𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu
alaikum da ftn malam Yana lfy. Dan Allah malam ina so a taimaka min da wata
addu'a Wanda Zan dinga yi dan na samu mijin aure. Allah ya jarabceni da
jinkirin aure shi ne nake neman taimako na addu'a ko Zan samu mafita.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikis
salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.
Abu na farko
da zanyi miki wasici dashi shi ne ki Ƙara haƙuri da juriya bisa wannan
jarrabawar da Allah ya dora miki. Ki sani cewa akwai wasu da dama waɗanda
musibar da suke ciki ta ninninka taki. Kuma ki sani cewa Allah bai manta dake
ba. Yana sane dake da kuma halin da kike ciki. Kuma da sannu zai yaye miki
damuwarki cikin falalarsa.
Ga wasu daga
Sahihan addu'o'i nan ki rikesu ki rikayi. In Shã Allahu zaki ga biyan bukata
cikin sauki:
1. Ayah ta
3-4 a cikin suratut Talaƙ:
وَمَن يَتَّقِ
اللَّهَ يَجْعَل لَّهُ مَخْرَجاً -وَيَرْزُقْهُ مِنْ حَيْثُ لَا يَحْتَسِبُ وَمَن يَتَوَكَّلْ
عَلَى اللَّهِ فَهُوَ حَسْبُهُ إِنَّ اللَّهَ بَالِغُ أَمْرِهِ قَدْ جَعَلَ اللَّهُ
لِكُلِّ شَيْءٍ قَدْراً
Yazo a cikin
Musnad na Imamu Ahmad bn Hanbal, Hadisi daga Sayyiduna Abu Dharrin Al Gifariy
(Allah ya yarda dashi) yace "Manzon Allah ﷺ bai gushe ba, yana karanta mun
wannan ayar, sannan yace "YA ABA DHARRIN, DA ACHE DUKKAN MUTANE ZA SUYI
RUKO DA WANNAN AYAR DA TA ISHESU".
(Aduba
Musnadu Ahmad juzu'i na 5 shafi na 178).
Don haka ki
rike wannan ayar ki rika yin wuridinta da kyakkyawar niyyah. In Shã Allahu zaki
samu biyan bukata cikin sauki.
Bayan wannan
akwai yawaita istighfari. Hadisi ya inganta daga Muhammad dan Aliyu dan Abbas
ya karbo daga babansa, daga Ka kansa Sayyiduna Abdullahi dan Abbas (Allah ya
yarda dasu) yace Manzon Allah ﷺ ya ce:
"DUK
WANDA YA YAWAITA ISTIGHFARI, ALLAH ZAI SANYA MASA YAYEWA DAGA KOWACCE DAMUWA,
DA MAFITA DAGA KOWANNE TSANANI, KUMA ZAI AZURTASHI TA INDA DUK BA YA
TSAMMANI".
(Musnadu Ahmad
juzu'i na 1 shafi na 248).
Ki yawaita
sadaƙah domin itama hanya ce ta samun yayewar tsanani da kuma biyan bukatu.
Sannan shima istighfarin ki rika yin daruruwa ko dubunnai a kullum.
Hakanan ki
yawaita salati bisa Shugabanmu Annabi Muhammadu ﷺ. Shima babbar hanya ce ta
samun biyan bukatu da yayewar damuwa in Shã Allahu.
Ina rokon
Allah Maɗaukakin Sarki ya biya miki bukatunki ya yaye miki damuwarki, kuma ya
azurtaki da samun miji nagari wanda zai rikeki cikin mutunci.
WALLAHU
A'ALAM.
Ga Masu Buƙatar
Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin mu...
NEMAN ADDU'AR SAMUN MIJIN AURE
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum. Tambayata itace Don ALLAH wacce
Addu'a zanyi domin samun miji nagari cikin karamin lokaci? Allah ya jarabceni
da jinkirin aure shine nake neman taimako na addu'a ko Zan samu mafita.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus Salam warahmatullahi Wabarkatuh
A iya karamin ilimin mu bamu san wata keɓantaciyar addu'a ba wacce Manzon Allah (Sallallahu alaihi
Wa sallam) ya koyar a karanta domin samun Miji nagari ko Mata tagari. Sannan
kuma bai halatta ga musulmi yayi addu'a yace yana son Allah ya biya masa da
bukatarsa nan take, ko kuma a lokaci qayyadadde. Saboda Shi Allah ba'a sanya
masa lokaci a biyan bukatar mai addu'a.
Amma mutum zai duqufa yana rokon Allah ya haɗa shi da mata tagari ko kuma mace Allah ya haɗa ta da Miji nagari.
Addu'a itace makami mai kaifi da mumini/mumina
zai/zata yi amfani wajen yanke duk wata matsala dake a gabansu.
Akwai wasu lokuta idan bawa yayi addu'a Allah na
karɓa masa kai tsaye. Misali kamar sulusin dare na karshe
kamar yadda ya tabbata a hadisi.
Yana daga cikin sharaɗin addu'a musulmi ya kasance babu haram a cikinsa (baici
abincin haram ko abin sha na haram ba), musulmi ya kasance bai yanke zumunta
ba, ya kasance baiyi gaggawa ba, kuma ya kasance ya zaɓi kyakkyawan lokacin yin addu'a, sannan ya nisanci Neman
gaggawar karɓawa.
Ya tabbata a hadisi cewa; An Karɓo daga Abu Hurayrah (R.A) Yace; Manzon Allah (sallallahu
alaihi Wa sallam) Yace: (Allah) yana karɓawa ɗayanku (addu'arsa) matuqar baiyi gaggawa ba, (shine) yace
nayi addu'a (amma har yanzu) ba'a amsamin ba. (Bukhari, 5865. Muslim, 2735).
Manzon Allah (Sallallahu alaihi Wasallam) Yace :
"hakika ubangijinku mai kunya ne, mai karamci ne. yana jin kunyar bawansa
yayin da ya cira hannayensa ya rokeshi, ace ya mayar dasu ba tare da komai
ba".
An karbo hadisi daga Buraidata (r.a) ya ce: Manzon
Allah (Sallallahu alaihi Wasallam) ya ji wani mutum yana cewa:
اللَّهُمَّ إِنِّي أَسْأَلُكَ بِأَنِّي أَشْهَدُ أَنَّكَ أَنْتَ
اللَّهُ لاَ إِلَهَ إِلاَّ أَنْتَ الأَحَدُ الصَّمَدُ الَّذِي لَمْ يَلِدْ وَلَمْ يُولَدْ
وَلَمْ يَكُنْ لَهُ كُفُوًا أَحَدٌ
MA'ANA: "Ya Allah hakika ina rokonka, na
shaida kai ne Allah, babu abin bautawa da gaskiya sai kai, makaɗaici, madawwami, wanda ba ya haifuwa kuma ba a haife shi
ba, kuma babu wanda ya kai shi."
sai manzon Allah (Sallallahu alaihi Wasallam) ya
ce: “Lallai ka yi roƙo da sunan da Idan aka yi roƙo da shi ana bayarwa, kuma idan aka yi addu'a da shi ana amsawa".
mutane huɗu suka ruwaito shi, Ibn
Hibban ya inganta shi.
Wannan hadisin na nuna mana kenan ana saurin Amsa
addu'ar Wanda ya yi amfani da waɗannan sunayen
kenan.
Saboda haka 'yar uwa Idan za ki yi addu'a, sai ki
fara ambaton waɗancan sunayen,
sannan sai addu'ar ta biyo baya.
Don haka ki kyautata tunaninki. Hakika Allah ya
riga ya amsa miki. Kawai lokacin ganin abun ne bai Qaraso ba. ki Qara hakuri da
juriya bisa wannan jarrabawar da Allah ya dora miki. Ki sani cewa akwai wasu da
dama waɗanda musibar da suke ciki ta ninninka taki. Kuma ki sani
cewa Allah bai manta dake ba. Yana sane dake da kuma halin da kike ciki. Kuma
da sannu zai yaye miki damuwarki cikin falalarsa. ki sani kowanne abu yana da
lokacinsa wanda Ubangijiya riga ya Qaddara agareshi. Kuma abubuwa suna gudana
ne bisa gwargwadon yadda Ubangiji Allah Ya Qaddara kuma yaso su faru.
Muna rokon Allah yabaki Miji nagari mai addini mai kaunarki, Wanda zai zamo farin-cikinki ya zama sanyin idonki. Ya Allah Matanmu marasa Maza, Allah kabasu Mazaje na gari masu addini. Mazanmu marasa Mata, Allah kabasu Mata nagari. Ka albarkaci al'ummar Musulmai a duk faɗin duniya. Ameen Ya Hayyu Ya Qayyum.🤲🏻
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance Damu...
INA SON ADDU'AR NEMAN MIJI NAGARI
TAMBAYA
(218)❓
Dan Allah
malam akwai wasu adda'o'in da zaka bani wanda zan yi dan samun miji nagari
sannan da sauran buqatuna dan Allah 🙏🏻🙏🏻🙏🏻
Sannan dan
Allah taya zan gane mijin nagari
AMSA❗
Banada ilimi
akan wata kebantacciyar addu'ar samun miji nagari
Saidai zaki
iya gane miji nagari ta hanyar bincike akan mu'amalarsa da addini musamman
wajen koyi da sunnah
Sannan kuma
sai mu'amalarsa da alummah
Rashin
kyakkyawar mu'amalar sa da mutane shi ne ke sa ake shan wahala idan aka aure
shi yayinda rashin kyakkyawar mu'amalar sa da sunnah kuma ke kawo rashin nuna
kulawa, zagi, duka, da kuma saki
Maganin kar
ayi kar a fara. Sannan kuma idan kin samu sai ki rakashi da addu'ar Istikhara
ya zamana kin fara bawa Allaah zabi kafin ku fara soyayyar saboda kada ki zo ki
ce in bashi ba sai rijiya, ki zo Allaah yabarki da zabinki dogaro da hadisin
Jabir Ibn Abdullahi (Radiyallahu anhu) da yace Annabi (Sallallahu alaihi
wasallam) yana koyar damu Istikhara kamar yanda yake koyar damu Sura daga cikin
Qurani
A yanzu haka
akwai miliyoyin matan da suke da na sanin auren mazajen su saboda kafin su aure
su sun nuna musu sunada kyakkyawar mu'amalar amman sai bayan anyi auren sai ta
gane ashe karya yake mata. Yayinda mutanen waje suke masa kallon Alhaji mai
babbar mota ita kuma tana masa kallon makaryaci mai karamar qwaqwalwa wanda ba
ya tarairayarta da ba ta kulawa
Ba shi da
kyakkyawar alaqa da mutane sannan kuma a cikin ibadar sa akwai kura kurai sunfi
cikin buhu
Akwai wani
saurayi shekarar da ta gabata, da na zauna dashi yacemin na sakashi a addua an
saka masa rana da wata yarinya
Matashin dan
kasuwa ne yanada rufin asiri ba laifi
Amman
matsalar shi ne a cikin kasa da mintuna 10 na gane cewar wallahi sai ta yi da
na sanin auren sa in dai bai tashi ya nemi ilimi ba
La'akari da
cewar common wannan add'uar da Annabi (Sallallahu alaihi wasallam) ya koyar ta
kusantar iyali wallahi bai iya ta ba
Na ce masa
zamu bude Online Class da yake da alaqa da gyaran Ibadah laakari da komai
ilimin ka a bangaren muamalar auratayya to fa ba komai ka sani ba
A yanzu haka
na rubuta littattafai guda 3:
1) MU'AMALAR
AURATAYYA A MUSULUNCI
2) HUKUNCE
HUKUNCEN JININ MATA
3) FATAWOWI
30 AKAN MU'AMALAR AURATAYYA
Kowanne
littafi yana dauke da sama da shafi 100 da hujjoji qwarara daga Qurani,
Hadisai, Ijma'i da Qiyasin malamai
Amman abin
mamakin shi ne a yanzu haka wasu tambayoyin da ake turomin ma gaba daya babu su
a cikin littattafan
Ilimi fadi
ne dashi kamar teku saidai kawai ka dangwalo iya rabon ka
Karshe dai
matashin can bayan mun rabu har yanzu da nake maganar nan batun shiga Class din
can ya sha ruwa. Fatan da nake shi ne Allaah yasa dai ya shiga wata makarantar
don ya gyara ibadar sa
Idan kuma
bai shiga ba to hakan fa na nufin lokacin da zai sadu da iyalinsa za su yi
tarayya ne da shaitan kamar yanda Annabi (Sallallahu alaihi wasallam) ya fada a
cikin Sahihayn
Kuma a haka
ake sa ran samun al'umma ta gari ?
Don haka
shawarar da zan baki anan shi ne ki dage da addu'a musamman a cikin watan
Ramadan dinnan sannan kuma kema din ki zamo ta gari in dai kikai hakan to
tabbas Allaah Azzawajallah zai kado miki wani Sunnah Guy a.k.a Rajalis Salih🥰wanda zaku yi aurenku cikin aminci da kwanciyar hankali
sannan kuma idan kun shiga Aljannah tare Allaah ya sake aurar daku, ku huta a
gidan dawwama sannan ku sha Zanjabeel daga tafkin Salsabeel
Wannan shi
ne shawarar da nake baki tareda sauran al'ummah dake wannan zauren na Tambaya
da Amsa
Wallaahu
taala aalam
Amsawa:
Usman
Danliti Mato (Usmannoor_Assalafy)
Zauren
Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/J1hm5Tw12uYBƙfaiPwf28l
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.