𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu
alaikum da ftn malam Yana lfy. Dan Allah malam ina so a taimaka min da wata
addu'a Wanda Zan dinga yi dan na samu mijin aure. Allah ya jarabceni da
jinkirin aure shi ne nake neman taimako na addu'a ko Zan samu mafita.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikis
salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.
Abu na farko
da zanyi miki wasici dashi shi ne ki Ƙara haƙuri da juriya bisa wannan
jarrabawar da Allah ya dora miki. Ki sani cewa akwai wasu da dama waɗanda
musibar da suke ciki ta ninninka taki. Kuma ki sani cewa Allah bai manta dake
ba. Yana sane dake da kuma halin da kike ciki. Kuma da sannu zai yaye miki
damuwarki cikin falalarsa.
Ga wasu daga
Sahihan addu'o'i nan ki rikesu ki rikayi. In Shã Allahu zaki ga biyan bukata
cikin sauki:
1. Ayah ta
3-4 a cikin suratut Talaƙ:
وَمَن يَتَّقِ
اللَّهَ يَجْعَل لَّهُ مَخْرَجاً -وَيَرْزُقْهُ مِنْ حَيْثُ لَا يَحْتَسِبُ وَمَن يَتَوَكَّلْ
عَلَى اللَّهِ فَهُوَ حَسْبُهُ إِنَّ اللَّهَ بَالِغُ أَمْرِهِ قَدْ جَعَلَ اللَّهُ
لِكُلِّ شَيْءٍ قَدْراً
Yazo a cikin
Musnad na Imamu Ahmad bn Hanbal, Hadisi daga Sayyiduna Abu Dharrin Al Gifariy
(Allah ya yarda dashi) yace "Manzon Allah ﷺ bai gushe ba, yana karanta mun
wannan ayar, sannan yace "YA ABA DHARRIN, DA ACHE DUKKAN MUTANE ZA SUYI
RUKO DA WANNAN AYAR DA TA ISHESU".
(Aduba
Musnadu Ahmad juzu'i na 5 shafi na 178).
Don haka ki
rike wannan ayar ki rika yin wuridinta da kyakkyawar niyyah. In Shã Allahu zaki
samu biyan bukata cikin sauki.
Bayan wannan
akwai yawaita istighfari. Hadisi ya inganta daga Muhammad dan Aliyu dan Abbas
ya karbo daga babansa, daga Ka kansa Sayyiduna Abdullahi dan Abbas (Allah ya
yarda dasu) yace Manzon Allah ﷺ ya ce:
"DUK
WANDA YA YAWAITA ISTIGHFARI, ALLAH ZAI SANYA MASA YAYEWA DAGA KOWACCE DAMUWA,
DA MAFITA DAGA KOWANNE TSANANI, KUMA ZAI AZURTASHI TA INDA DUK BA YA
TSAMMANI".
(Musnadu Ahmad
juzu'i na 1 shafi na 248).
Ki yawaita
sadaƙah domin itama hanya ce ta samun yayewar tsanani da kuma biyan bukatu.
Sannan shima istighfarin ki rika yin daruruwa ko dubunnai a kullum.
Hakanan ki
yawaita salati bisa Shugabanmu Annabi Muhammadu ﷺ. Shima babbar hanya ce ta
samun biyan bukatu da yayewar damuwa in Shã Allahu.
Ina rokon
Allah Maɗaukakin Sarki ya biya miki bukatunki ya yaye miki damuwarki, kuma ya
azurtaki da samun miji nagari wanda zai rikeki cikin mutunci.
WALLAHU
A'ALAM.
Ga Masu Buƙatar
Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin mu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/J1hm5Tw12uYBƙfaiPwf28l
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.