Ticker

6/recent/ticker-posts

Bikin Saukar Alƙur’ani A Garin Gusau

Kundin binciken da aka gabatar a Sashen Nazarin Harsuna Da Al’adu, Tsangayar Fasaha, Jami’ar Tarayya Gusau, saboda cike wani gurbi, domin samun shaidar kammala digirin farko na fannin nazarin harshen Hausa (B.A. Hausa) (Oktoba, 2021).

Bikin Saukar Alƙur’ani A Garin Gusau

Na

Makiyu Balarabe

Sauƙar Karatu

SADAUKARWA

Na sadaukar da wannan aiki nawa zuwa ga mahaifana Marigayi Malam Musbahu Balarabe Rogo da mahaifiyata Rukayya (Gambo), domin su suka bani ƙwarin guiwa dan ganin na mai da hankali a kan karatuna da kuma irin addu’o’in da suka yi. Da fatar Allah (SWT) ya jaddada harama a gareshi da sauran Musulmi baki ɗaya.

 

GODIYA

Ina miƙa godiya ga Allah (SWT) mai kowa mai komai, mai iko a kan kowa, wanda ya ƙaddare ni da kammala kundin Digirina Farko. Ina Salati marar iyaka ga jagoran al’umma Annabi Muhammad (SAW) da iyalansa da sahabbansa, da kuma waɗanda suka bi tafarkin sa har ya zuwa ranar ƙiyama.

 

Ina miƙa godiya ta musamman, ga madugu uban tafiya, wato ubanmu, kuma shi ne ya yi ƙoƙarin ɗora ni a kan hanya don ganin an yi nasarar wannan aiki, wato Dr. Adamu Rabi’u Bakura. Haka kuma ina godiya ga sauran Malamai na sashe kamar Malam Musa Zaria, Mal. Isah S. Fada, Malam Bashiru Abdullahi da Malama Halima da Dr. Aliyu Dangulbi.

 

Godiya ta musamman ga Shehi na kuma Murabbina wanda shi ne mai tarbiyantar da ni Sheikh Mal. Abdullahi Abubakar Yabo, Zawiyya, Gusau, da kuma mai ɗaki na Rahinatu Muhammad Bello (Baby), da yaranmu Makiyya da Muhammad Abdullahi (Murad) da ma duk wanda ya taimaka a kan wannan nasara da Allah ya bani ta kammala wannan Digiri na Farko, Allah Ubangiji ya saka maku da mafificin Alkhairi amin.

 

TSAKURE

Wannan bincike mai taken Bukin Saukar Alƙur’ani a Garin Gusau, ya sha banban da sauran bukukuwan ƙasar Hausa, domin ana gabatar da shi ne, a sanadiyar sauke Alƙur’ani ko haddace shi da ɗalibai kanyi. Ya yin gudanar da wannan bincike, an yi waiwaye domin duba ayyukan masana da manazarta, kama daga bugaggun littafai, kundayen bincike, mujallu da muƙalu. Wannan bincike ya bayyana ma’anar kalmar biki, sauka, Alƙur’ani, gari, Gusau, daga bisani an kawo ire-iren bukukuwa da kuma tasirin da zamani ya yi game da bukin saukar Alƙur’ani, haka kuma an bayyana yadda ake aiwatar da bukin saukar Alƙur’ani a Garin Gusau Jiya da yau.

BABI NA ƊAYA

GABATARWA

1.0 SHIMFIƊA

Dukkan yabo da godiya sun Tabbata ga Allah Ubangijin talikai, mai kowa mai komai wanda ya ƙaga halittar ɗan-Adam ya kuma Sanar da shi abin da bai sani ba. Salati da Aminci su ƙara tabbata ga jagora Annabi Muhammadu (S.A.W.) da Alayansa da sahabbansa da masu bin su har zuwa ranar tsayuwa, Ina kara godiya ga Allah da ya ƙaddara gudanar da wannan bincike a fannin Ilimi domin kammala karatun digiri na farko.

A wannan babi mai suna "Gabatarwa" za a yi bayanin abubuwa muhimmai kamar haka: manufar bincike domin babu wani aiki da za a gudanar ba tare da wata manufa ba. Saboda haka wannan aiki akwai manufar gabatar da shi idan an shiga cikin aikin za a ga manufar. Haka kuma an yi tsokaci a kan hasashen bincike, Farfajiyar bincike, matsalolin bincike, haka kuma an kawo Muhimmancin Bincike, Hanyoyin gudanar da bincike,  daga ƙarshe naɗewa.

1.1 MANUFAR BINCIKE

Duk wani abu da ɗan Adam zai yi to yana da manufa ko Dalili , babu shakka duk wani abu da aka yi shi babu maunufa to wannan abu ko ba shi da ma'ana kuma ba shi da amfani.

 

Wannan bincike yana da manufar da tasa aka gudanar da shi. Manufar gudanar da wannan bincike sun haɗa da: cike girbin kammala karatun samun shedar digiri na farko a fannin Hausa (B.A.Hausa). Haka kuma akwai ƙudirin  bayyana yadda ake Bikin saukar Alkur'ani a garin Gusau, wata kuma manufar ita ce domin a zaƙulo muhimman bayanai da suka shafi bikin sauka da ire-iren ta ko kashe kashenta. Domin a fahimtar da al'umma yadda Addinin Musulunci da ilimin Al-ƙur'ani suke da muhimmanci da matsayi a rayuwar Hausawa, dan gane da yadda suke gudanar da bikin saukar Al-ƙur'ani musamman in mun kalle shi ta fuskar jiya da yau (da da yanzu) a garin Gusau.

 

1.2 HASASHEN BINCIKE

A yayin da aka kammala wannan aikin ana hasashen binciken zai fito da hoton yadda ake gudanar da bikin saukar al-ƙur'ani ƙarara a garin Gusau, ya zama wata manazarta ga masu bincike game da bikin saukar Al-ƙu'ani da sauran bukukuwan Hausawa.

 

Bugu da ƙari ana hasashen ya zama wani madubin dubawa na lura da abin da ya kamata a yi koyi da shi musamman dan girmamawa ga Al -ƙur'ani dangane da airin abubuwan da ake aiwatarwa a wajan wannan biki na sauka. Daga ƙarshe ana hasashen a kallo irin rawar da uwayen yara da malaman su suke takawa a wajan saukar ɗaliban dangane da karrama su

 

1.3 FARFAJIYAR BINCIKE

Kafin Shiga cikin aikin ya kamata mu leka taskar malamai ko masana domin mu san Ma'anar “Farfajiya/Muhallai".

 

Sabo (2005) ya ce"Muhalli shi ne mazaunin da ke kewaye da mutum da dukkan Abubuwan da suke taimaka wa rayuwarsa ta yau da kullum, Muhalli ya samu ne ta hanyar basira da Allah ya yi wa ɗan Adam.  Muhalli awannan bincike shi ne Farfajiya, ko bagiren da aka gabatar da wannan bincike.

 

Wannan aiki an gudanar da shi ne a fannin al-adun Hausawa, da suka danganci bukukuwan sha'anin addini. Sannan an keɓance shi ne a garin Gusau domin samun sauƙin bayyana yadda ake yin bikin saukar Al’kur'ani.

1.4 MATSALOLIN BINCIKE

A nan matsalolin bincike sun fara ne tun daga lokacin da aka aminta da wannan batu da za a yi magana a kai, kafin shiga cikin wannan ya kamata mukalli maa'nar "matsala"kamar yadda masana sukayi tsokaci akai. Fulani da wasu (2014) sun ce: " Matsala na nufin duk wani abu da ya zo ya takura wa rayuwar ɗan Adam ya hana mutum ya kasa cimma burinsa ɗari bisa ɗari". Matsala na iya zama tawaya ga duk wani abu da mutum zai yi ko ya yi ko kuma yake yi. Bisa ga wannan ra'ayi za a'iya cewa "Matsala"na nufin duk wata ƙuntatawa a rayuwa da akan shiga ta fili ko ta boye.

 

Haƙiƙa an yi karo da matsaloli da dama. Daga cikin su akwai: Rashin kuɗi da rashin samun haɗin kai awajan mutanen da aka buƙaci a yi fira da su da kuma rashin samun wadatattun ɗakunan karatu da rashin samun littatafai masu alaƙa da aikin binciken namu, rashin samun hasken wutar lantarki da rashin tsaro.

 

1.5 MUHIMMANCIN BINCIKE

Muhimmanci ya na nufin amfani, kamar yadda ƙamusun Hausa (2006) ya bayyana ma'anar muhimmanci da cewa "Abu ne mai daraja kwarai ko amfani kwarai da gaske. Aikin bicike yana da matukar muhimmanci musamman ga dalibai masu karatu a gaba da sakandare. Domin shi bincike ya na ba da damar a gano matsala da kuma samun waraka a kan wannan matsala. Daga cikin muhimman cin wannan bincike zai taimaka wa ɗalibai masu nazarin al'ada musamman na gaba da makarantun sakandare.

 

1.6 HANYOYIN GUDANAR DA BINCIKE

Akan bi hanyoyi da dama, domin gudanar da bincike, To a wannan binciken an bi hanyoyi da dama domin samun nasarar wannan bincike. Daga cikin hanyoyin da a ka bi an leƙa ɗakunan karatu domin kalato bayanai a bugaggun  littafai da kundayen bincike da  mujallu da muƙalu da muhimman bayanai da za su taimaka don gudanar da wannan aiki. An kuma shirya yin fira da masu ruwa da tsaki ga lamarin wato  malamai, da Uwayen yara, hatta da su kan su ɗaliban an yi kokarin jin ta bakin su.

 

1.7 NAƊEWA

A wannan babi mai suna gabatarwa, ya na matsayin shimfiɗa ne ga aikin binciken, kuma yana matsayin tsanin takawa wajen gudanar da wannan aiki. A cikin wannan babi an kawo shimfiɗa, manufar bincike, hasashen bincike. Haka kuma an kawo farfajiyar bincike, da kuma matsalolin bincike, muhimmancin bincike, da hanyyoyin gudanar da bincike, daga ƙarshe naɗewa.

 

BABI NA BIYU

BITAR AYYUKAN DA SUKA GABATA

 

2.0 SHIMFIƊA

A wannan babi mai taken bitar ayyukan da suka gabata za ayi laluben wasu daga cikin ayyukan magabata, kama daga bugaggun littafai da kundayen bincike mujallu da muƙalu,waɗanda su ke suna da alaƙa da wannan bincike namu, alaƙar ta kai tsaye ko kuma ta wani ɓangare ce, to anan za muyi ƙoƙarin fito da wannan alaƙa. Sannan za a yi tsokaci a kan hujjar cigaba da bincike daga ƙarshe a zo da naɗewa.

 

2.1 BITAR AYYUKAN DA SUKA GABATA

Magabata sun yi rubuce-rubuce da wallafe-wallafe dangane da abubuwan da suka shafi biki da ma bukukuwan al-adun Hausawa amma masu alaƙa da wannan aikin bincike waɗanda hannun mu ya iya kaiwa gare su akwai irin Ƙofar Nasarawa, (2006)".Tsarin Tsangayun Al-kur'ni a Arewacin Najeriya". In da mawallafin a sashe na ɗaya babi na ɗaya ya ɗakko abun tun asali in da ya yi maganar asalin zuwan Musulunci a Arewacin Najeriya. Ya kuma yi bayani game da bikin sauka da sadaka a matakai daban-daban. Haka ya taɓo bayanin malaman Al'kur'ani na jihar Zamfara.

 

Muhammad, A. (1998) A littafinsa mai take: "Aure da Biki A ƙasar Hausa. Ya yi maganganun da suka shafi bukukuwan Hausawa na Al-adun su  a farkon littafin ya yi magana a kan ma'anar biki da kuma ire-iren biki. In da  mu kuma aiki na yana nazari ne a kan wani nau'i na biki.

 

Ɗangambo, (1984) A littafisa mai take: Rabe-Raben Adabin Hausa da Muhimmancin sa ga rayuwar Hausawa. Wannan littafi shi ma yana da Alaƙa da wani ɓangare na aiki na, dan aikin nawa ya shafi wani ɓangare ne na adabi.

 

Gusau, (2012) Bukukuwan Hausa, wanna littafi ya tattauna sosai musamman a kan al'adun bukukuwan da Hausawa su ke yi da kuma Muhimmancin su ga rayur Hausawa. A nan nima zan kalli irin muhimmancin Bikin Saukar Karatun Alƙur'ani.

Kundayen Bincike,

A nan a na buƙatar aduba kundaye daban-daban domin gano irin gudummuwar da suka bayar game da bikin saukar karatun Al'ƙur'ani ko kuma abun da ya yi kama da haka .da farko za mu kalli

 

Alhasan, M. (1994). Bambance-Bambancen Al-adun Bikin Aure tsakanin Al-ummar Hausawa da yarabawa. Kundin Digiri nafarko wanda aka gabatar a sashen harsunan Najeriya, Jami'ar Bayero, Kano. Wannan kundi ya yi tsokaci a kan irin bambance-bambancen da ake samu cikin bikin Aure.

 

Tahaka ne, nima zan kalli irin yan bambance-bambance da ake samu a tsakanin makarantun Allo da na Islamiyyoyi dangane da al’adun bikin saukar karatun Alƙur'ani mai girma.

 

Muhammad, (1992) Kundin Digirin farko, wanda aka gabatar a Jami'ar Maiduguri. A sashen nazarin Harshen Larabci. Wannan kundi kai tsaye ya yi bayani sosai dangane da abinda ya shafi bikin saukar karatun Al’ƙu'ani Maigirma, a garin Maiduguri dan haka ya na da alaƙa ta kai tsaye da wannan aikin nazari nawa. Duba da irin wannan ne ake ganin tahaka ne za a iya gano irin nasara ko gudummuwar da sukabayar a cikin binciken su,sannan kuma shi wannan aiki nawa ya san in da zai dora domin bunƙasar irin wannan nazari.-

Kundin Tsare-Tsaren Inganta makarantun Allo da na Isalamiyyoyi wanda Gwamnan Kano Malam Ibarahim shekarau ya kaddamar a ranar 23/10/2003 P.TT. Wannan kundi ya yi magana a kan yadda ake gudanar da wasu abubuwa dangane da karatun Al-kur'ani Maigirma.

Mujallu da Muƙalu Kuwa

Malamai masana da kuma Ɗalibai yan uwana sun gabatar da muƙalu da dama  da kuma rubuce-rubuce a kan irin wannan aiki sai dai hannuna baikai ga takardar da a ka yi kai tsaye a kan wannan aiki da ke nazari akai ba, na bikin saukar Alƙur'ani a garin Gusau ba  amma dai an samu masu kama da su ,kamar irin su:

 

Hassan, (2013) Nason baƙin Al-adu a kan Al’adun Aure da haihuwa da mutuwa na Hausawa. Muƙalar da aka gabatar a taron ƙarawa juna sani na ƙasa, a sashen harsunan Najeriya. Jami'ar Ummaru musa yar Aduwa.

 

Tabbas ta fannin nazarin mu wato bikin saukar karatun Al-ƙur'ani ana samun baƙin al’adu a cikin su, dan haka ne wannan Takardar muƙala ta na da alaƙa da wannan aiki nawa.

Bunza, (2004), Takarda a kan  Ilimin Tsubbu a ƙasar Hausa, jiya da yau. Angabatar da ita ne a Jamiar' Bayero Ranar 7, ga watan yuli 2004.

Bunza, (2013).Zama da Maɗaukin Kanwa ke sa farin kai; Nason Baƙin Al-adun Auren Hausawa. Mukalar da aka gabatar a Taron ƙarawa juna sani na ƙasa a sashen Harsunan Najeriya,Jami'ar Ummaru Musa Ƴaa'duwa.

2.2 HUJJAR CIGABA DA BINCIKE.

Kasancewar masana da manazarta sun yi aikace-aikace a kan abinda ya shafi biki ko bukukuwan al’adun Hausawa a nan  garin Gusau amma ba a samu wani da ya yi aiki a kan bikin sauka ba, musamman a nan Jami'ar Tarayya Gusau.

 

Masu nazari waɗanda su ka gabace mu ba su karaɗe ko ina ba dan haka sun bar giɓi wanda ya zamar mana hujja ta mu cigaba da yin bincike akai. Ina kira ga ɗalibbai yan'uwana da su cigaba da bincike don su ma su cika sauran gurbin da hannun mu bai kaiba.

 

2.3 NAƊEWA

A wannan babi na biyu an yi ƙokarin zaƙulo bitar ayyukan da suka gabata wanda suka ƙunshi bugaggun littafai da kundayen bincke da mujallu da muƙalu.Bugu-da-ƙari anyi tsokaci kan hujjar cigaba da bincike daga ƙarshe an rufe babin naɗewa.

 

BABI NA UKU

FASHIN BAƘI AKAN MA’ANONIN DA SUKA SHAFI TAKEN BINCIKE

3.0 SHIMFIƊA.

A wannan babi an kallo ma’anonin da suka shafi taken bincike a inda aka mai da ƙarfi wajen fayyace ma’anonin kalmomi, da su ne aka haɗa a ka samar da sunnan wannan bincike. Saboda haka ne suka zama tubalan ginin wannan bincike.

 

3.1 MA’ANAR KALMAR BIKI

Masana da dama sun tofa albarkacin bakin su dangane da maa'nar "biki" kamar yanda za a gani ɗaya bayan ɗaya:

 

Gusau, (2012) ya ce "Biki wani taro ne na mutane da suke shiryawa, su gudanar don nuna farincikinsu a kan wata bai wa da Allah (s.w.t.) ya yi mawa wani daga cikinsu ko ya yi wa wasu " ya ƙara da cewa biki ana yin sa don a nuna irin farin cikin da ake da shi ga wani abu ko don nuna farin ciki ga wani abu da ya faru ko don tunawa da wani abu muhimmi, ko don zagayowar wata rana.

 

Bayero, (2006) biki (sn,nj,jam'i bukuwa) An bayyana

1- Biki: shagalin farin ciki ko murna 2-kyauta ko gudummuwa wacce yawanci mata kan yi wa ‘ya’yansu yayin wata hidima da ta same su.

 

B.U.K.(2006:46) (Biki,sn,nmj,jam'i bukukuwa/bukunkuna) shagali na nuna farin ciki,Aure,ko suna,ko naɗin sarauta,ko salla, ko al’adun gargajiya. Garba (1990) (sn)"Annushuwar da ake yi don murnar wani abu".  A tawa fahimta, biki shi ne duk wani taro da ake yi domin taya murnar a kan wani abin farin ciki da ya samu.

 

3.1.1 Bikin Aure

Bikin Aure biki ne mai faɗin gaske, kuma biki ne wanda duk wasu ƙananun al’adu ba akan bar su ba sai an yi, saboda haka zamu dubi yadda tsarin Aure yake a Al-adar Bahaushe.

 

Aure Muhimmin abu ne a tsarin rayuwa, saboda haka, akwai hanyoyi ayyanannu da ake bi wajen atabbatar da shi, waɗannan hanyoyi sun haɗa da:

·        Zance

·        Baiko

·        Sarana

·        Kamu

·        Kunshi /wankan Amarya

·        Ajo

·        Ɗaukar Amarya

·        Sayen baki

·        Buɗar kai.

Kowanne daga cikin waɗannan al’adun na aure, na da bayanin yadda ake yin su da irin waƙokin da ake yi lokacin wasu daga cikin su, musamman ma lokacin kamu da ƙunshi da wankan Amarya.

 

3.1.2 Bikin Suna

Zanen suna al’ada ce da Bahaushe ke bi yana raɗa wa abin haihuwa wanda ka iya zama yaro ko yarinya suna.

 

Bunza, (2002), ya ruwaito cewa wannan al’ada daɗaɗɗiyar al’ada ce da ta wanzu a Ƙasar Hausa tun kafin kowane sauƙaƙƙen addini. Ana yin wannan al’ada ne ta hanyar samun wasu dattawa/dattaɓai su yi zane-zane a jikin kararen rama ɓararru guda bakwai, sannan sai a ɗauka a kaiwa mai jego, wanda duk ta zaɓa sai a yi amfani da zanen da ke jikinsa a raɗa wa jaririn ko jaririyar suna.

 

Wannan al’ada ta zanen-suna ta samu sauye-sauye da dama. Daga ciki akwai sauyin farko da ta samu yadda ya koma kawai jama’a na taruwa a ƙofar gidan da aka yi haihuwa, sai a rarraba musu goro da sauraran abubuwan da suka samu, sannan liman ya ce an sawa yaro ko yarinya suna wane ko wance. Sai kuma maroƙi ya faɗa da ƙarfi kowa ya ji. Sannan a yi addu’a, sai kuma kowa ya watse. Su kuma yara a lokacin da ake yin wannan addu’a, sai su ruga da gudu su shiga cikin gida wajen mata su gaya musu cewa an saka wa jariri ko jaririya suna wane ko wance. A lokacin da suke gudun suna ambatar Allah ya raya wane ko wance. Duk yaron da ya yi sauri ya fara isa ya je ya sanar cewa wane ko wance aka saka, akan bashi tukuici wanda kuɗaɗe ne da alewa da goro amma ba masu yawa ba. (Malam Isah, 2021).

 

Sai kuma a halin yanzu da Musulunci ya yi ƙarfi, a mafiya yawan gurare musamman birane, ba a ma taruwar sai dai a raɗa sunan a masallaci.

 

Ta fuskacin biki kuwa, akan yi shi hawa-hawa. Akwai wanda ake yi nan-take da zarar an raɗa sunan. Akan fito da abinci jama’ar da suka taru su ci, su kuma maroƙa da makaɗa suna kaɗe-kaɗensu.

 

Bayan kuma an gama wannan, sai su ma mata su haɗu yawanci har zuwa maraice, suna ‘yan kaɗe-kaɗe, da waƙe-waƙensu na mata, suna guɗa da sauransu. Sannan kuma sukan zo da kyaututtuka a matsayin gudunmawa ga ita mai haihuwar. Wannan taro na mata bai cika kaiwa faɗuwar rana ba.

 

Idan kuma haihuwar fari ce, to, akan samu mata su taru a gidan iyayen mai jego; wato gidan mata kenan, su haɗo nasu abubuwan. Bayan sun tattara abubuwan da suka tara, sai kuma su ɗauko shi da maraice zuwa gidan da aka yi haihuwa, gidan maza kenan, su zo su rarraba ga iyaye, da sauran dangin miji. Wannan rabo shi ake kira tsaraba.

 

Abun Lura: Akan samu saɓawar wasu abubuwa daga wani gidan zuwa wani ko kuma daga wani yankin zuwa wani yankin wanda ka iya zama ƙari ko ragi a kan abubuwan da aka zayyana a cikin wannan rubutun.

 

3.1.3 Bikin Salla Ƙarama

Bikin salla ya shigo ƙasar Hausa ne bayan shigowar addinin Musulunci. Wannan biki, jerin bukukuwa ne da ake gudanarwa a lokutan Idin Ƙaramar Salla. Waɗannan bukukuwa da ake yi suna da yawa; akwai hawan salla da sarakuna ke yi da dawakai, akwai kuma bukukuwan da sauran jama’a ke yi waɗanda suka shafi kaɗe-kaɗe da waƙe-waƙe, da gaishe-gaishe da kuma kyaututtuka da ziyarce-ziyarce.

 

Shi hawan salla biki ne da Sarakuna ke gabatarwa, a ƙasar Hausa, akan fara bikin hawan salla ne daga filin idi. Sarkin yanka yakan yi hawa da hakimansa da dagantansa da sauran masu riƙe da muƙaman sarautar gargajiya.

 

Kowane ɗaya daga cikinsu zai hau dawakai da tawagarsa cikin kwalliya daga su har dawakan nasu, suna tafiya jama’a kuma na kewaye da su suna kallo suna miƙa gaisuwa. A ranar farko akan tashi daga filin idi zuwa gidan sarki. Idan aka je gidan sarki, sai a jira sarki ya zo ya sauka, sannan duk sauran hakimansa ɗaya-bayan-ɗaya su je su yi gaisuwa. Bayan an kammala kuma sai sarki ya yi jawabi ga jama’ar ƙasarsa baki ɗaya sannan a sallami kowa ya watse.

 

Idan aka gama wannan a ranar farko, to washegari kuma sai a ci gaba, wanda wannan yakan bambanta daga masarauta zuwa wata masarautar. Kowace masarauta akwai takamaiman wani guri da sarki ke zuwa a wannan rana, su kuma jama’a su fito gefen hanya suna miƙa gaisuwa ga sarki, fadawa kuma suna karɓa.

 

Daga cikin sauran bukukuwa da mutane kan yi a lokutan salla akwai kiɗan kalangu da ake yiwa ‘yan’mata suna rawa, akwai makaɗa da mawaƙa da suke gudanar da wasanni ciki har da makaɗan ban-dariya, da makaɗan jama’a.

 

3.1.4 Bikin Salla Babba

Bikin salla babba anayin wannan biki ne a watan shabiyu na kalandar musuluncin ko wacce shekara wato "Zulhajji "ya yin da watan ya yi kwana goma. Shi ma yana ɗaya daga cikin bukukuwan da addinin Musulunci ya zo da shi. Kamar dai sauran bukukwa shi ma ya na tattare da irin nashi al’adu kama daga yin sabbin ɗunkuna yanke-yanke (layya) ziyartar yan uwa da abokan arziki. Sannan a cikin wannan watan ne ake aiwatar da ɗaya daga cikin shika shikan musulunci guda bayar da ake da su, wato aikin hajji wanda yake wajibi ne ga dukkan mutum, musulmi, baligi maihankali, kuma wanda Allah ya horewa kuɗin zuwa.

 

3.1.5 Bikin Mauludi

Bikin Maulidi biki ne wanda shi ma ya na ɗaya daga cikin bukukuwan da suka samu sakamakon zuwan addinin Musulunci a ƙasar Hausa. A na yin bikin mauludi ne a cikin watan Rabi'u Auwal wato watan uku na kowa ce shekarar Musulunci. Anayin wannan biki ne a sha biyu ga watan rabu'u Auwal ana yin bikin ne sabo da tunawa da zagayowar ranar da aka haifi fiyayyen hallita Annabi Muhammadu (S.A.W) wasu suna yin bikin sau biyu bayan na ranar haihuwa har da na ranar suna suke yi. Bikin Mauludi yana tattare da al’adu a cikinsa kamar: Yanke-yanke kaji da raguna da shanu Akan shirya abinci iri-iri ana yin sababbin ɗukina. Ana raya dare da karance karancen yabon Annabi.

 

Ana karatun tarihin Annabi Muhammad (S.A.W.) ‘yan mata sukan shirya abinci ga samarin su masu neman auren su.

3.2 MA’ANAR KALMAR SAUKA

Masana sun bayyana tasu ma’ana dangane da kalmar "sauka". Kamar yanda za a gani kamar haka:

 

Bayero (2006:394) ya nuna cewa kalmar Sauka (Sn, Mc) 1-Jiɗa 2-Baƙuntar wani gida 3-kammala kartun Al-ƙur'ani maigirma gabaki ɗayan sa.4-Bai wa baƙo abinci saboda zuwan sa.

 

A tawa fahimta, kalmar sauka na nufin kammala wani abu da ya zama dole musamman idan muka kale ta a matsayin "sauke "misali sauke farali (zuwa aikin haji ga wanda Allah ya ba ikon zowa).

 

Kalmar sauka ana amfani da ita wajan tashi, ko hauhawar fara shin kayan masarufi. Wanda ida sun yi sau ƙi akan ce ai kaya sun "sauka ".

 

3.2.1 Ma’anar Kalmar Al-Ƙur'ani

Al-ƙur'ani zancen Allah ne, wanda aka saukar da shi ga Annabi Muhammadu (S.A.W.) ta hanyar malaika Jibrilu, cikin harshen Larabci, abin karantawa daki-daki, wanda karanta shi ibada ce.

Alƙur'ani yana da sunaye daban da ban kamar yadda ya zo a cikin alƙur'ani

1.Al-ƙur'ani (القرآن ).

kamar yadda Allah ya ambace shi a cikin Suratul-Baƙara  aya ta 185

 ãöky­ tb$ŸÒtBu üÏ%©!$# tAÌRé& ÏÏù ãb#uäöà)ø9$# Wèd Ĩ$¨Y=Ïj9 ;M»oYÉit/ur z`ÏiB 3yßgø9$# Èb$s%öàÿø9$#ur 4  

Fassara:

Watan Ramadana ne wanda aka saukar da Alƙur’ani a cikin sa, yana shiriya ga mutane da hujjoji bayyanannu daga shiriya da rarrabewa. (2:185)

2.Alfurƙan ( الفرقان)

Kamar yadda ya zo acikin suratul furƙan aya ta 1,

 

Fasssara; Albarka ta tabbata  ga wanda ya saukar da( littafi)mai rarrabewa akan bawan sa, domin ya kasance mai gargaɗi ga halittu.

 

3.ZIKR(ذكر) kamaryadda yazo a suratul

Hijiri ayata 9 

 

Fasssara: Lalle mu ne muka saukar da Ambto (Al-kur'ni)kuma lalle haƙiƙa mu masu kiyayewa ne gare shi”.

4.KITAB (الكتاب) Kamar yadda ya zo a cikin suratul khahfi Aaya ta 1

Fassara:

“Godiya ta tabbata ga Allah, wanda ya saukar da littafi akan bawansa, kuma bai sanya karkata ba agareshi”

 

3.3 MA’ANAR KALMAR GARI

Bayero (2006: 159), ya nuna cewa kalmar “Gari” na cikin jerin sunaye na maza, jam’i kuma garrumma, a wani Karin halshe akan ce garurruka, ko garurra. Kalmar na nufin wurin da mutane suka zauna suka yi gidaje.

 

3.3.1 Kalmar Gusau

Dangane da ma’anar kalmar Gusau kuwa, har ila yau bayero (2006: 177), ya bayyana cewa kalmar na cikin jerin kalmomin suna jinsin mace, ya kuma nuna kalmar na ɗauke da ma’anar: “Sunan babban Birnin Jahar Zamfara.

 

3.3.2 Kafuwar Garin Gusau

An kafa Garin Gusau a shekarar (1811) bayan tasowa daga “Yandoto a shekarar (1806) garin Gusau na ɗaya daga cikin manyan garuruwan tsohuwar jihar sakkwato, kafin daga bisani yazama babban birnin jihar Zamfara a she karar (1996) kamar yadda kudin tarihun ƙasa na (1920) yanuna, garin yana bisa kan hanyar sakkwato bisa titin Zariya, kilomi kilo mita 179 tsakanin shi da Zariya, kilomita 210 tsakanin shi da sakkwato. Daga gabas ya yi iyaka da ƙasar Katsina da Ƙwatarkwashi daga Arewa ya yi ika da ƙasar Ƙaura, daga yamma yayi iyaka da Bunguɗu ta ɓangaren kudu kuma yayi iyaka da ƙasar Ɗansadau da Tsafe. Gusau , (1912:7).

 

Kasancewar Almajiran shehu Usaman Ɗanfodiyo ne wato Malam Sambo ƊanAshafa, shi da jamaar'sa suka kafa Gusau ya sa ba a samu baragurbi ba a ƙasar dangane da bautar gumaka ko bautar tsafi da iskoki irin na jahiliyya ba .Hakan ya sa duk Al-adun Gusau al’adu ne irin na Addinin Musulunci, kuma shi duk da shigowar baki a cikin garin na Gusau ba ta sa al’adun nasu sun gurɓata ba, mafi yawan bakin da suke shigowama malamai ne na Addinin musulunci. Ta ɓangaren yaƙi kuma duk abin da zai taso to zayi maganin shi ne cikin dabara da abin da Musulunci ya yadda da shi wato "sulhu "don kyakkyawon ɗabi'u irin nasu.

 

Gudummuwar da sarkin katsinan Gusau ya ba yar a (1867m/1282h-1877m/129h) Malam muhammadu modibbo an samu kwararar baƙi Da ƙungiyoyi daban daban wanda hakan ya sa haɓakar garin Gusau a cikin ƙanƙanin lokaci. Zuwan Bature da Turawa a ƙasar Hausa ya sa an shimfiɗa tsarin makarantun boko wanda ya haifar da samuwar wasu al’adu. Kwatsam! anan sai ga shariar musulun ci ta sake kunnu kai ta gwadaɓe tajdidin wannan lamari, shi ma ya ƙara kawo canje-nacanje na Alheri a Ahlin mutanen garin Gusau amatsayin su na babban birnin jiha.

 

Garin Gusau tana da babbar masarauta guda ɗaya(1) tana da wakilan uwayen ƙasa guda goma sha uku (13) ƴan majalissa sha takwas (18) sarautun fada kuma akwai kimanin ɗari ɗaya da huɗu (104) Masallatan juma’a ashirin da (23)kananan makarantun boko sittin da huɗu (65) mutsakaita kuma arba'in da uku (43). Haka kuma akwai kasuwanni guda uku (3). Daga lokacin da aka kafa garin Gusau an yi sarakuna da dama kamar haka:1-Malam Muhammadu Sambo (1806-1827) 2-Malam Abdulƙadir (1827-1867) 3-Malam Muhammadu Modibbo (1867-1976) 4-Malam Muhammadu Tubari (1876-1887) 5-Malam Muammadu Giɗe (1887-1900) 6-Malan Muhammadu Murtala (1900-1916) 7- Malam Muhammadu (1916-1917).

 

Sai waɗanda suka yi sarautar  Gusau ba daga gidan Malam Sambo ba, sunhaɗa da; 1-Malam Umaru malam (1916-1929) 2-Malam Muhammadu  Mai Akwai (1929-1943).3-Usman Ɗan samaila(1943-1945) 4-Ibrahim Marafa (1945-1948) 5-Muhammadu sarkin kudu (1948-1951) 6-Alhaji  Sulaiman isa (1951-1984). Daga nan kuma sai sarautar ta sake dawowa gidan bayan wannan tsawon lokacin, inda ta faɗa a kan 1- Alhaji Muhammadu Kabiru Ɗanbaba (1984-2015) 2- Alhaji Ibrahim Bello (2015-to date) Ataƙaice dai wannan shi ne tarihin garin Gusau tun bayan ta sowa daga ƴandoto.

 

3.4 NAU'O'IN' MAKARANTUN MUHAMMADIYYA.

A nan ana maganar hanyayoyi ne kamar yadda aka ambaci sunan da "Muhammadiyya "wato hanyar da ake bi wajen aiwatar da karatun Musulunci ko muce na Addinin Musulunci, wanda Annabi Muhammadu, shi ne ya zo da wannan Addini, Dan haka ne ake kiran karatu da "karatun muhammadiyya.  

 

Haƙiƙanin gaskiya akwai hanyoyi da nau'o'i da dama da ake bi wajan karatun Addinin Musulunci a ƙasar Hausa, kuma cikin su duk hanyar da mutum ya bi ko ya tashi ya samu kansa a ciki to zai iya cimma duk wani matsayi dangane da karatun ko ilimin Addinin Musulunci. Akwai Nau'i daban daban na makarantun Addinin Musulunci kamar haka:

 1-Makarantun zaure

 2-Akarantun Allo /Tsagaya

 3-Makarantun isalamiyya.

 

3.4.1 Makarantun Allo /Tsangaya

Makarantar Allo ita ce tsohuwar hanyar koyo da koyerwa a ƙasa Hausa a manyan garuruwa kamar Kano da Katsina da Zariya, a Kano ana kyautata zaton an kafa makarantu kusan shekaru ɗari shida da sittin da suka shuɗe abaya, zamanin Sarki Yaji da Tsamiya (1349-1385) wato a daidai lokacin da Fulanin Wangarawa suka zo garin Kano .

 

Katsina kuwa Ana ganin tun shekaru ɗari shida da sittin da uku a baya da suka wuce wato a zamanin Sarki Muhammadu Korau (1384-1398) lokacin Sheikh Abdurrahaman Zaite da jama’arsa suka je Katsina. Wannan makaranta a cikinta ake koyon karatu da rubutu, da kuma Haddace Al-Ƙurani baki ɗayan sa, Malaman Makarantar allo su suke rubuta Ƙur'ani ko dai da ka, ko kuma ta hanyar mai-da-kama. Makarantun allo makarantu ne masu tsari irin nasu, a kan kai yaro makarantar allo idan yaro ya kai shekaru shida (6) ko bakwa (7) da haihuwa wanda idan namiji ne an yi masa kaciya (bante) idan a ka kai yaro to shi ke nan yaro ya zama ɗan makaranta wanda ake kira Almajiri.

 

A makarantar allo ɗalibai kala biyu ne a kwai waɗanda ke kwana a makaranta akwai kuma waɗanda su ke komawa gidajen iyayensu su kwana, kamar dai yanzu yadda aka da tsarin makarantun kwana da kuma jeka-ka-dawo a makarantun boko.


Lokutan karatu:

Akwai lokutan da ake gudanar da karatu amakarantun tsangayu da na Allo kamar haka;

1.       Ana karatu tsakiyar dare wato (tayi) kawai za a tayar da Almajirai suna tsakiyar bacci cikin dare ko gab da Asuba  wanda zai kai har bayan Asuba ko har gari ya waye, amma yanzu ba kasafai ake samun wannan ba.

2.       Lokacin karatu na biyu shi ne idan hantsi ya yi sai a zauna wasu kuma awannan lokacin ne suke tafiya bayan gari wato ƙiskali ɗaki ne da ake yin shi da kara da yayi a bayan gari ko cukin gonaki.

3-      Zama na bayan Laa'sar

4-      Sai zama na ɗare.

Tsarin  Koyon  Karatu

1-    GWAJI: Shi ne mataki na farko da ake ɗora sabon Almajiri akai ana koya masa Fatiha zuwa Alamtarakaifa. Galibi yara sukan iya wannan surori da ka wasu ma sama da waɗannan, alhali kuwa ba su ma fara riƙe allo ba.

2-    BABBAƘU: A wannan mataki ne yaro ko yarinya ke fara amfani da allo, matakin babbaƙu kamar yanda sunan ya nuna mataki ne na sanin baƙaƙen Alƙur’ani.

3-    FARFARU: Shi ne mataki na uku wanda ake koyawa almajiri laƙantar wassulla, a nan akan mai da yaron da ya kammala sanin ɗaiɗaikun haruffa a matakin babbaƙu baya, ma’ana sai a sake rubuta masa Ta’awizi da Basmalah zuwa Suratul Fili tare da wasullah. Matakin farfaru yana da wahala domin kuwa a nan ne yara da yawa kan jima basu ficeshi ba.

4-    Hajjatu: Bayan yaro ya laƙanci sanin baƙaƙe da kuma iya karantasu da wasullah, Sai matakin Hajjatu Malami kan yi la’akari da cewa a yanzu idon yaro ya buɗe, don haka sai ya biya masa kamar layi ɗaya ko biyu na allonsa tare da ɗora yatsan yaron akan kalmomin da ake biya masa.

5-    Darasu: Almajiri kan je wannan mataki ne, ya yin da idan ya yi ƙwari wajen haɗa baƙaƙe da ta dasu, yara masu hazaƙa kan yi ƙoƙarin karanta guraren da ma basu kai ba a cikin Alƙur’ani.

6-    Gardi: Shi ne makarancin da ya wuce shekara 25, kuma karatunsa ya yi nisa, kuma a wannan mataki ne ake haɗa harda ta zauna daram.

7-    Satu: Kalmar barebari ce da ke nufi iya rubuta baƙaƙen Alƙur’ani bayan an hardace, makaranta a tsarin tsangayu ba sa fara rubuta Alƙur’ani har sai sun kai matakin yin satu.

8-    Alaramma: Matsayi ne na wanda ya hardace Alƙur’ani har ma ya rubuta shi, ma’ana dai ya laƙanci duk wasu ilimai da luggogi na Alƙur’ani, kuma har yana da wasu dunƙulallun kalmomi da makaranta ke amfani da su, na hisabi da makaranta Alƙur’ani ke amfani da su, dan tantance adadin kalmomi ko baƙaƙen Alƙur’ani.

9-    Gwani: Shi ne matakin ƙoli cikin azuzuwan makaranta a tsarin tsangayu, makaranci kan zama gwani bayan ya kai matakin gardi har zuwa matakin alaramma, bayan alaramma ya yi shekaru da yin fice a fagen Alƙur’ani, makaranta kan ayyana shi a matakin gwani a cikinsu.

10-       Gangaran: Akwai saɓani a wasu lokutta wurin wasu malamai a tsakanin gwani da gangaran wanne ne a gaba? Wannan ya biyo bayan wani shahararren makarin zance “Gangaran kafi Gwani” ala ayyi halin gwani shi ne mafi karɓuwa a azuzuwan makaranta, amma fa wanda makaranta ke kira da gangaran to ya fi gwani.

 

3.4.2  Makarantun Zaure

A nan ya zama wajibi mu kalli maa'nar zaure shin mene ne "Zaure"? Zaure wani ɗaki ne wanda ake yin shi a farko shigowa gida kuma dole sai an bi ta zauren nan ida za a shiga cikin gida. Ga al’adar Hausawa zaure ɗaki ne mai matuƙar muhimmanci mafiyawan malaman zaure suna karantar wa ne a zaure kuma mafi yawansu dattijai ne haka nan kuma mafi yawan masu ɗaukar karatun a zaure za a cimma magidanta ne ba kamar makaran tun allo ba.

 

3.4.3 Makarantun Islamiyyah

Tarihi ya nuna cewa, karatun Islamiyya ya shigo ƙasar Hausa a cikin ƙarni na 20, wajen shekara ta 1930. Wannan ya nuna cewa karatun Islamiyyah bai daɗe da shigowa ba a ƙasar Hausa ba ganin waɗannan shekaru ba su da yawa idan an kwatanta da hasashen shigowar addinin Musulunci a ƙasar Hausa. Ba ko shakka, a makarantun Islamiyya ne aka fara koyar da yara da matasa ‘yan makaranta karatun Alƙur’ani ta hanyar karatun tajwidi. Abin da ya bambanta karatu a makarantun allo da karatu a makarantu Islamiyya shi ne, a makarantun allo yara na karatunsu da allo ne (wanda massaƙa suke sassaƙawa da icce) har sai sun kai Suratul Amma ko Tabara, suna ɗaukar karatu da bita sannan Malamansu su riƙa barinsu suna zuwa makaranta da Alƙur’aninsu, don karantawa. Amma makarantun Islamiyyah kuwa, ana faraway yara karatunsu a kan allon bango irin na makarantun boko, su kuwa ɗalibai suna rubutawa a cikin littafinsu kamar yadda ake yi a makarantun boko. Don haka bikin yaye ɗaliban makarantun Islamiyya ba ya da wasu al’adun Bahaushe masu yawa a ciki. Don haka, za mu danganta tarihin samuwar makarantun Islamiyyah da zuwan Sarkin Kano, Alhaji Abdullahi Bayero ƙasar Masar.

Sun ziyarci ƙasar Masar, inda aka shirya da wani Balarabe mai suna Abu Sa’ud cewa zai zo Kano ya tsara yadda za a gudanar da irin wannan makaranta da ma’aji Suleimanu ya shawarci Sarki a kan a kafa ta. To da Abu Sa’ud ya iso Kano sai aka yi amfani da waccan Makaranta ta Elementary ta ƙofar kudu, aka buɗe ajin manya don a tafiyar da irin wannan tsari na Misirawa, sai ya zamana an ɗauki ɗalibban wannan makaranta ta safe su ne suke komawa da yamma, ana karantar da su Arabiyyah da koyar da addinin musulunci. (Sufi: 1993:217).

 

Shi Malam Wada wanda yake yin Headmaster sai ya dawo ya ci gaba da tafiyar da wannan makaranta ta boko ta safe tare da waɗancan Malamai nasa, su Malam Baƙo Bauchi, da Malam Abba (Ka), akwai kuma Malam Umaru Ɗan Madaki, sai Malaman Arabiyyah, Malam Ɗan Amu da Malam Nasiru Kabara, a lokacin ana kiransa Malam Nasiru Namagangara, da kuma Malamin sa’ana Malam Alhaji na Soron ɗinki.

 

Ita kuwa wannan makaranta ta yamma ta Arabiyyah (Islamiyyah), wani Bazazzagi Almajirin Ma’aji Suleiman wanda aka fi sani da M. Abubakar Na-Wali ko M. Abubakar Maisaje, shi ne yake shugabancinta. Ana karantar litattafan fiƙihu kamar As’halul Masaliki da Durusun Nahawiyya, da wani littafin koyan Larabci da ake kira: “Ƙira’atul Asarariyyah”. Ya yin da Bamisire, yana koya wa waɗannan yan makaranta wasannin motsa jiki, amma da harshen Larabci, ana yin guje-guje da tsalle-tsalle a kowace ranar Alhamis da yamma, duk kuwa kowane yaro yana sanye da farar yar taguwa mai gajeran hannu mai wuyan kwala, da wani ɗan gajeran wando fari, kamar yadda Sufi (1993:218) ya nuna.

 

Ana yin wannan guje-guje ne da tsalle-tsalle a wannan ƙaton sararin da ake cewawa da shi filin gawo, wani lokaci ma sai ɗalibai su dinga zagaye wannan ɗaurin guga na Filin Gawo da ake cewa da shi “Soron Zauna Lafiya” wanda aka faɗe shi a baya, sai su riƙa zagayashi a guje. A cikin waɗannan daliban makarantar akwai wani ƙaton yaro ɗan sarkin Muri ana ce da shi Misa. A wani lokaci kuma sai wannan Balarabe ya dinga koyawa waɗannan yara rawa irin ta ‘yan sanda ko soja, sai yaran su dinga tafiya suna ɗaga ƙafar hagu da ta dama, shi kuma yana cewa SHIMAR YAMI, wai hagu da dama, kenan idan sun yi yar tafiya sai yace ILAL HALAF ILTAFIT sai yaran su juya baya suna cewa WAHIT NIN sai kuma ya ce ‘ILAL AMAM SIR” sai yaran su miƙe da tafiya darkwai sai ya ci gaba da faɗin SHIMAL YAMIN. Haka za a ta yi sai lokacin da yace a tashi daga wannan rawa. 

 

3.5 NAƊEWA

Wannan babi ya kunshi muhimman Abubuwa kamar samuwar ko kafuwar makarantun allo a garin Gusau da kuma nau'o'in makarantu Muhammadiyya da muke da su da kuma irin tsarin karantarwarsu da matakin da yaro ya ke kaiwa kafin a sashi a makarantar allo ko islamiyya.

 

BABI NA HUƊU

BIKIN SAUKAR ALƘUR’ANI A GARIN GUSAU

4.0 SHIMFIƊA

Kamar yadda babin da ya gabata aka yi bayanin ma’anar kalmar biki tare da kawo wasu ire-iren bukukuwan Hausawa tare da yin tsokaci game da kalmar gari da taƙaitaccen tarihin garin Gusau. A wannan babi na huɗu za a kawo shimfiɗa da asalin bikin saukar Alƙur’ani tare da bayanin waɗanda suka fara aiwatar da bikin. Haka kuma za a yi bayanin yadda bikin saukar Alƙur’ani yake a da, sannan yaɗuwarsa da bunƙasarsa, sannan kuma an kalli irin tasirin da zamani ya yi game da bikin saukar Alƙur’ani.

 

Bugu da ƙari, an kawo bayani dangane da irin rawar da uwaye, da Malamai da ɗalibai ke takawa duk a wajen bikin saukar Alƙur’ani, daga ƙarshe a zo da naɗewa.

 

4.1 ASALIN BIKIN SAUKAR ALƘUR’ANI

In ana magana kan asalin bikin saukar Alƙur’ani to abin da ya kamata a sani nan shi ne, a sani shi, Allah ya saukar ma Annabi Muhammad (SAW) Alƙur’ani mai tsalki ta hannun Mala’ika Jibril (AS), “Manzon Allah (SAW) ya kasance idan Alƙur’ani ya sauka gare shi yakan karantar da Sahabbai abin da ya sauka, kuma ya umarce su da su rubuta shi. Ubangiji maɗaukaki ya yi wa Annabi da Sahabbai umarni da su karanta Alƙur’ani kuma su yi aiki da shi. Wannan ya sa sahabbai da yawa sun haddace Alƙur’ani a ƙirajensu (K/Nasarawa 2006:4). Da wannan ne mu ke cewa bikin Saukar Alƙur’ani ya samo asali ne tun zamanin Sahabban Manzon Allah (SAW); saboda “Sayyidina Umar yardar Allah ta tabbata a gare shi, lokacin da ya haddace Suratul Baƙara ya yanka raƙumi domin nuna godiyarsa ga Allah da wannan ni’imar” da ya yi masa” (Tafsirin Imamu Kurɗabi).

 

Da wannan ne muke jingina hujjar cewa bikin Saukar Ƙur’ani ya samo asali ne tun zamanin sahabbai, kuma kasancewar Addinin musulunci ya na da tsarin da Annabi Muhammad (SAW) ya ɗora shi bisa ga umarnin da Allah ya yi masa da koyarwarsa da kuma koyarwar Sahabbansa, domin ya faɗi cewa a bi Allah da kuma shi (Annabi Muhammad (SAW) da kuma Sahabbai. (Sahihul Bukhari Ɓol. 4, Hadish No. 645) (Ƙur’an 4 ɓerse 136).

To daga nana abin ya cigaba har ya kawo ga al’ummar Annabi Muhammad (SAW) kuma har gobe ana gudanar da bikin saukar Alƙur’ani mai girma a cikin duniya, sai dai ya danganta da irin yadda ake aiwatar da bikin ta hanyar al’adar al’ummar kowane wuri da ƙarfin tattalin arzikinsu da kuma sauyin da zamani ya kawo masu.

 

4.1.1 Waɗanda Suka Fara Aiwatar da Bikin Saukar Alƙur’ani

Kasancewar Annabi Muhammad (SAW) shi Allah ya saukar ma Alƙur’ani ta hannun mala’ika Jibrilu (AS) kuma Annabi (SAW) yana karantar da sahabbansa ya kuma umarce su da su rubuta shi, dan haka kafin kowa ya fara sanin ƙur’ani bayan Manzon Allah, to sahabbansa su suka fara sanin Alƙur’ani da haddace shi, domin ko akwai wasu daga cikin sahabbai da suka haddace Alƙur’ani “Mahaddata Alƙur’ani cikin sahabbai  Muhajirai sun haɗa da halifofi huɗu Sayyidina Abubakar, Sayyidina Umar, Sayidina Usman da Sayyidina Aliyu da “Dalha da Sa’ad da Ibn Mas’ud da Huzaifa da Salim da Abuhuraira da Abdullahi bn Sa’ad da A’isha da Hafsa da Ummu Salma (RA). A cikin mutanen Madina wato Ansar an samu Mahaddata Alƙur’ani cikin Sahabbai waɗanda su ka haɗa da Ubaidatu bn Samit da Mu’az (Abu Halima) da Mujammi’i bn Jariya da Fudhala bn Ubaida da Muslama bn Mukhalad. Kodayake wasunsu sun kammala haddarsu ne bayan wafatin Annabi (SAW) akwai kuma waɗanda da yawa da suka haddace Alƙur’ani cikin sahabbai (RA) ko da yake su suka yi fice da shahara domin riwayoyin kira’o’i goma na Alƙur’ani na komawa gare su”. (K/Nasarawa 2006:9).

 

Da wannan ne za a tabbatar da cewa kafin kowa ya fara bikin Saukar Alƙur’ani to Sahabban Manzon Allah (SAW) su suka fara aiwatar da bikin saukar Alƙur’ani har ya kasance ake koyi da su domin duk abin da suka yi sunna ne kuma shari’a ta yarda da shi tamkar yarda da hadisin Annabi (SAW) ne. Kuma bikin saukar Alƙur’ani ya cigaba bayan wucewarsu. Kuma wannan ne ma ya sa ake kallon wanda ya sauke ƙur’ani wani babba a cikin al’umma, baya ga irin hidima da uwaye ke yi na nuna jin daɗin ɗansu ya sauke Alƙur’ani, ‘yan uwa da abokan arziki na zuwa wajen taya murna da sauran mutane makusanta.

4.1.2 Samuwar Makarantun Al-Ƙur'ni A Garin Gusau

Kasancewar masarautar Sakkwato ta kafu ne daga baya-bayan nan idan andanganta ta da masarautar gobir da zamfara da kebbi hakan ya sa, tarihin Al-ƙur'ani da ilimi yana koma wa ga malaman ‘Yandoto.

Wani muhimmin abu da ya ƙara haɓɓaka sha’anin Malamanta da samuwar Malamai ya ci gaba da haɓɓaka, sannu a hankali shi ne, samuwar Daular Sharifai a ‘yandoto wadda ta zama matattara ta gaggan Malamai masu ƙoƙarin yaɗa ilimin Addinin musulunci, Lamarin da ya haifar da yawaitar gaggun Malamai na kowane fanni a wannan daula ta jahar Zamfara. Ita wannan daular Yahaya Ɗannafsuzzakiya ɗan Aliyu Zainul Abidina ɗan Sayyadina Hussaini ɗan Sayyadina Aliyu Bn Abi Thalib daga wajen Nana Faɗima, shi ya ka fata. Sharif Yahaya ya kafa daular ne a ƙarni na takwas miladiya. Kuma yana ɗaya daga cikin Malaman Imamu Malik. Wannan ya taimaka wajen kakagidan da Mazhabar Malikiya ta yi a ƙasashen Hausa, kamar yadda Ibrahim (2009:16) ya nuna, daular ta gudana har zuwa zamanin Sheikh Usmanu Ɗanfodiyo.

 

Kasancewar garin Gusau gari ne mai cike da baƙi musamman ta ɓangare makaranta tarihin kafuwar makarantun Al-ƙur'ani bai ɓuyaba, dan kuwa, Akwai manya-manya makarantu acikin birnin Gusau kamar haka:

1.     Makarantar Malam Almu Ɗandurmi

2.     Makarantar Malan Yahuza Filin Nayawo

3.     Makarantar Malam Nakanoma Sabon Fegi

4.     Makarantar Malam Idi na Mal. Mukhtar Kofar Jange

5.     Zawiyyar Sheikh Balarabe, Gusau

6.     Zawiyyar Malam Aliyu Mai Kanti Shiyar Mayana

7.     Makarantar Malam Fari Ɗandutsen Gabas

8.     Makarantar Malam Hamisu, Kusa da Gidan Makaranta

9.     Makarantar Malam Ango Lungun Malamai

10. Makarantar Malam Musa mai Almajirai Tudun Wada

11. Makarantar Gidan Malam Nadango Kanwuri, Gusau

12. Makarantar Malam Ibrahim Nagangare

13. Makarantar Malam Nazoma Albarkawa

14. Makarantar Malam Lawali Jibiya, Bakin Silima

 

4.2 YADDA BIKIN SAUKAR ALƘUR’ANI YAKE A DA

Tun zamanin sahabbai ana gudanar da bikin saukar Alƙur’ani ne ta haddace wani ɓangare ba wai sauke shi gaba ɗaya ba, kuma bayan wucewarsu abin ya ci gaba da gudana a haka, domin ko in aka ce yaro ya zo sabbi to akwai ɗan dafe-dafen da za a yi domin ana ganin ya taka wani matsayi da kuma jin daɗin da uwaye ke ji harma ana ma saukar sabbi kirari da cewa “Sabbi Saukar Mata” (Bunza 2009). Wai kamar in mace ta iya sabbi ta sauka, sannan haka aka cigaba da koyon Alƙur’ani in an zo kowane izu da kwai abin da ake yi na farin ciki, to amma in aka sauke Alƙur’anin gaba ɗaya to irin bikin da ake yi ya banbanta da na baya, (wato kafin a sauka).

 

Sannan kuma yadda ake aiwatar da bikin ya banbanta domin ko kowane gari suna da irin yadda suke yin bikin su, amma ga yadda wani Malami ya yi bayanin yadda ake bikin saukar Alƙur’ani a da kamar haka: “Idan mutum ya sauka ana ba malami tuwo misalin malmala biyar ko shidda, da kuma dawo huɗu ko biyar kuma ana ba shi masa guda talatin ko arba’in ko hamsin sannan kuma da goro talatin ko arbi’in ko hamsin daidai gwargwadon karfin gidan wanda ya sauke alƙur’ani. Sannan kuma ana ba Malamin kai na bisar da aka yanka da ƙafafu, kuma ana bashi kuɗi dai dai gwargwado. Ranar bikin za a tara jama’a daga ɓangare na ‘yan uwa da abokan arziki domin su zo su shaidi cewa lallai wannan yaron ya sauka, sannan kuma ‘yanuwan yaron da ya sauka na ba da gudummawa domin taimako ga wannan bikin saukar Alƙur’ani. Bayan haka ana rarraba abinci ga waɗanda suka halarci taron bikin saukar Alƙur’ani da abin sha.

 

Bugu da ƙarim ana yi ma wanda ya sauka ɗinkin sutura da suka haɗa da babbar riga da tagguwa da wando a naɗa masa rawani ya fito kamar wani Malami domin ana yi masa kallon ya fara taka wani mataki na shiga sahun malanta. Sannan sai ya karata Fatiha da wani ɓangare na Alƙur’ani, wato Farkon Suratul Baƙara sai kuma Malamai su yi masa nasiha, bayan an gama nasihar sai shi yaron da ya sauke Alƙur’ani ya hau saman durum ko shigehwa domin ya yi ma mutanen da suka zo shaidar wannan bikin saukar Alƙur’ani watsin sababbin kuɗi da nuna murna da jin daɗinsa a wannan rana, da kuma jawo hankali ‘yan’uwansa da abokansa da basu sauka ba, da su dage su zage dantse don suma su ga sun sauka” (Malam Usman Tambuwal, 2021).

 

Kasancewar a da ana samun ƙarancin masu sauka shi ya haifar da yin bikin a gidajen waɗanda suka sauka, amma dai a hankali har ya dawo makaranta ke shirya yadda za a yi bikin, kuma a harabar makaranta, sai dai uwaye, da yan uwa su zo makarantar da yaran su suke don shaidar ganin bikin saukar alƙur’ani da ɗansu ya yi.

 

4.3 YAƊUWAR SA DA BUNƘASAR BIKIN SAUKAR ALƘUR’ANI A GARIN GUSAU

Kasancewar Al’amarin karatun Alƙur’ani da bikin saukar duk abubuwa ne masu asali tun zamanin Annabi Muhammad (SAW) da sahabbansa, to amma anan Afrika kuwa, yaɗuwar karatun Alƙur’ani ta bayyana ne a hannun Murabiɗun ma’ana (Mayaƙan da ke dako kan iya kokin musulmi) bayan zuwan Uƙuba bn Nafiu, a duk sannanin da waɗannan mayaƙa suka taru za ka samu babu abin da suke yi sai karatun Alƙur’ani. (K/Nasarawa: 2006:5)

 

Wannan shi ne asalin samuwar cibiyoyin Alƙur’ani a Afrika da kuma dalilin da ya sa tsangayun Alƙur’ani ke keɓanta kansu nesa da jama’a. Kamar kuma yanda zamu ga ita kanta kalmar ta tsangaya (Sangaya/ musanghi) a wurin barebare tana nufin masu jira ko tsammani, wanda ya yi daidai da masu ribaɗi ko murabiɗun a wancan lokacin. A taƙaice dai karatun Alƙur’ani a tsarin tsangaya, ga manya ko ƙananan yara, ya samo asali ne daga zamanin Annabi da sahabba da mabiyansu. (Sanusi Yuguda Kofar Nasarawa 2006:6).

 

Amma in ana maganar bunƙasarsa da yaɗuwar bikin saukar Alƙur’ani sai a fara kallon a nan najeriya duk wanda ake so ya san Alƙur’ani ya kuma yo karatunsa, a wancan lokacin to dole sai an kai shi ƙasar Barno (Maiduguri) domin zamowar ƙasar wata babbar cibiya ta Alƙur’ani. Kuma in mutum ya sauke ya dawo garinsu, shi ke nan sai a yi masa biki, daga nan shi ma ya zama malami sai ya cigaba da koyar da wasu don su ma su samu ilimin Alƙur’ani ta hannunsa.

 

Amma yaɗuwa da bunƙasar bikin saukar Alƙur’ani to yana da alaƙa da zuwan zamani da canza salon koyarwa daga makarantun allo zuwa makarantun Islamiyyah, ta la’akari da wancan lokacin ana amfani da allo wajen rubutawa da karanta ma yara, amma dawo da tsarin Islamiya sai kawai aka fara amfani da ƙur’ani cikakke sakamakon bunƙasar maɗaba’a da yawaitar Alƙur’ani bugun dutsi (Ɗan Misira) a ka rinƙa karantar da yara, in sun dawo su biya aka fahimci sun iya sai a yi masu ƙari, ta haka abin ya ci gaba da wakana, in yaro ya kai izu biyu sai ya ce ma uwayensa a fanso (sayo) masa izu biyar. Haka dai har yara su kammala izu sittin, to daga wannan lokacin sai a ce yaro ya yi saukar zuƙu, ma’ana yana iya karanta Alƙur’ani tare da dubawa.

 

Kuma wannan ba ƙaramin yaɗuwa da bunƙasa karatu da bikin saukar Alƙur’ani  ya yi ba, domin ko a faɗin jihar Zamfara garin Gusau kaɗai yana da yawan makarantun da sun fi guda ɗari da hamsin (150) da duk bayan shekara sai an gabatar da bikin sauka ma ɗalibai kuma makarantar Zawiyyar Sheikh Balarabe Gusau a duk shekara ana iya samun ɗalibai sama da yara ɗari uku da ake ma bikin saukar zuƙu, bayan kuma ana iya samun Alarammomii wato waɗanda suka haddace ƙur’ani ba tare da dubawa ba a ƙalla yara arba’in zuwa hamsin (40-50).

 

4.4 TASARIN ZAMANI

Kafin kawo bayanin tasirin zamani to ya kamata mu ɗan haska ma mai karatu game da kalmar zamani. “Asalin wannan kalmar ta aro ce daga Larabci wato ZAMAN,  dake nufin lokaci. Hausawa suka ara, suke amfani da ita daidai da ma’anarta ta larabci. A wajen wasu zamani shi ne sabon abu, wannan dalili ne ya sa duk wani abu da ya faru ya wuce sai a ce ai wannan tsohon yayi ne. Haka kuma wasu na fassara zamani da ikon Allah, musamman tsoffi. Mai yuwuwa wannan na da alaƙa da yadda idan sabon abu ya shigo yake game dukkan al’ummar da ke amfani da shi musamman matasa. Saboda haka zamananci na nufin lokaci ko yayi. (Ɗantumbishi, p 76-77).

 

Amma game da irin tasirin da zamani ya yi dangane da bikin saukar Alƙur’ani musamman a garin Gusau to ana iya cewa irin yadda ake yin anko (ɗinki kala ɗaya), tun daga masu bikin Saukar Alƙur’ani da kuma ahalinsu na kusa da na nesa. Sannan kuma ana yin hotuna da ake sanyawa a waya (stiker) da kuma Kalanda (clander) da ake sanyawa a ɗaki, ga mai hali har littafi ake yi mai ɗauke da hoton wanda ya sauke Alƙur’anin ko kuma mai saukar Alƙur’anin. Bugu da ƙari ana amfani da wayoyin hannu tafi da gidanka ana ɗaukar hotuna, sannan kuma ana haɗa maza da mata wajen taron, tun daga yaran da za a yi ma bikin da kuma ‘yan uwansu maza da mata manya da yara. Sannan kuma ana gayyato manyan mutane da malamai, da ma’aikatan hukumomin gidajen radio da na Talabijin (TƁ) irin su Gamji da sauransu. Ana rarraba abubuwan lashe-lashe da tanɗe-tanɗe da na ci da sha ga baƙin da aka gayato. Sai kuma wasu ‘yan shirye-shiye da ake tanada da suka haɗa da was an kaikayo da ɗaliban makaranta ke aiwatarwa domin nuna ma al’umma muhimmancin ilimin da suka koya.

Sauƙar Karatu

Hoton ɗalibai maza masu sauka

  Sauƙar Karatu 

Kalandar Malamai da ɗalibai maza da mata masu sauka

 

Sauƙar Karatu

Sauƙar Karatu

Hoton ɗalibai mata masu sauka

 

Sauƙar Karatu

                                     Hoton Malami mai jawabi a wajen bukin sauka Alƙur’ani

 

4.5 RAWAR DA IYAYE KE TAKAWA

Rawar da Iyaye ke takawa wajen Gudanar da bikin saukar Alƙur’ani ta ‘ya’yansu. A nan za a kalli abin tun daga farko, wato tun daga lokacin da iyaye suka sa yaro makaranta za a ga cewa sun bayar da gudummawa ta hanyar tanada masa abubuwa irin su littafai kuɗin mashin idan ba kusa yake da makaranta ba, da ba yaro kuɗin tara, wasu iyayen na dafa ma yaron abinci ne saboda tsawon lokacon da yaro ke yi a makaranta.

 

Haka, ɗinkin makaranta da sauran abubuwa, kama da biyan kuɗin wata, laraba da sauran kuɗaɗen da makaranta za ta buƙata daga wajen iyayen yara. Ta gefen bukin saukar Alƙur’anin kuma, za a tarar cewa tun daga lokacin da makaranta ta tabbatar da cewa yaronka ya sauka za a fara yin zama na musamman a tsakanin uwayen yara da malaman makaranta, domin tsara yadda za a tunkari hidimar bikin. A ƙarshe kuma za a tsayar da adadin kuɗin da ko wane uba zai bayar na game da ɗansa 

 

Wasu uwaye kan tanadar da bisa (dabba) da za a yanka ma yaro, wani lokaci ana kai wani sashen naman bisar makaranta, wannan ya danganta da zarafin iyayen wanda ya sauka. Haka kuma, iyaye kan dafa abinci don tarbar baƙi wato ‘yan ‘uwa da abokan arziki na kusa da na nesa. Wasu iyayen na yi wa ‘ya’yansu kalandu da sitika da sauran ababen da za a raba ga waɗanda aka gayyata domin nuna farin ciki, murnar baiwa. 

 

Sannan kuma iyaye na yi ma ‘ya’yansu ɗinkin kalar tufafin da hukuar makaranta ta ayyana, wanda za a yi amfani da su ranar buki.

 

4.5.1 Rawar da Malamai ke Takawa

Kasancewar Malami na da muhimmanci ya sa aka ce “in yaro ya hango malaminsa da kaya, kuma ga mahaifinsa da kaya, to ya karɓi kayan Malaminsa ya kyale babansa, (Littafin Ta’alimin Muta’allim).

 

To amma in ana maganar game da irin rawar da Malamai ke takawa a wajen bikin saukar Alƙur’ani to ɗaliban makarantarsa, ya fara ne, daga koyar da yaran tun daga farko har ya zuwa lokacin da yaran suka sauka. Kuma daga cikin irin rawar akwai shirya wurin da za a gudanar da walimar bikin saukar Alƙur’ani, inda makaranta ta tanada, kuma suke da haƙƙin gayyato manyan malamai da manyan baƙi da ake son su samu halartar bikin saukar Alƙur’anin.

 

Su ke gabatar da duk wasu karance-karance da jawaban da manyan baƙi za su gabatar a wurin, sannan kuma suna tanadar kayan tanɗe-tanɗe da lashe-lashe da za su raba ma baƙin da suka gayyato. Haka Malaman nan su ke gayyato ‘yan gidan rediyo da a wajen domin ɗaukar bikin saukar a tsakanin al’umma.

 

A ƙarshe bayan taro ya tashi malamai ke tattara duk kayan da aka yi amfani da su tare da maida ma masu su da kuma yi masu godiya sai kowa ya tafi gidansa. (Sheikh Munnir Muhammad 2021)

 

4.5.2 Rawar Da Ɗalibai Ke Takawa

Rawar da ɗalibai ke takawa a wajen bikin saukar Alƙur’ani ta fara ne tun daga wurin da suka dage suka mai da hankali ga karatun su har Allah ya kaisu lokacin da aka kai ga saukar Alƙur’ani, domin sau da yawa yara da dama na fara karatu tare, amma ba kowannen su ke samun damar kai ga matsayin kammalawa ba, domin ko abin baiwa ne. Haka kuma, zuwa makaranta ba dare ba rana ruwa da iska ba su hana su, ita ma wata horewa ce ga Allah. Yaran su kan gayyato abokansu da kuma yi masu tanadin abin da za su ba su bayanan kammala bikin. Sannan kuma suna taka rawa a wajen biki na yin karance-karance da makaranta ta tsara domin ɗaliban su gabatar a bainar jama’a.

 

4.6 NAƊEWA

A wannan babi mai suna bikin Saukar Alƙur’ani a garin Gusau, an yi bayani game da asalin bikin saukar Alƙur’ani tare da waɗanda suka fara aiwatar da bikin saukar Alƙur’ani. Haka kuma, an kawo bayanin yadda bikin saukar Alƙur’ani ya ke da, da kuma yaɗuwarsa da bunƙasar bikin saukar Alƙur’ani a garin Gusau. Bugu da ƙari, an kawo tasirin zamani a kan bikin saukar Alƙur’ani, tare da bayanin irin rawar da iyaye, da malamai da su kansu ɗaliban ke takawa a wannan fage.


BABI NA BIYAR

SAKAMAKON BINCIKE

5.0 GABATARWA

Kasancewar wannan babi na biyar shi ne babi na ƙarshe, an taɓo muhimman abubuwa kamar haka, bayan gabatarwa anyi sharhi akan sakamakon bincike, da shawarwari daga ƙarshe naɗewa.

 

5.1 SAKAMAKON BINCIKE

Kasancewar duk wani bincike da aka gabatar dole ne a ƙarshe a samu samakon bincike. Wannan bincike an yi ƙoƙarin gano asalin kalmar biki, da kuma sauka, da Alƙur’ani da kuma waɗanda suka fara gabatar da bukin saukar Alƙur’ani, haka kuma an kawo wasu sunaye da ake yi ma bukin saukar Alƙur’ani. Bugu da ƙari an yi bayani irin rawar da iyaye da Malamai da kuma ɗalibai ke takawa wajen bukin saukar. A ƙarshe an nuna yadda ake aiwatar da bukin saukar Alƙur’ani jiya da yau a garin Gusau

 

5.2 SHAWARWARI

Duk wani aiki da mutum ya gabatar ko ya gudanar, akwai buƙatar shawara daga gareshi domin cin gajiyar wannan shawarwari ga al’umma, saboda haka ina ba duk wanda Allah ya baiwa ikon zai yi nazari a wannan fanni shawara cewa, in dai ya ci karo da wannan kundin kuma har binciken sa yana da alaƙa da wannan da ya yi ƙoƙari ko suyi ƙoƙarin ɗorawa daga inda wannan bincike ya tsaya, kar su ce su kwashe kawai, domin ko yin hakan baya taimakawa a fagen nazari, kamar yanda aka zaƙulo wannan taken na bikin Saukar Alƙur’ani a Garin Gusau a ka yi ƙoƙari har aka tattaro bayanan da suka gina wannan kundi, ya zama abin karatu ko nazari ga yan uwa na ɗalibai, to lallai suma ya zama wajibi su dage don su samar da wani abu mai amfani ga al’umma.

 

Sannan kuma kafafen sadarwa na zamani suna da rawar da zasu taka wajen zaburar da sauran yara da ba su sauka ba, domin ta hanyar nuna abin a gidajen yana sa yara su ji daɗi da kuma ƙara dagewa, haka kuma iyaye da Malamai ya kamata su kalli wasu abubuwa da ake aiwatarwa kamar abin da bai da kyau, to su yi ƙoƙarin hanawa domin kawo cigaba a cikin addini.

 

5.3 NAƊEWA

A wannan babi na biyar kuma babi na ƙarshe, ya fara da gabatarwa da shimfiɗa, bayan nan ya yi bayanin kundin gaba ɗaya, amma a taƙaice, sannan ya kawo shawarwari, daga ƙarshe naɗewa.

 

MANAZARTA

Al-Ƙur’ani Maigirma

Adamu, M.T (1998) “Aure da Biki a ƙasar Hausa” Kano: Ɗansarki Kura Publishers Nig. Ltd.

Abubakar, T.A (2015) “Ƙamusun Harshen Hausa” Zaria: Norther Nigeria Piblishing Company Limited.

Al-Hassan M. (1994) “Banbance-Banbance Al’adun Bikin Aure Tsakanin Al’ummar Hausawa da Yarbawa” Kundin Digiri na Farko Jami’ar Bayero, Kano, Sashen Harsunan Nijeriya.

Bunza A.M (2017) “Dabarun Bincike: A Nazarin Harshe da Adabi da Al’adun Hausawa” Zaria Ahmadu Bello Uniɓersity Press Limited

Bayero J. (2006) “Ƙamusun Hausa” Kano Cibiyar Nazarin Harsunan Najeriya, Jami’ar Bayero.

Ɗanfodiyo J. (2005) “Ɗunɗaye” Mujallar Nazarin Hausa juzu’i na Ɗaya Fitowa ta Biyu December, 2005. Department of Nigerian Langauge, Usman Ɗanfodiyo Uniɓersity, Sokoto.

Gusau, G.U (2012) “Bukukuwan Hausawa” Gusau Oral Faith Printis.

Gusau G.U (2010) Tasirin Al’adu cikin Makarantun Allo a Ƙasar Hausa Journal of Language Education Ɓol. 3, Katsina: Isa Kaita College of Education Katsina State.

Kabiru A.M (2019) “Zamfarci da Rabe-Rabensa”, kundin Digiri na Farko, Sashen Nazarin Harsuna da Al’ada Jami’ar Tarayya Gusau.

 

 


MUTANEN DA AKA YI FIRA DA SU

1.     Sheikh Abdullahi Abubakar Yabo, Zawiyyah, a Zawiyyar Sheikh Balarabe 20/1/2021 : 9:00am

2.     Sheikh Mal. Abubakar Abubakar Abi, a Gidansa Asibitin Shagari, Gusau  22/1/2021:10:00am                 

3.     Sheikh Mal. Muniru Muhammad Ɗaibah Asibitin Shagari, Gusau  24/1/2021 - 12:00am

4.     Mal. Mansur Ahmad Makaranta, a Gidan sa da ke Tudun Wada Gusau 24/1/2021 – 10:00am

5.     Sheikh Mal. Usman Tambuwal a Zawiyyar Sheikh Balarabe 27/1/2021 – 12:00am

6.     Sayyidi Malam Aliyu Uwaisu Rogo, a Zawiyyar Sheikh Balarabe 4/2/2021 9:00am

7.     Alh. Hafiz Alaramma Murtala Aliyu Dabbagi, a Sabon Gari, Gusau 10/3/2021 10:00am

8.     Mal. Aminu Aliyu Hizburrahim S/Gari 11/3/2021 – 12:00am

9.     Mal. Abdulrahman Ibrahim, Hizbirrahim Dandutse 20/4/2021 1:00


Post a Comment

0 Comments