𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum. Don Allah malam
mene ne hukuncin saƙon da za a turo ana faɗin cewa an yi mafarki cewan duk
wanda ya tura zai kasance cikin alkhairai masu yawa, wanda kuma bai tura ba bala'i
da musiba za su afku mishi?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus Salam. A gaskiya
Ire-iren waɗannan saƙonni da a ƙarshensu ake cewa idan ka tura wa adadin mutane
kaza za ka ga abin alheri, idan kuma ka ƙi tura ma kowa za ka haɗu da bala'i da
musiba nan da kwana kaza, duk irin waɗannan maganganu ƙarya ce kawai tsabarta,
domin ko addini ba a ce dole ne sai an tilasta mutum ya yi ba, balle kuma tura
wani saƙon da ba shi da asali.
Sau da yawa masu ƙirƙirar ire-iren
waɗannan saƙonnin suna jingina ƙarya ga limamin Makka ko Madina ne, ko su
jingina ƙarya ga mai gadin masallacin Annabi ﷺ su ce wai limamin Makka ko na
Madina ko mai gadin masallatan ya yi mafarkin Manzon Allah ﷺ ya ce masa kaza da
kaza, kuma Annabi ﷺ ya umarce shi ya isar wa da mutane wannan saƙo, kuma duk
wanda ya ji ko ya ga wannan saƙo idan bai isar wa da adadin mutane kaza ba, to
bala'i da musiba za su same shi nan da kwana kaza, idan kuma mutum ya isar wa
da adadin mutane kaza ko kaza zai ga alheri a rayuwarsa.
Wani lokacin ma har da rantsuwa
suke haɗa wa su ce wai wani mutum a wani gari ko wata ƙasa ya ga wannan saƙo ya
tura wa adadin mutane kaza sai ya sami alheri mai yawa a rayuwarsa, wani kuma
ya ga saƙon sai ya ƙi tura ma kowa sai Allah ya mayar da shi biri, ko kare, ko
su ce wai ya sami karayar arziki saboda ƙin tura ma kowa.
A gaskiya duk irin waɗannan saƙonni
ƙarya ce tsantsa suke jingina ma waɗancan limamai ko masu gadin Haramain, kuma ƙarya
ce tsantsa suke wa Annabi ﷺ Kuma Annabi ﷺ ya ce: "Duk wanda ya jingina
mini ƙarya da gangan ya jiraci masaukinsa a wuta".
Bukhariy 1291. Muslim 3004.
Addini ya riga ya cika, babu wani
alheri da Annabi ﷺ ya bar shi bai nuna ma al’ummarsa ba, haka kuma ba wani
sharri da bai faɗakar da mu shi ba. Don haka mu guji yi wa Annabi ﷺ ƙarya da yaɗa
ƙaryar da aka yi masa, Allah ya kare mu da yi wa Annabi ﷺ ƙarya, amin.
Allah ne mafi sani.
Jamilu Ibrahim Sarki, Zaria.
Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan
Group Zaku iya bi ta Links ɗin mu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.watsapp.com/FmJ5Ojsns1KFolTP8ƙu9GT
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.