1.5 ABIN KIƊANSA

Kamar yadda kowane makaɗi yake da abin kiɗansa haka shi ma Kassu Zurmi ba a bar shi a baya ba, yana da nasa abin kiɗan. Kayan kiɗan Kassu Zurmi su ne kalangu, kamar yadda muka sani, kalangu wani abin kiɗa ne da ake amfani da shi a wajen kiɗa. Kuma shi kalangu yana da baki biyu kuma ana buga shi da (kurya Maladi).

Shi dai kalangu wani ice ne da ake sassaƙawa masassaƙa kan sarrafashi a daji su kuma maidashi kalangu, kashi biyu ne akwai mazan kalangu, sune dake da sauti mai tsauri-tsauri kuma ƙanana ne basu yi girman wasu ba. Irin waɗannan kalangun ne Alhaji Kassu Zurmi, da sani Sabulu, da Ɗanba'u buwai suke amfani dasu.

3.1.6  YARAN  KASSU ZURMI

Bayan yaransa na tsatso yana da waɗansu yara waɗanda yake tare da su wajen gudanar da sana'arsa ta kiɗa da waƙa. Yaran Kassu Zurm na sana’ar kiɗa, sune kamar :

i.                   Dodo

ii.                 Tunau

iii.              Shata

iv.               Namakka

v.                 Ummaru ƙaho

Shi Shata dai yaron sa ne ta fuskar kiɗa, amma shi Dodo taubashin sa ne kuma abokinsa ne. Shi kuma Tunau zaman da yake ga Kassu Zurmi saboda kawunsa ne. Su kuma sauran ya'yansa ne na tsotso shi ya haife su.

 

3.1.7 NAU'O’IN WAƘOƘINSA

Kassu Zurmi ya yi nau'o’in kaɗe-kaɗe a matsayinsa na makaɗin kalangu. Daga cikinsu akwai.

1. Kiɗan Noma

2. Kiɗan Farauta Na'yan Tauri

3. Kiɗan Yan Caca

4. Kiɗan Barayi

5. Kiɗan Fawa.

3.1.8   IYALAN KASSU ZURMI

Kassu Zurmi ya yi aure kuma Allah ya arzurtashi da ‘ya’ya da yawa. Daga cikin ‘ya ‘yansa ne Ummaru ya zama makaɗin tauri kusan shi ne mai gadonsa.

Amma shi  Usman, ya zaɓi hanyar almajiranci inda ya yi karatun allo mai zurfi har ya zama malamin makarantar allo yana koyar da yara karatu (Gusau 2005:229). Kassu yana da "yaya goma sha biyu (12) da matan aure huɗu :

1.     ‘Yar jari

2.     Auta

3.     Abu

4.     Karɓa

3.1.9 RASUWAR KASSU ZURMI

Kassu Zurmi ya rasu bayan yayi fama da wata gajeruwar rashin lafiya wadda har ta sa kwantawa  a asibitin Gwaji na Gusau a shekara 1987 (Gusau,2005:229)

3.2  MA'ANAR SALO

Masana da dama sun tofa albarkacin bakinsu game da ma’anar salo. (Yahaya 2001). Ya ce salo dabara ce ko hanya mai yin kwalliya ga abu domin abin ya kwarzanta ko ya bayyana.

Salo yana nufin duk wata dabara ko hanya a cikin waka wadda aka bi domin isar da sako. Ita wannan dabara ko hanya ta yiwa waka kwalliya ta yadda sakon wakar zai isa ga mai sauraro ko mai karanta waƙar (Sarbi, 2007) cewa ya yi salo na nufin zaɓi cikin gudanar da wani abu ko alƙawari amma a fagen waƙa, salo hanya ce da marubuci ke bi wajen isar da saƙonsa ga jama’a.

Salo wata dabara ce ko hanya da marubuci ke bi wajen isar da saƙonsa ga makaranta cikin hikima da gwanintar harshe wajen isar da saƙo ga makaranci cikin hikima da azanci da nuna gwanintar harshe.

Salo dabara ce mai wahalar bayyanawa saboda salo ya bambanta tsakanin marubuta, ma'anar kowane mawaƙi da irin salon sa, haka kuma marubuci ɗaya na iya amfani da salo daban-daban dangane da sha’awarsa, lokaci ko yanayin daya samu kasan a ciki da kuma irin saƙon da yake son sadarwa ga jama’a.

(Ɗangambo, 2008) kamar yadda na nuna yana da wuyar a gane shi a bisa kansa, sai dai ana iya gane wasu sigogi nasa. Bisa jimla, muna iya cewa salo shi ne hanyoyi ko dabarun isar da saƙo.

A tawa fahimtar salo tamkar jini ne da tsokar kowane lamari saboda haka salo wani babban abu ne da mawaƙi zai bi domin ya nuna manufarsa zuwa ga masu saurare ko masu karantawa. Salo tamkar gishiri ne a cikin zance ko jawabi ko kuma waƙa, wanda idan babu shi zai sa abin ya zama bambarakwai kamar miyar da ba gishiri.

3.2. 1 IRE-IREN SALO

To zan kawo masanan da suka yi bayani akan iren-iren salo. Kamar yahaya (2001. 95)

3.2.2  MA'ANAR SALON KAMBAMAWA

Masana da manazarta da dama sun bada ma'anar salon kambamawa.

A ƙamusun Hausa (2006) .

Kambamawa ita ce idan mawaƙi ya yi zuƙu cikin magana ko ya ƙara mata gishiri a taƙaice ya bayyana abu fiye da yadda yake, a nan zamu ce wannan mawaƙi  ya yi amfani da salon kambamawa. (Yahaya, 2001:95). Idan muka tattara waƙoƙin soyayya zamu ga cewa mawallafa waɗannan waƙoƙin suna amfani da salon kambamawa ne. misali Muhammad Rabi'u saulawa ya ce da masoyiyarsa.

Wannan mata mai ƙyan sifa,

 Kin mamaye matan duniya.

(R.M Saulawa labarin zuciya)

Wannan mawaƙi ya yi kambamar zulaƙe,don ya bayyana masoyiyarsa ta fi dukkan matan duniya. Don haka ya yi kambamar zulaƙi.

3.2.3  IRE-IREN SALON KAMBAMAWA

Salon kambamawa hanya ce ta kambama abu fiye da yadda hankali zai amince akan yi amfani da wannan dabara domin waɗannan abubuwa kamar haka:

1. Kambamawar zulaƙe                              

2. Kambamawar yabo

3.3 NAƊEWA

A wannan babi an gabatar da taƙaitaccen tarihin rayuwar Kassu Zurmi tun daga haihuwarsa da kurciyarsa da neman iliminsa da fara waƙoƙinsa, wanda muke ce gado ya yi da abin kiɗansa da nau’oin waƙoƙinsa.Haka kuma an kawo yawon iyayensa da lokacin rasuwarsa. A dai wannan babi an ga ma’anar Salo da ire-irensa, har da Salon kambamawa wanda a kansa ake gudanar da wannan bincike.

BABI NA HUƊU

4.0 SHIMFIƊA

A wannan babi na huɗu za'a duba salon kambamawa a wasu waƙoƙin Kassu Zurmi. Sai kuma a kowa ma'anar salon kambamawa, hadi da kawo bayani akan ire-iren salon kambamawa, duk a cikin wannan babi na huɗu.

4.1 SALON KAMBAMAWA A WASU WAƘOƘIN KASSU ZURMI

Kassu Zurmi mawaƙan farauta ne da "yan tauri da kuma barayi, kamar yadda tarihi ya nuna. A cikin wasu wakokinsa yakan yi amfani da wannan salon na kambamawa domin ya zuga ko ya kambama gwarzayen sa, saboda su yi abin da ba su tashi yi ba. Ga misali  ire-iren kambamawa kamar haka.

4.1.1 KAMBAMAR ZULAƘE

Ita ce idan mawaƙa ya yi zuƙu cikin magana wato ya ƙara mata gishiri, a taƙaice ya bayyana abu fiye da yadda yake a haƙiƙani, za mu ce wannan mawaƙin ya yi amfani da kambamawa zulaƙi (Yahaya, 2001:95).

Kassu zurmi ya yi amfani da wannan salon a kambamar zulaƙe a cikin wasu ɗiyan waƙoƙinsa.

Bisa ga ƙa'ida bahaushe Allah kaɗai yake cewa maiduka, maibisa, maikomi, maikowa, idan aka yi amfani da ita ga wani bawa daga cikin bayinsa an yi kambamawa zulaƙi (Bunza, 2009).

4.1.1.1 waƙar Musa na ƙasar ɗan Ali mai Tauri.

Jagora         : Manyan hwaɗa,                                      

: Musa na kasar Dan Ali wan Karhi

   Wannan kalma ta wanƙarhi kambamawa zulaƙe ce, saboda karhi bai da wa.

4.1.1.2  Waƙar Ummaru Sabon Birni.

Jagora :Daɗi na da Gobirawa,

:Du in da kunka zo ba ku hukuntuwa.

 A nan ana nuna isa ga gobirawa, amma kalma hukunci ba bu wanda ya wuce hukunci, A nan an yi kambamar zulaƙe.

4.1.1.3 Waƙar Ɗanjijji.

Jagora : Mazan jiran maza Ɗanjijji ɗanguru,

:Shiriritad duniya na bayan tanda,

:Ibilishim masussuki Ɗanjijji,

:Da kai ne mai koda nag gani tar rude.

  An yi amfani da wannan salon a kambamar zulaƙe wajen shiriritad duniya na bayan tanda. Wannan kowa yasan bayan tanda baki ne kawai a nan an yi kambamar zulaƙe.

   Kalmar ibilishi masussukin Danjimma wannan kalma ta nuna cewa shaidan ko aljani a nan an yi kambamar zulaƙe.

4.1.2 KAMBAMAR YABO

Dabara ce ta jawo hankali fiye da kima. Hanya ce ta kambamawa abu fiye da yadda hankali zai amince. A kan ya amfani da wannan dabara, musamman domin yin yabo. Ana nuna cewa mutum ya yi wani abu, wanda a zahiri ba zai yiwu ba, ko ya mallaki wani abu da zai iya mallaka ba. (Sarbi, 2007).

4.1.2.1           Waƙar Baƙo Na Ɗanƙaya

Jagora : Buwai mai raba gardama ga mazaje,

               : Anne baƙo na malam mai takobi

Wannan kalma ta ‘Anne’ tana nufin Taurarewar zuciya a nan Kassu ya Kambamashi da wannan kalma ta mai taurin zuciya mai ƙwazo a nan an yi kambamar yabo.

Jagora :  :Baƙo na danƙaya na Buwai,

              : Damusheren Gandau na Buwai,

              : Daji Baƙo na Mallam mai takobi

              : Anne gidan ku babu Muhammad,

              : Gidan su ba mai suna ragoranci.

Wannan kalma ta ‘Damushere’ tana nufin gawurtatce an yi kambamar yabo.

Ma’anar kalmar Damushere

                   I.            Mutum mai aiki tuƙuru

                II.            Mafaɗacin mutum

             III.            Mutumin da yake son abi umurnin da ya bayar nan take ba da inda-inda ba

            IV.            Daidai da damisa

Ƙamus Hausa,2006 :92-93

4.1.2.2 Waƙar Nomau na Magarya

Jagora: Dan kalgo bani kar na ƙarye,

            : Wa ka sai mani doki magarya?

            : Nomau ne ko abin tuwo ba ya dashi,

            : Kahiri karen bunu Baƙo,      

            : Yanzu kau karen Alhaji ne.

A cikin wani ɗan waƙar ana nuna cewa Kassu Zurmi ya yi amfani da kambamar yabo inda yake yabon gurzunsa da kalmar kahiri.

          Ma’ana kalmar kahiri a addinance tana nufin wanda bai da addini, A kuma wani ƙauli tana nufin mai ƙarfin zuciya, anan Kassu Zurmi ya yi amfani da kambar yabo.

4.1.2.3 Waƙar Shaye Ɗan gida Labbo

Jagora: Kata koro Lado Iro na Ummaru,

            : Kura mai guzurin kunye.

A wannan ɗan waƙar ana nuna cewa anyi kambamar yabo, Ma’anar katakoro yana nufin mai ƙarfin gaske / ƙaton mutum.

4.1.2.4 Waƙar Rabi’u Ɗan Manyan Matcata

Jagora: A’a Rabi’u ka kyauta ma Kassu,

            : Rabi’u ka kyauta ma Kassu,

            : Mai dala’ilu ɗan manyan matcata.

A cikin wannan ɗan waƙa anyi amfani da kambamar yabo idan aka gwarzanta shi da kalmar Dala’ilu, ma’anar wannan kalma wato mai dala’ilu yana nufin mai tsananin wuridi ga ubangijin halittu.

Jagora: Ya san mu tare da tsoho nai,

            : Ko da ya yam mutu shidai bai saki ba,

            : Rabi’u dan manya makata,

            : Dan manyan kasake

            : Rabe dutsin hwashin tama,

            : Rabi’u zakka a won maza ɗan maidamma na kande.

A cikin wannan jigon anyi amfani da kambamawar yabo, inda ake kambama shi da kalmar Dutcin hwashin tama, anan ana nufin gwarzon jarumi a wajen faɗa.

          Sai kuma a waje ɗaya inda ake kambama shi da kalmar zakka awon maza, wannan kalma na nufin wato shi Rabi’u, Rabiu sikeli na auna mazaje, wato shi ne abin ƙwatance saboda jaruntaka.

4.1.2.5 Waƙar Mai Barbara Shehu Guraguri

In da yake cewa a cikin dan waƙarsa.

Jagora: Tauri wuya garai sai a yi ƙoƙari,

            : A sha malammai a bi sayyu a yi kariya,

            : In an ƙiya ana cim ma sanin wani,

            : Sai ya gamu in yi wai,

            : Da ni da wane sai mun gamu kassuwa,

            : Amma ina gida ina tad da zuge-zugi,

            : Kun yi kalan goni suna hwaɗin wani ya kashe wani.

Kalmar taurin wuya tana nufin gwarzo mai jarumta.A nan  an yi kambamar yabo in da ake kambama shi da Taurin wuya, wato jarumi, mai gwarzantaka.

Kalmar taurin wuya tana nufin gwarzo mai jarumta.

4.1.2.6 Waƙar Musa na Ƙasar Ɗan Ali mai Tauri

Jagora: Ɗan Mande ban ga jinin ka ba,

                              : Ɗan Mande mai taurin jiki,

                                : Ɗan Mande na gode,

  : Ka bani kuɗi,  

 : Kuma ka bani dawaki,

 : Ka koma ka sa man riguna,

  : Na gode baura,

: ka sun kuɗa mani kuɗɗi ɗan maliki,

  : Kassu kuma riguna sai na gaji

  : ka sai mani doki,

: ka koma ka sa man riguna,

 : Allah dai shi ƙara maka arziki,      

: Baura Allah dai shi ƙara ka amin don Kassu,

: Allah dai shi ƙara maka arziki,

  : Baura Allah dai shi ƙara ka amin don Kassu.   

Wannan ɗiyan waƙa an nuna anyi kambamar yabo, in da aka ce Taurin jiki na nuna ƙarfin hali, ko jauriya.

Ya ci gaba da cewa:

Jagora: Gagare daga karen ido,

     : Karen ido mai karhin gaba.

Wannan kalma ta Gagare’kalma ce ta laƙabi da ake yi wa mai suna Abubakar tana kuma nufin jarumi. Don haka kambamar yabo ce. 

4.1.2.7 Waƙar Ummaru Sabon Birni

Jagora: Ko can in kaji gatari sai buzu,

            : Yara ko can don hwaɗa aka tsoron zuwa gidan

    jangwarzo,

            : Don hwaɗa aka tsoron zuwa gidan jangwarzo.

Anan an nuna anyi kambamar yabo domin kalmar Jangwarzo tana nufin majiyin ƙarfi, jarumi.

Duk a cikin wannan waƙar an cigaba da kambamar yabo a dubi wannan ɗan waƙa na gaba.

Jagora: Hana noma na hanƙurau,

: Sa’adu mai hana noma na hanƙurau,

  : Sa’adu barkakka da yamutsi,

 : Sarkin karman Gobir arnan Sabon birni.

A cikin wannan ɗan an yi amfani da kambamar yabo, inda ake kawo kalaman hanƙurau, wannan kalma ta na nufin mai tsananin hanƙuri ne.

Jagora: Sabon birni gidan Bawa jangwarzo,

 : In da masu yaƙi suke gurzuwa,

Kalmar gurzuwa tana nufin haɗuwar mazaje a wurin yaƙi yadda kowa zai ji jiki.

4.1.2.8 Waƙar Mani Na Maƙera.

Jagora: Ya gagari gaba Mani,

            : Ya gagari gaba Mani,

            : Kai ne maƙera gudu sai mata,

            : Kai ne maƙera gudu sai mata.

A cikin wannan baiti an nuna kambamawar yabo domin kalmar gagara tana nufin buwaye wato wanda yafi ƙarfin kowa ke nan.

Jagora: Wo jikan zaki,

            : A jan zaki ba a haye ma barde,

            : Im ba maganab banza ba,

            : Mani bay yi idon tsoro ba,   

            : ko kusa ba shi da tsoron kowa,

            : Halin gidan jimfi kay yi jikan zaki,

Ma’anar wannan kalma ta  “Jikan Zaki” zaki dabbar daji ce, yafi kowace dabba karfi, Kassu yana yabon gwarzonsa da wannan kalma don  ya nuna gadon ƙarfi ya yi don haka ya ce masa “Jikan zaki” barewa kuwa ba ta yin gudu danta yay i rarrafe kamar yadda Dankwairo yake cewa.

Jagora :Danbajimi, bajime ne,

                             :Dan giwa, giwa ne,

                             :Dan giwa, giwa ne,

Kai tsaye Jikan zaaki ya nuna shi ma zaki ne

       Jagora    : Barkaka da gaba mani,

:Toho jikan zaki bari tsoron arna,

:Hude-Huda na makera ina ban kwana,

:Bari dai rena ma kiran mani ba,

:Da niz zo wadda akai dayayyi mai,

:Zaman ɗaki da kaho to yai man.

  Huda-Huda tsuntsu ne kyawawa mai kama da hazbiya da ɗan tukku a kan sa. Wasu na kiran sa alhuda-huda an bayar da labarinsa a ƙissar Annabi Suleiman a matsayin mai ilimi wanda ya kawo masa labarin sarauniya Balkisu da gadon mulkinta. A kasar Hausa idan a na son a nuna mutum mai son karatu sai a dan gan ta shi da wannan tsuntsun.

   Kassu Zurmi yasan haka wanda ya kira da sunan ko yana nufin mai ilimi ne ko kuma saboda kyawonsa da kyawon shigar sa.

4.2 NAƊEWA

A Wannan babi na huɗu an yi ƙoƙarin bayyana waɗansu abubuwa waɗanda suka shafi wannan babi. Sun haɗa da shimfiɗa, salon kambamawa a wasu waƙoƙin kassu zurmi kambamar zulaƙe, kambamar yabo.Duk a cikin wannan babi.

 

 

 

 

 

 

 

 

BABI NA BIYAR

5.0 SHIMFIƊA

A cikin wannan babi an kawo bayanai a taƙaice dangane da wannan bincike da aka gabatar, sai kuma sakamakon da binciken ya gano.

5.1 SAKAMAKON BINCIKE

Sakamakon wannan bincike ko nazari dangane da abubuwan da ake yi kiciƃis dasu, an fahimci cewa makaɗin Kassu Zurmi mutum ne mai hazaƙa da basira da kuma hikima da azanci wajen ƙulla ɗiyan waƙa.

Haka kuma wannan bincike ya gano Kassu Zurmi mutumin Magarya ne ta ƙasar Zurmi ta Jahar Zamfara. Har illa yau kuma wannan nazari ya gano cewa Kassu Zurmi makaɗi ne mai amfani da kalmomin kambamawa, da kururutawa,da kuma yabo, da zuga.

5.2 SHAWARWARI

Hausawa na cewa “shawara ɗaukar daƙi. Ina bada shawara ga duk wanda zai karanta wannan bincike don wani nazari ko don wani abu daban ya lura da aikin da aka yi a kan salo, musamman salon kambamawa a cikin wasu waƙoƙin shahararre mawaƙin nan watau Alhaji Kassu Zurmi. Domin ya gano abin da mawaƙin ke nufi.

Ina kuma bada shawara ga dalibbai masu nazarin harshen Hausa da cewa su ɗauka in da na aje. Musamman dangane da aiki irin wannan, wanda ya shafi adabin baka.

Wata shawara kuma da nake son in bayar a nan shi ne ɗalibai da sauran al'umma su karanta wannan kundin bincike domin gano fasahar da mawaƙin  ya yi amfani da ita a cikin waƙoƙin nasa.

Daga ƙarshe ina bada shawara da cewa a ci gaba da rubuce-rubuce a kan nazari waƙoƙin baka na makaɗa saboda kada su salwanta, domin sun  kamo hanyar ɓacewa.

5.3 NAƊEWA

Wannan bincike ko nazari gaba ɗaya tun daga farko har ƙarshe an gabatar da shi ne a kan salon kambamawa a cikin wasu waƙoƙin Kassu Zurmi.

A babi na farko an kawo shimfiɗa da manufar bincike, da farfajiyar gudanar da bincike, da hanyoyin bincike, matsalolin da suka shafi gudanar da binciken, da kuma hassashen bincike.

Sai babi na biyu, an yi waywaye ga wasu ayukan da suka gabata makamantan wannan aiki da suka haɗa da bugaggun littattafai, da kundayen bincike da muƙalu. An kuma yi bayani hujar ci gaba da wannan bincike.

A babi na uku na kawo bayani kan tarihin Kassu Zurmi, da kuma ma’anar salo, ire-iren salo da ma’anar salo kambamawa haɗi da kawo ire-iren salon kambamawa.

Sai babi na huɗu wanda shi ne ƙashin bayan binciken in da nayi bayanin salon kambamawa a ciki wasu waƙoƙin kassu zurmi, haɗi da bayanai akan kambamar zulaƙe, da kambamar yabo.

Daga ƙarshe a babi na biyar wanda kuma shi ne na ƙarshe na kawo shimfiɗa, da sakamakon bincike da shawarwari haɗi da kawo manazarta duk a cikin wannan babi na biyar, wanda shi ne na ƙarshe a cikin wannan kundin binciken. Sannan da ratayen waɗansu waƙoƙin Kassu Zurmi.

MANAZARTA

Ammani, M. (2009) “ Nazarin Maganganun Hikima a Waƙoƙin Aliyu Ɗan

               Dawo” Kundin digiri na biyu. Sashen Koyar da Harsunan   Najeriya. Kano. Jami’ar Bayero.

 

Bunguɗu,I. (1990), “Muhammad Auwal, Isah Bunguɗu, da waƙoƙinsa”

                  Kundin digiri na ɗaya. Sashe koyar da Harsunan Najeriya. Kano: Jami’ar Bayero.         

 

Bunza, A.M (2009) Narambaɗa Lagos: Ibrash Islamic Publication center

Limited.

 

Dangambo, A (2007) Daurayar Gadon Fede Waƙa. Kano Amana Publishers.

 

Dumfawa,A.A (2005) Zambo da Habaici A cikin rubutattun waƙoƙin Addini. Sokoto.Sashen Harsunan Nijeria.Jami’ar Usmanu Danfodiyo.

 

Gusau, S.M (2005) Makaɗa da Mawaƙan Hausa, Kano: Benchmark    Publishers Limited.

 

Gusau, S.M (2013) Dangantakar Waƙoƙin Baka da Al’adun Hausawa:

Bunƙasa Ko Koma-Baya sashen koyar da harsunan Najeriya.  

Kano.

Magaji,A. (2016) Kassu Zurmi da Waƙoƙinsa. Publish By Spectrum Books

Limited Spectrum House Ring Road Ibadan.

 

Sarbi, S.A (2007) Nazarin Waƙa Hausa. Kano: Samarib Publisher Limited.

 

Yahaya, A.B (2021) Salo Asirin Waƙa Kaduna Media Service.

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

Rataye Na Daya

Wasu Wakokin Kassu Zurmi Na Tauri

Shayi dan Gidan Labbo

Jagora: Mai kwana ya tashi,

: Mai tahiya ko ya dakata shi kau:

: Ku tashi kun ji kidin Shayi dan gidan Labbo.

 

Jagora: Ku hwalka na Kai ga masu dongashi,

: Lalle Shaya ad da ɗangashi

: Ya yi bida amre bara sai da yas samu,

: lro ya kar ta gidan niaigidansu yah hwaɗi,

: Yam mutu yab bas shi ba abin amren.

: Kana ba hatcin diba.

 

Jagora : Da an game da Labbo yana tattalin diyan dangi.

 : To dada ya amren Sha, Labbo ya wahala,

: Ra amren Sha, Labbo yai yawo,Yai yawo,

: Amren shaya, Labbo ya yi jidaɗi.

Jagora : Garin biɗad bashi.      

: Ya sha raba kamak Karch dajl.

: Ya sha rana kamat tukin daki,

: Labbo ya tawaiwaye walki shina ginah hanya,

: Maidabo dan aula za ya ba shi yah hwasa.

 

Jagora : Irin gidan Bawa dan Galadima,

: Sai da Bawa yab ba shi sai ladar takkwace,

: Tac ce sabilin Shaya ba a bashe su,

: Dan nema bai raganma kowa ba,

: Wata yag gona garai cikin tabki,

: Bara yat tashi yana Kashin awakinmu,

: Tac ce masalin mai kato gudan awa Shayi,

: An nan ka bidab bashi.

 

Jagora : Labbo yac ce katon gidan na-banza ne.

: Komi yab bida na mata ne

: Dum mata sun bi Iro sun kode,

: Yakkamnatai tana yi mar wazu,

: Yakkamnatai tana yi mai wazu,

: La anannen ba ya jin batun kamnai.

: La'anannen ba ya jin ba

: Tana hwadin,

: Tana hwadShayi ga ka dai da karhin, Shayi ga ka dai danka,

: Na Abu hak ka lalace tsohuwa ta cishe ka.

: Na Abu hak ka lalace ts

 

Jagora : ta Dangiwa Hauwa na yi mai bida

: Ba ta da karhi ba ta biyak kuyya,

: ‘yat tahwasa taka diba a ba ta sadare,

: Ta kau ci hat ta cishe shi,

: Taro kun san ko hauwa uba naice.

 

Jagora : Katakoron Lando, Iro na ummaru

: kura mai guzurin kunya

: Sha-yaya Magarya ta yi ma doro

: Tana nan ta bar ka, Atu ta tsere.

: Dauri an bar ma ka tsohuwa ta cishe ka,

: Tsohuwag ga ta fuzge

: To dada Sha wa ka cishe ka?

 

Jagora : Kakab bana tai kyawo

: Ko ta bara mun gode,

: Sai dai Shaya bai yi komi ba.

: Na ga yan tantabaru cikin rihewassu,

: Tantabara goma,

: Amma yanzu ba su sun kare,

: Yanzu kam saura nai guda baki namiji,

: Ko shi kam dan yana yi mai waka,

: Inda sahiya taw waye ya dora mabanci.

 

Jagora: Tantabari na rigan ka tasowa,

: Kai  ga Ka da ranak Kwana sai luhwa ta shuɗe,

: Sai tsuntsu ya hiko yana sijan hantci,

: Yana gashin keya,

: Shina dubin inda za ka hudowa,

: Shi kau yana cikin dakı,

: Tantabari na gyaran jiki nai.

 

Jagora : Sai da Shaya yaɗɗago daki,

: Dam mazan tantabaringa na yi mai guda,

: Shina kudunguru Shayi dan gidan Labbo,

: Kudunguru Shayi dan gidan Labbo,

: Kudunguru Shayi dan gjdan Labbo,

: Shi ko kokirzon

: Shi ko kokirzonsai ya watsa ‘yas tsaba sai ya watsa yas tsaba,

: Kai ko tsuntsu teintce tciyakku ta bi ku.

: Kai ko tsuntsu tcentce tciyaku tabi ku

 

Jagora : Ya'ya an nan dubu kamas Shayi,

: Babu kayan turawa ruhewakku

: Tai kyawo

: Rannan Shaya yas Shigo sa'a

: Ga ya da dogon baki da yaw wutab bota,

: Na Abu yankan bakinka ya yi ma kyawo,

: Ya samu gama aron zanen saki,

: Had da tsamiya yaddauro da yab bakas shadda.

 

Jagora : ‘Yammata sun gane shi sun je mai.

: Anka dora wasoso,

: Ni wanin Shayi ni ka jide shi,

: A a kina karya na riga ki zado shi.

: Kamas su buga gasu nan cikin gebe

: Na ce kak ku buga ya ishe ku jidawwa.

 

Jagora: Daukash Sha-yaya munka sha daula,

: Mun sha damnalutsa mun sha mai,

: Mun sha zabbi ga dan gidan Labbo,

: Nicce ma yan yarana, ku sha ahaha ce,

: Tunda ba ya maishe ta.

 

Jagora : Katakoron Lando, Iro na Ummaru,

: Kura mai guzurin kunya

 

Jagora: Sai da za mu watcikkewa,

: Kana uwayen matanga sunka jawo ni,

: ga ni ga yammatanga ga uwayensu

: Mu kadai cikin zaure

: Kassu amana Allah ka ba mu labari,

: Nic ce, Wane labari.

:  Labarin Shayı dan gidan Labbo,

: Yammata sun walwale baikonsu,

: Sun ce Shaya Shi Ka rankonsu,

: Shi muka son ka ba mu labari,

: in akwai gidan Kirki

: Nic ce yau kam dattijo kunka maishe ni,

: Ya yi, ku koma ku shaida na Abu dan uwana ne,

: Mutum kau ba ya shidaddan 'uwanshi ko hwada

 

Jagora: Kassu amana Allah ka ba mu labari,

: Ni kau amana Allah kadai ka sha min kai,

: In na bi amana Allanga na yi batanci,

: Kuma in tuna ba ni Cin amana Allah sabadda tantiri.

: Amma hwa ku ba shi in kuna bashi,

: Na-Abu Shayidai da ne,

: Sunka ce "Ba haka munka so ba dan yaro,

: Aimun san da ne tunda anka haihe shi,

: Ba mu labari in akwai gidan kirki?

 

Jagora: Ni ce, I gaskiyakka dattijo

: Mutum kau ba za ya kai diya tai ba

: Gidan da ba abin kirki

;Amma hwa ku ba shi in kuna ba shi

: Sai diyad dattijai kadai ka amren

: Sha-yaya dan gidan Labbo, na Abu

: Tunda kowa amre shi ita ka cishe shi

: Ta biya kudin garin karen kyasko

: Sannan ta yi mai abin ruhwa

: Kana ta koma ta yi dabbalin abin damri.

 

Jagora: Dattiyo yat tashi : Yab buge riga yai cikin zaure.

 

Nomau na Magarya

Jagora : Nomau tushen hwada karem masu gari,

: Toronkawan tciya uban Mairogo,

: ko hwatara tai yawa takan zam iko,

: Nomau ko ba ka jin batun masu gari.

 

Jagora : Na Magaji kankari ba ka jika,

: gaude ba ka matanki,

: Baba kade ba ka baka,

: Nomau tushen hwada karem masu gari

 

Jagora: Gagarabadau ubangidan yaj Jimmau,

: Da Kassu barka da tciya,

: Banawa kyawon hwada a yo accakwama,

: Baba a wo ta bakikkirin ta kare maku can,

Na Magaji in ga ham magabata, Suna hawa za a bida.

 

 

 

Jagora : Nai tambaya cikin ‘yan tauri

: Taro na tambaya ga manyam makada

: Wa anka ba doki da gangami ba ni ba?

 

Jagora: Doki da gangami sai Nomau na Magarya

: Uban Balindo shi ya she ni hak Kadawa

: Yac ce "Kassu ana bidak kada doki

: Ga ka kana alhwarma.

 

Jagora: Dan kalgo ba ni kamnak karya

: Wa ka sai mani doki Magarya

: Nomau ne ko abin tuwo ba ya da shi,

: Kahiri karen Bunu Bako,

: Yanzu kau karen Alhaji ne.

 

Jagora: Yac ce da tarbace Za a saye.

: Niko ga ni da son doki,

: Sai nij ja turayena,

: Nit tasam ma Magarya,

: Niddora"Magarya shin ina alkawali?

: Magarya shin ina alkawali?

: Jama a ashe ba wanda yaj ji yag gani,

: Karya ce.

: Ta shani waka banza.

 

Jagora : Nizzo nic ce Saraki doki nika so,

: Ku Kau nac ce da tarbace za Ku saye,

: Yac ce la-la-la babu ruwana,

: Kassu in dan ni ko anini nau ba ya shiga,

: Nomau dai ba ya rage ma kowa Magarya,

: Sannan wani ba ya sa shi aiki shi tahi.

 

Jagora :Nic ce Allah waddan karhin Nomau,

: Mi karhinka yad dada na Magarya?

 

Jagora: Ni na baz zuwa gida ba ka yi shi ba.

: Baba in da sata ka kai, yi satak ka saye,

: In kau ka ga ba ka sata yi hwashe,

: Amma na baz zuwa gida ba ni da shi,

: In kau na isa gidan, bilai ya kasan,

: Sai La'ilaha illa lahu,

: Dada Kassu ya yi rantsuwak kahhwara.

 

Jagora : Nomau yaz zo yac ce,

: Saraki ka ga shi doki,

: Sabad da shi za ni hwashe,

: Shegen dai ya shige gida, ya ki hita,

: To hak kajuya yi rantsuwa ka ta kasa

: Saraki yac ce, "Mis sha muna kai,

: In dom mu ka tashi ko yanzu ka je.

 

Jagora: Sai ga Nomau ana ta gyaran layu,

: Da kambuna za a hwashe,

: Nic ce "In da sabad da ni,

: Ba ka hwashe na Magarya,

: Bari in ba ka shawara,

: Inkab bi ta gobe dokin aka yi

: Magarya, ko ba a da shi".

 

Jagora: Ba mai gina Magarya sai ta ruhewa,

: Dug gidan kara na,

:Amsad doki gidan kara mina na ga matcaci.

: Jagora Bari sai gobe da swahe,

: Iskan nan ta taso,

: Wanga na shikag gujiya,

: Mai kwasas sansami yana gamawa da Kasa,

: Ya faffako kar-kar-kar,

: sannan ebo wula ga ragga ka hita,: Sannan ebo wuta ga ragga ka

  hita

: koma daz zuwa gidan Dan-Aljanna, Koma daz Zuwa gidan Da

: Hwalka yab bura uba-sai daji,

: Na Magaji rantsuwa ka ta kasan,

: Gama da yan kashin wuta, za ni hita

: Yac ce Kassu shawarakka ita za hi biya,

: Baba in kau kab bi ta,

: Gobe dokin aka yi Magarya ko ba ada shi.

: Dakanta ka jiya Nomau,

: Yac ce Kai ba in Jiya Da,

: Jab bura uba,

: Ba ni kamnak kowa Magarya,

: Duk ku rabu da ni.

: Ina biye ni kau ina y mai mabanci,

: Ina hwadin in dai ba a sonka,

: Tungak ka hita,

: In dai ba Su sonka,

: Tungak ka hita.

 

Jagora : Yac ce, Ina hita Mai-Kassuwa,

: Amma hwa ba da alheri ba,

: Bari ko an hana ni yanzu dd rana,

 

: Sai iskan sha diyun dare ya taso,

: Sannan za ni kunna yab bura uba,

: Magarya Sannan wada ko diyansu wasu ba su hita.

 

Jagora: Gaude ba ka matanki,

: Baba kade ba ka baka,

: Na Magaji kankari, Ko Allahu na ruwa ba ka jika,

: Dakokiso ko ba ka jin batun masu gar?

: Ba ka ya da cukurhwa ba,

: Ba ka ya da taimakon yaki da,

: Bunu ko Kudin gari a shahwa su hita,

: Nomau in am matce ka ce ba ka da su,

: Ban ga abin da za su diba ba garai

 

Jagora: Sannan Magaji yac ce,

: Assha Saraki dattijo da kai,

: Shin kaka kwabo guda ka lalata gart,

: Kwabo guda mina ne Magarya

 

Jagora: Ba dai doki ba na tauri,

: Ko mota munka so saye ba mu saye?

: To iyakan Nomau hwa an nan.

 

Jagora: In yak kau mu yab baro,

: Ban ga abin da za ka diba ba garai

: Wandara sai dai a koshi damri a sakat

: Nomau sai a koshi dibaw.wa adi,

 

Jagora: Torankawan teiya uban Mairogo

: Ko hwatara tai yawa takan zam iko

:A'a Nomau ko ba ka jin batun masu gari?

: Rabi'u dan Manyan Matcata

 

Jagora: Ba lahiya Rabi'u ka saba da yaya

: Rabe dutcin hwashin tama lam Majdamma matcaci,

: Wadda kai mani ka kyaula mia Kassu.

 

Jagora: Na gode ma Rabe zaki dan Musa mai takobi,

: Im ma Rabi'u kidi ya tashi ya karo kau-da-bara,

: Wadda ubanai nah hwada ma1.

 

Jagora Mutuwa na da magani dan Musa,

: Rabe gidanka ka ga abina bal bace ba.

 

Jagora :Rawaiya ba ta ratsuwa ai stina,

: Maidamma bai sake ba,

: Rabi'u da nai ka ka yadda,

: Doki ukku kay yi man dan Musa,

: Take-take kowane sau nai bai bace ba,

: Doki ukku kay yi man dan Musa,

: Nomau take-take kowane sau nai bai bace ba.

 

Jagora : A a Rabi'u ka kyauta ma Kassu,

: Rabi'u ka kyauta ma kassu,

: Mai dala'ilu dân manyan matcata.

 

Jagora :Sannu da hwama na Rakkiya nal Ha'u,

: Na Rakiya na Ba'u,

: Kahiri na yab bulala,

: Koway yi gum da Rabi'u banza na kashi nai.

 

Jagora : Na san hwada ga rai dan Musa,

: Bana kowai karo da Rabi'u ya kaskanta kai bai.

 

Jagora : Na gode ma Rabe,

: Alhaji Mahammadu na gode da kyaula,

: Sarkin Tasha Mahammadu na gode da Kyauta,

: Abdu na mai doki wadda kai mant ka kyauta makassu

: Sabadda Rabi'u dan manyan matcata.

 

Jagora :Doki ukku kay yi man dan Musa,

: Duk dore-dore kowane sau nai bai bace ba.

 

Jagora : Kyautaddan Maidamma mai ganin kwanji dub baya yin ta,

: A ba ka ka amso fan talatin,

: Kuma gobe shi baka ka ka hwai sai fan talatin,

: Kuma jibi shi ba ka hwai sai fan talatin,

: Rabi'u ya kyauta ma Kassu,

: Mai da Yas Sababai Allah ka so nai.

 

 

 

Jagora :Na san in Allah ya saukawa ma Rabi'u mota.

 

Jagora: Ya sam mu tare da tsoho nai,

: Ko da yam mutu shi dai bai saki ba,

: Rabi'u dan manyam matcata

: Dan manyan kasake,

: Rabi'u dan manyan matcata,

: Rabe dutcin hwashin tama,

: Rabi u zakka awon maza dan Maidamma matcaci.

 

Jagora : Dutcin hwashin tama dan Musa,Saoues StA a Dung

:Rabi'u zakka awon maza dan Maidamma na Kande.

 

Jagora : Maibabarbara Shehu Guraguri,

:A'a kluna bargazak kalangui ku rage wuta,

: Ku kashe wuta,

: Kuna hwa Jin kidin lad da hayaniya,

: Banawa ko ba ku Jin kalangan karayyaw wuka,

: Kuna jin batutuwan tad da hayaniya.

 

Jagora : Tauri wuya ga rai sai ayi kokari.

: A sha malammai a ebi sayyu a yi kariya,

: in an kiya a cinma sanin wani,

: ina ruwanmu ba ni Ka gama ku ba,

: Tunda Kuna wurin hwada goma ina gidanmu,

: Sai ya gamu in ji wai,

: Da ni da wane sai mun gamu kassuwa,

: Amma ina gida ina tad da zuga-zugi,

: Kun ji kalangai suna hwadin wani ya kashe wani

 

Jagora: Bimin Magaji ba su furguria Kassu ba,

: Aa ba su rena kidinga ba,

: inna zo arinsu sai Sui mani kokari,

: Im mun gamu kassuwa suna ba ni na shan hura,

: Sule uku sule hudu,

: Kana su ce sabka lahiya suna gai da wadan gida,

: Mai babarbara Shehu Guraguri,

: Kun ji kidin shehu masu banna da ido wuri.

 

Jagora :Rat tariyat Firimiya an bidi yamutci K.aura,

: Ranat taryat Firmiya an piat anc,

: sai ga magaji ya dora gadauniya

 

Jagora :Mai babarbara Shehu Guraguri na Musa,

: Ka biya ni ba ka shanye kidin ga ba,

: Dada mahaukaci ya tsare unguwa,

: Amma dai ka na hwakewa da hayaniya ta, -

: Wa bai san kai ne ba ne Musa,

: Shehu masu banna da ido wuri

 

Jagora :Ba a san kai ne ba na Musa,

: Kassu abin da za a yi dufa yi in gani,

: Kassu abin da za a yi du'a yi in gani,

: Amma kuma ba ni Son ana tad da hwada gida,

: Don kada mu tara wasu ku yi yamutci,

: Ku dai sassabta: Ku dai sassabomu samu jallin tahiya gid mu samu jallin

tahiya gida.

: Mai babarb:  Mai babarbara Shehu guraguri na Mra Shehu guraguri na

  Musa.

: Ka biya ni ba ka shanye kidin ga ba,

: Ka ji kidin Shehu masu banna da ido wuri.

 

Jagora : Wasa an yi an gama sai tahiya gida,

: Barau na Bawa yas so tahiya gida,

: Niy yi rakkiya nik Koma ciki,

: Yan Gangare sun zo tahiya gida,

: Kassu ni yi rakkiya nik koma ciki,

: Ina dao Birnim Magaji ban tashi barin ta ba,

: Mani na garinmu yas so tahiya gida,

: Kuma niy yi rakkiya nik koma ciki,

: Ina nan Bimim Magaji ban tashi barin ta ba,

: In kun zo ku ce muna gai da wadan gida,

: Sai mun biya mu dan nan mu yi kan wani,

: Daga Gidam Kaso, Kassu ya yi Cgama,

: In dan dai shamusalli ban tashi zuwanta ba,

: Na wuce Sai dai badi in tano,

: Ina gidan Shehu mata tai na tuwo tana ba my kare- kari,

: Saura a y kassuwa,

: In dai don ubangidan ba a daka ciki.

 

Jagora : Ba a san kai ne ba na Musa

: Shehu masu banna da ido wuri.

: Yara kuna jin ina hwadin Shehu Guragur

: Yara kuna jin irin kidin Shehu Guraguri.

 

Alhaji Isa Nakatuka

Jagora : katuka karhwandamin kare mai kashe kura,

: Mahaukaci na kohur hana noma na Mairo,

: Taho da shirin gaba dan Haruna dan mai hana nonma.

 

Jagora : Kai mutane in dai mutum Huntuwa yaz zo,

: In dai Huntuwa kaz zo,

: In dai ba ka bidi gidan masu gari ba,

: Ba 'yan maza kama Alhaji Isa,

: Wadanda Sunka hali aka zo su ne Delu,

: Na Katuka karhwandamin kare mai kashe kura,

: Mahaukaci na Kofur nana noma,

: Taho da Shirin gabl dan Haruna,

: Dam mai hana noma na Kande

 

Jagora : Kai ubangidan shanu da Gaybu

: Na Delu albarkacinka nis sabu da Ciambu

: Kuma niss Sabu da Snata nay yay yi man kujerah Hajiniz zo

: Doki ba a san ka hwasa daukal lihidi ba

 

: Arziki bu nga na da Ko a zwage ma mutun shi

: Ba ka gudun gaba dan Huruna dam mai hana noma na Delu

: Ba ka gudun gaba dan haruna dam mai hana noma.

Jagora : Na Katuka,

: Na Katuka karhwandamin kare mai kashe kura na Delu,

: Da munka zo gidan Alhaji lsa,

: Yac ce kidi in yi ma Gambu shi alhaji ne shi,

: Nac ce to ban kau rarrabad da waka haka nan ba,

: Yarana ku dora tausa mashi taki,

: Sai an ga hankalin alhaji ya kau,

: Sai ga alhaji an hilo da gora da barandami

 

Jagora : Da kau wakakkashi runtce ga hannu,

: Dada hwa hankalin alhaji ya kau na Kande

: Na Katuka karhwandamin kare mai kashe kura

: Na Katuka mai jan hali na Gambu hana noma,

: Na Katuka mai jan hali na Gambu,

: Mahaukaci na kofur hana noma,

: Doki ba a san ka whasa daukal lihidi ba,

: Ban san huntuwa ba sai dai in shiga garin in yi Kaduna,

: Kuma in biyi ciki in kashe sauna,

: Kuma in shigo garin in yi Kaduna,

: Sai yanzu da dan Haruna yas sa mani hannu,

: Ban dai son in kwan cikin gari ba ni da kowa,

: Kwan da shirin gaba dan Haruna dam mai hana noma,

: Mahaukaci na Kohur hana noma na Kande.

 

Musa na Kasar Dan 'ali Mai Tauri

Jagora : Ya san hanyah hwada,

: Musa na kasad Dan AR-mai tauri.

 

Jagora : Kai mutane tauri ya koma ga gadajje,

: Manyan hwada Musa,

: Na kasad Dan'Ali wan karhi.

 

Jagora : Na so zuwa gidam Mani a kaye ina sauna,

: ba yan yara warina,

: Sai yac ce diya nai ba su son tauri,

: Tsohon kau ya yi yayi nal,

: Nic ce sai nai kidi,

: In dai hanyak kidi ta taho.

 

Jagora : Jama'a na so Zuwa gidam Mani,

: Ba hanyak kidin tauri.

 

Jagora : Dan yaro ne Musa,

: Ashe ya ci magani,

: Bai samu wunn gwaji nai ba,

: Rannan sai yaddauki kwashe nai,

: Yat tasam ma gona tai,

: Ya ishe Sulllubawa,

: Yab bi yana bugun shanu,

: Yab bi yana kashin shanu,

: Yab bi yana kashin shanu.

 

Jagora : Ashe Musa ya ci magani,

: Bai samu wurin gwaji nai ba,

: Suna ta bugu suna sara,

: Dud dai ba a huda kainai ba,

: Ku am manyan hwada,

: Musa na kasad Dan Ali mai tauri.

 

Jagora : Yak kai kurwah hwada,

: Mata kuma sun sheka suna kuka,

: Ku yo gudummawa Hillani sun kashe Musa,

: Ku yo gudummawa Hillani sun sabafta shi.

 

Jagora : Had Dan'Ali zai wo hawa,

Nac ce: Ko ba ka ji Mani,

: Hillani sun kashe ma da.

 

Jagora : Tsoho bai bata rai nai ba,

: Bai kai ko ga kai nai ba,

: Sai yai ta jikon karera nai,

: Ya san ya shiryi yara nai.

 

Jagora : Nac ce ko ba ka ji tsoho,

: Hillani sun sabatta ka.

Yac ce "Dan'Ali koma gida,

: Ja dan nan ba ni son Karya,

: Ba ta biyu ba ba sara,

: Ba kau yakin takbi ba,

: Dan su Musa na tahowa gida.

 

Jagora : Manyan hwada,

: Musa na Rasad Dan'Ali wan karhi

 

Dammande

Jagora : Gagari daga karen Iro ba a ga jininka ba,

: Dammande mai taurin jiki,

 

Jagora : Na gidan alasan mutanen Zamani,

: Ga ka da karhi Alasan ka hukadkudaku,

:  Ko gewaya sat ran gina dan Musa,

: Ko gewaya sai ran gina,

: Dammande mai tarin jiki,

: Dammande maij tàrin jiki,

 

Jagora : An yi hwada da Baura ana kuddin gari,

: Ni ce Ku ne zurn'ar rashin dadin batu,

: To an yi hwada da Baura ana kuddin gari,

: Ni ce "Ku ne zuri'ad da ba dadin batu,

: In ka ji an tad da ba, Dansanda ne,

: Kanan ga a dunkuli wuski,

: Bana ba biya sai sai lamuni dan ldi.

 

Jagora : Dammande ban ga jininka ba,

: Dammande mai taurinjiki

: Dammande na gode,

: Na gode na Gidan oga na gode,

: Ka ba ni kuddi,

: Kuma ka ba ni dawaki,

: Ka koma ka sa man riguna,

: Na gode Baura,

: Ka sunkuda mani kuddi Dammaliki,

: Kassu kuma riguna sai na gaji,

: Ka sai mani doki,

: Ka koma ka sa man riguna,

: Allah dai shi kara maka arziki,

: Baura Allah dai shi kara ka amin don Kassu,

: Allah dai shi kara maka arzikinka,

: Baura Allah dai shi kara ka amin don Kassu.

 

Jagora : Na gode Alasan mutanen zamani,

: Ga ka da karhi Alasan ka hudak kudaku shi kadai,

: Ko gewaya sai ran gina,

: Dammande mai taurin jiki,

: A Dammande ba a ga jininka ba,

: Dammande mai taurin jiki.

 

Jagora : Gagari daga karen ldo;

: Karen ldo mai karhin gaba.

: Ummaru Sabon Birni .

 

Jagora : Wannan abun mu né dangin Bawa Gobirawa,

: Amma ko da Bawa yam mutu ba inda bai baro suna nai ba.

 

Jagora : Ko can in ka ji gatari sai buzu,

: Yara ko can don hwada aka tsoronuwa gidan Jangwarzo.

: Don hwada aka tsoron zuwa gidan Jangwarzo

 

Jagora : Haba abimmu ne dangin Bawa Gobirawan asali,

: Ko da bawa yam mutu ba inda bai baro suna nai ba,

: A'a ba inda bai baro hwansa ba,

: Ko gobe dan hwada aka isoron zuwa gidan Jangwarzo.

 

 

Jagora : Rad da Allah yay yo ni

: Kassu rad da Maisama yay yo ni,

: Ka ganan nan ban zo kidi ba Sabon Bimi,

: Sai da Ummaru yay Kirammu sabon Birmi,

: Sanda jikan Shawai,

: Ummaru jikan Shawai, :Zuriyag gidan Jari Kada.

 

Jagora : Sai da Ummaru yay kirammu sarki naz zo,

: Amma im baicin rashin sani,

: Ba bako ba ne gida nid dawo,

: Dan hwada aka isoron zuwa gidan Jangwarzo

: ko gobe dan hwada aka tsorgn zuwa gidan Jangwarzo.

 

Jagora : Wo dam maki gudu

: Mai sulken jiran maza dan Isa

: Da kai amza suka tsoron hwada na Sabon Bimi

: Dan hwada aka tsoron 2uwa gldan Jangwarzo.

: Bagobiri Sabon Birni

 

Jagora : A baude ma Bagobiri,

: Koma shirin duniyag ga hay yau ba ta gyaru ba,

: Ku shirya ba ta kimtsu ba,

: Koma shiri duniyag ga hay yanzu da yamutci,

: To bari wani yai izgilki a debe mashi doriya,

: Kada wani yai zigili a gabce mashi kan hwari,

: Saji da Bagobir.

 

Jagora : Dadi na da Gobirawa,.

: Du inda kunka zo ba ku hukuntuwa.

 

Jagora : Baban Lawwali uban fnai saje.

: Sa adu barkak ka da yaute

: Barkak ka da yamutci

: Sa'adu barkak ka da yamutci.

 

 

Jagora : Baude ma Bagobiri,

: Sabon Birni Sa adu barkak da ka yamutci.

 

Jagora : Ga sako wanda za ni kai ma,

: Ka lura da wakad da yay yi ma,

: Sai ka yi kokari ka šho mani rakumi,

: Kahin in taho mu iske ka da rakumi,

: Caman in na zo Arewa sai na rike rakumi,

Kulum niz zo Arewa sai na rika rakumi.

 

Jagora : Sarkin Rahi Haruna ya kai mani rakumi,

: Sarkin Rahi na Haruna ya kai mani rakumi,

: Dandawaki na mai lalle ya kai imani rakumi,

: Dandawaki na Mai'lalle bara ya kai mani rakumi.

 

Jagora : In na zo arewa sai' na rike rakumi,

: Ina son ka yi kokari,

: Ina son ka yi hamzari, ka yi cinaki ka damre mani in taho.

 

Jagora : Sa adu ina son ka y cinaki ka damre mani in tano,

: Baude na Bagobiri.

 

Jagora : Baban lawwal uban mai saje,

: Sa'adu barak ka da yamutci,

: Nabara so nikai

: Nabara so nikai ku damre mani rakumi

: Ku damre mani rakumi,

: Ku aika mani in taho,

: Kai Nabara so nikai ku damre mani rakumi,

: Ku aika mani in taho.

 

Jagora : Hana noma na Hankurau,

: Sa’adu mai hana noma na Hankurau,

: Sa'adu barkak ka da yamutci,

: Sarkin Karman Gobir an nan Sabon Birni.

 

Jagora :Yara ku san dadina da Gobirawa,

: Du inda Sunka zam ba su hukuntuwa,

: Ina wani mai gardama a debo mashi doriya,

: Ina wani mai son hwada a jirge mashi kan kwari.

 

Jagora : A koma shiri duniyag ga hay yau ba ta gyaru ba,

: Yara ku koma shiri duniyag ga hay yau ba ta kimtsu ba.

: Madalle Bagobiri,

: Madalle Bagobiri,

: zuma na yawo,

: Yaro kada ka yi izgili ta hwada maka kakkarai.

 

Jagora : Sabon Birni gidan Bawa Jangwarzo,

: Inda masu yaki suke gurzuwa.

 

Jagora : Gidan bawa Jangwarzo

: Ka gane su hay yau ba su milku ba,

Sa’adu hay yau ba ku gyaru ba.

Post a Comment

0 Comments