Kundin bincike da aka gabatar a Sashen Koyar Da Harsuna Da Al’adu, Tsangayar Fasaha Da Al’adu, Jami’ar Tarayya Gusau, don samun shaidar kammala digiri na ɗaya (BA.HAUSA).
Laluɓen Al’adun Hausawa A Cikin Wasu
Waƙokin Musa Ɗanƙwairo
NA
Binta Gambo
GODIYA
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah
madaukakin sarki mai kowa mai komi da
yayi ni’ima a garemu tsira da amincin Allah su tabbata ga shugabanmu Annabi
Muhammad (S.A.W) da alayensa da sahabbansa da iyalansa da al’ummarsa baki ɗaya.
Bayan haka, wannan aiki na bincike
yana da wahala mutum ya aikatashi ba tare da ya samu mataimaka ba, dan haka ya
zama dole in mika godiya ta ga waɗanda suka bani gudunmuwa wajen ganin na
kammala wannan aikin mai matuƙar wahala.
Hausawa na cewa “Bin na gaba bin
Allah” don haka dole ne in miƙa godiya ta ga mahaifana bisa ɗaukar ɗawainiya ta
da suka yi tun daga haihuwa ta har zuwa ganin na samu ilimi tare da bani
gudunmuwar addu’oin su a kaina har zuwa wannan rana.
Har
ila yau Hausawa na cewa “Iyakar gudu ƙuryar ƙaki” ya zama dole in mika
godiya ta zuwa ga malammaina da jinjinar ban girma a gare su tun daga aji daya
har zuwa aji huɗu da kuma malama ta musamman wadda ke duba ni da aiki na na
bincike wato malama Halima Mansur Kurawa bisa ga juriyar duba wannan aiki tun
daga farkon sa har zuwa ƙarshe, da kuma gyara da shawarwari irin na ɗiya da uwa
domin ganin wannan bincike haƙarsa ta cinma ruwa.
Haka zalika ina miƙa godiya ta ga ɗaukacin
malammaina da hukumar wannan jami’a da fatar alkhairi a garesu baki ɗaya Allah
ya saka masu da alkhairi.
Har ila yau, ya zama dole inyi jinjina
ta musamman ga maigida na Ibrahim Shehu wanda ya bani damar yin wannan karatu
tare da bani ƙwarin guiwa da shawarwari da biya mani kuɗin makaranta da riƙa
mani iyalaina wajen ganin na samu abinda nike nema Ubangiji Allah ya saka mashi
da gidan Aljanna ya bashi abin da yake nema duniya da lahira kuma ya bashi abin
da zai ci gaba da ɗawainiya damu Amin.
Bugu da ƙari ya zama dole in mika
godiya ta ga mahaifana da ‘yan uwana da makota na da addu’oin da suke tayi min
ganin cewa na kamala karatuna da fatar alkhairi da suke man na gode Allah ya
saka masu da alkhairi baki ɗaya. Amin.
SADAUKARWA
Ni
Binta Gambo “Yarlele” wato Maman Amir. Na sadaukar da wannan kundin bincike,
mai taken “laluben Al’adu a cikin wasu waƙoƙin Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun”
ga mahaifana musamman Alhaji Dahiru Gambo Ahmad da mahaifiyata Hajiya Asiya
Dahiru da ƙannen mahaifiyata marigayi Bello Mainasara da malamina na islamiya marigayi
malam Dalhatu Ahmad bisa ɗawainiyar da suka yi dani tun ina ƙarama har kawo
yanzu.
Haka kuma na sadaukar da wannan
bincike zuwa ga kakata Hajiya Hassana da ƙanwata Jamila Dahiru da Zainab Aliyu
da ƙanena
TSAKURE
Kasancewar
waƙoƙin baka suna daga cikin muhimman ɓangarorin adabin da Hausawa ke ɗauka da
muhimmanci saboda kasancewar su tamkar wasu madubai daga cikin maduban da ake
dubawa domin gano irin hanyoyin rayuwar ita wanna al’umma.
Don haka ne
ma, ba kamar rubutattun waƙoƙi ba, su waƙoƙin baka sun fara ne lokaci mai tsawo
da ya gabata kuma hasashe na tarihi ya nuna sarakuna suna daga cikin waɗanda aka
fara yiwa kiɗa da waƙa.
Kiɗa da waƙa
a ƙasar Hausa wani ginshiƙin abu ne da aka aiwatarwa don ilmantarwa ko
sadaukarwa ko nishaɗantarwa ko ba da wata gudunmuwa ta musamman, kusan kiɗa
yayi ruwa da tsaki ya durmuya sosai a
cikin rayuwar Bahaushe , musamman rayuwar da ta ƙunshi zamantakewa da sana’oi
da bukukuwa da lokutan shakatawa.
Wannan aiki
ya ƙunshi laluben al’adu a cikin wasu waƙoƙin Alhaji Musa Ɗan ƙwairo Maradun.
Bugu da ƙari
shi wannan aiki an kasa shi gida biyar ya ƙunshi gabatarwa, dalilin bincike,
iyakancewar bincike da kuma tarihin mawaƙi haihuwa da mutuwarsa, da bayani kan
al’adun Hausawa da ma’anar al’ada da ire-iren al’ada da al’adu a cikin wasu
waƙoƙinsa har zuwa babi na biyar wanda ya kunshi kammalawa da sakamakon bincike
da shawarwari da manazarta.
BABI NA ƊAYA
1.0
SHIMFIƊA
Da sunan Allah mai rahama mai jinkai tsira da amincin Allah su ƙara
tabbata ga shugaban halitta Annabinmu, Annabi Muhammadu (S.A.W), tare da
alayensa da kuma sahabansa amin.
Waƙoƙin baka suna daga cikin muhimman ƃangarorin adabi da Hauwasawa ke ɗauka
da mahimmanci saboda kasancewar su tamkar wasu madubai daga cikin maduban da
ake dubawa domin gano irin hanyoyin rayuwar ita wannan alumma. Wato dai waƙoƙin
baka suna daga cikin manyan rukunan adabin baka na Hausa da suke taimakawa
wajen fahimtar shi kansa adabin wannan al’umma so sai da so sai.
Don haka ne ma,ba kamar rubutattun waƙoƙi ba, su waƙoƙin baka sun fara
ne lokaci mai tsawo da ya gabata kuma hasashe na tarihi ya nuna sarakuna suna
daga cikin waɗanda aka fara yiwa kiɗa da waƙa.
Kiɗa da waƙa a ƙasar Hausa wani ginshiƙin abu ne da aka aiwatarwa don
ilmantarwa ko sadarwa ko nishaɗantarwa ko bayar da wata gudunmuwa, ta musamman,
kusan kiɗa yayi ruwa da tsaki ya durmuya sosai a cikin rayuwar Bahaushe,
musamman rayuwar da ta danganci zamantakewa da sana’oi da bukukuwa da lokuntan
shaƙatawa.
Wannan aiki ya ƙunshi laluben Al’adu a cikin wasu waƙoƙin Alhaji Musa
Ɗanƙwairo Maradun. Kuma shi wannan aiki an kasa shi ne a manyan kaso har guda
biyar.
Babi
na ɗaya
: An yi Magana a kan manufar bincike, da hasashen bincike, da farfajiyar bincike, da matsalolin da ake
fuskanta yayin gudanar da wannan bincike da kuma hanyoyin da ake bi wajen
tattaro bayanai sai kuma jawabin naɗewa, wato takaita abin da babin ya ƙunsa.
Babi
na biyu
: Wannan babi ya ƙunshi ayukan da suka gabata, masu dagantaka da wannan aikin.
Misali littattafai da kundaye da kuma maƙalu.
Babi
na uku
: Ya na ƙunshe da tarihin makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun wanda ya haɗa da
haihuwarsa, rayuwarsa, iyalinsa, da fara kiɗa, da nau’oin waƙoƙinsa, waɗanda
suka haɗa da waƙoƙi a kan Al’adun Hausawa.
Babi
na huɗu:
Ya ƙunshi ma’anar Al’ada, da ire-iren Al’adun Hausawa da kuma nazarin wasu
waƙoƙin Alhaji Musa Ɗanƙwairo a kan Al’adun Hausawa da saƙon da suke ɗauke da
shi.
Babi na
Biyar:
Babi na ƙarshe kuwa, yana ɗauke ne da jawabin kammalawa da sakamakon bincike
wato abinda bincike ya gano, da kuma shawarwari don inganta ayukan masu zuwa a
ƙarshe wannan aiki anzo da manazarta, inda aka kawo littattafai da kundaye da
maƙalu waɗanda ake dubawa yayin aiwatar da wannan bincike, an kuma kawo ratayen
waƙoƙi da aka samo misalan daga cikinsu.
1.1 MANUFAR
BINCIKE
Akwai
mahimman hujjoji ko dalilai waɗanda suka sanya a gudanar da wannan bincike kamar haka:
Dalili
na farko, shi ne ina da matuƙar sha’awar sauraron waƙoƙin makaɗa da
mawaƙan Hausa, musamman Waƙoƙin Alhaji
Musa Ɗanƙwairo.
Wani
dalilin kuma, domin a ƙara fito da baiwar wannan makaɗi a fili, a fahimci
hikima da fasarar da Allah Ubangiji maɗaukaki ya yi masa ta waƙa in da har ya
fito da Al’adun Hausawa masu kyau da nufin faɗakarwa wajen kiyaye su, dalili na
uku shi ne taskace wasu waƙoƙinsa da ya yi a kan Al’adun Hausawa don ‘yan baya
masu nazari ko neman wasu bayanai su amfana. Haka kuma wannan binciken an yi
shi domin cike wani gurbi na samun shaidar kammala digiri na farko a fannin
Hausa wato (B.A Hausa).
1.2 HASASHEN BINCIKE
Babbar manufar wannan bincike ita ce
labubo wasu Al’adun Hausawa daga cikin waƙoƙin Alhaji Musa Ɗankwairo. Sannan a
yi hasashen ko Hausawa suna riƙe da wannan Al’adu? Da kuma alfanun riko da su,
idan kuma sun watsar da al’adun to wannan jan kunne makaɗin ya yi kuma a wane
hali a ke ciki yanzu.
1.3 FARFAJIYAR BINCIKE
Wannan
bincike zai ta kaikawo a wasu daga cikin waƙoƙin Alhaji Musa Ɗanwairo Maradun,
kuma binciken zai kalli wasu Al’adun Hausawa da mawaƙin ya yi amfani da su a
cikin wasu waƙoƙin na sa.
Don
haka duk abin da bai shafi Al’ada ba a cikin wasu waƙoƙin ba za’ayi maganar su ba.
1.4 MATSALOLIN BINCIKE
1.
Rashin wani wanda ya gaba ce ni wajen
aikin lalubo wasu Al’adun Hausawa.
2.
Matsalar mutane sun watsar da Al’adun su
wajen lullubi da sa kaya irin na Al’adun gargajiya.
3.
Matsalar wajen tattaro waƙoƙin mawaƙin
4.
Mutane sun watsar da al’adun su na
sauraren waƙoƙin makaɗan gargajiya.
1.5 MAHIMMANCIN BINCIKE
Bincike
wata hanya ce da ake ƙudurta ta ta
hanyar yin nazari akan wani abu da ake ganin ya cancanta domin a gano wani
sabon al’amari don cigaban al’umma. To in ko haka ne a yayin gudanar da bincike
yana buƙatar tunani shin ko binciken nan zai yi amfani ga al’umma?
Don
haka akwai waɗansu mahimman abubuwa da suke iya zama ko kuma suke da inganci
abincika kamar haka: Domin a fito da hanyoyi masu sauki na gudummuwar da
mawaƙan Hausa na baka suke bayarwa zuwa ga al’umma haka kuma wani mahimmancin
wannan binciken shi ne Habaka ko bunƙasa adabin Hausa. Wannan binciken yana da
mahimmanci domin a ƙarawa malammai da ɗalibai ƙwarin gwuiwa wajen farfado da
kuma raya Al’adun Hausawa. Daga ƙarshe wannan bincike ya na da mahimmanci wajen
nuna bunƙasar ko cigaban da harshen Hausa ya samu a yau ta bangeren adabi.
1.6
HANYOYIN GUDANAR DA BINCIKE
Hanyoyin
da ake bi wajen gudanar da bincike sun haɗa da :
1.Duba
kundayen bincike da aka gabatar don samun digiri na ɗaya zuwa na uku masu
dangantaka da wannan aiki.
2.Amfani
da littattafai da maƙalu da aka gabatar a tarukka daban-daban.
3.Sauraron
kaset- kaset masu ɗauke da waƙoƙin Musa Ɗanƙwairo waɗanda suka shafi Al’adun
Hausawa.
4.Hira
da masana da masu sauraron waƙoƙin Musa Ɗankwairo.
1.7 NAƊEWA
A
wannan babi an yi bayani ne akan shimfiɗa,manufar binkice,hasashen
bincike,farfajiyar bincike,matsalolin bincike da ya samu wajen gudanar da shi
da kuma hanyoyin gudanar da bincike da naɗewa duk acikin babi na ɗaya.
BABI NA BIYU
2.0 SHIMFIƊA
A
wannan babi na biyu za’a yi bayani akan bitar ayyukan da suka gabata makamantan
wannan aikin bincike.
Inda
za’a yi bayani dangane da littattafai da muƙalu da kundaye, haɗi da bayanin
hujjar ci gaba da bincike da kuma naɗewa duk a cikin wannan babi na biyu.
2.1 BITAR AYYUKAN DA SUKA GABATA
Babu ko
shakka ko wata tantama akwai wasu ayyuka da aka gudanar game da waƙoƙin wannan
shahararren makaɗi wato, Makaɗi Alhaji Musa Ɗanƙwairo. Domin zai zama abin
mamaki a ce mashahurin mawaƙi na ƙasar Hausa kamar makaɗi Alhaji musa Ɗanƙwairo
ba a yi wani nazari a kan waƙoƙinsa ba sam-sam.
Hausawa
suna cewa ‘Daga na gaba ake gane zurfin ruwa’.ko da na gaban wada ne haka kuma
sun ce “inda Akuyar gaba ta sha ruwa haka nan
ta baya ke sha” wannan kuwa haka yake babu shakka ansha gudanar da
bincike da kuma rubuce rubuce a ciki da wajen sassan adabin Hausa na waƙoƙin
baka da rubutattun waƙoƙin Hausa daga malamai da manazarta daban-daban domin
dada zurfafa aiki don cigaba da gudun maimaici.
Haka
kuma akwai littattafai da muƙalu da kundayen Digiri na ɗaya har zuwa na uku da
aka yi a jami’oi daban-daban don haka zan diba wasu ayukan da suka gabata domin
su zama jagora wajen wannan nazari da kuma taimakon mai duba aikin.
2.1.1 BUGAGGUN LITTAFAI
Masana
da manazarta da dama sun rubuta littattafai da yawa da suka shafi adabin Hausa
musamman na baka.
Ɗangambo
(2007) A cikin littafinsa daya wallafa
mai suna “Ɗaurayar Gadon feɗe waƙa” ya bayyana yadda a ke nazarin rubutattun
waƙoƙi a ciki ya yi bayanin salo da sarrafa Harshe da abinda ya kunsa da kuma
bayanin Awon Baka (zubi da tsari) da sauransu.
Wannan
aiki ya yi kama da wannan saboda duk suna Magana ne a kan adabi, kuma wanda ya
ƙunshi waƙa.
Sai dai
kuma inda suka bambanta shi ne aikin yana magana ne a kan yadda mawaƙi ke waƙa
Al’adun Hausawa a ciki waƙoƙin baka musamman na Hausa.
Gusau(2005)
a cikin littafinsa mai suna makaɗa da mawaƙan Hausa ya yi bayanin yadda mawaƙan
Hausa suka rabu ya kasa littafai har kashi biyar.
1. Kashi
na ɗaya makaɗan yaƙi
2. Kashi
na biyu makaɗan sarakuna na I
3. Kashi
na uku makaɗan sarakuna na II
4. Kashi
na huɗu makaɗan jama’a sai
5. Kashi
na biyar makaɗan sana’a.
Wannan
aiki ya yi kama da wannan da yawa saboda duk suna magana ne akan mawaƙan baka
na Hausa. Sai dai bambancin su shi ne mun ɗauki mawaƙi ɗaya ne mu yi nazarin
laluben al’adun Hausawa a cikin wasu waƙoƙinsa.
Bunza
A,(2009) ya wallafa littafi mai suna Narambaɗa. Wannan littafi, Bunza ya fito
da muhimman bayanai da suka shafi tarihin rayuwa da ayyukan Ibrahim Narambaɗa
Isa, tare da yin sharhi mai gamsarwa na ilimi da kuma rarrabe wasu waƙoƙin nasa
a mahangar al’ada da tarihi. Haka kuma ya yi ƙoƙarin fito da wasu hikimomi a
cikin Littafin.
Wannan
aiki ya yi kama da wannan saboda duk muna magana a kan mawaƙan baka na Hausa.
Sai dai inda suka bambanta shi ne shi yana magana ne akan Ibrahim Narambaɗa,
shi kuma wannan aikin yana magana ne akan Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun.
2.1.2 KUNDAYEN BINCIKE
Masana
da manazarta da dama sun rubuta kundayen bincike masu alaƙa da wannan bincike.
Kurawa,(2004)
ta gudanar da binciken ta, a cikin kundin Digirinta na farko a kan “Adon Harshe
cikin waƙoƙin sardauna” na makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo a wannan bincike ta
kawo ma’anar Adon Harshe daga masana daban-daban sannan kuma ta yi nazarin wasu
tubalan Adon Harshe.
Wannan
aiki yana da alaƙa da wannan aikin, domin duk ana magana ne akan mawaƙi ɗaya
wato, Musa Ɗanƙwairo. Sai dai inda aikin namu ya bambanta shi ne namu aikin
yana Magana ne a kan laluben al’ada acikin wasu waƙoƙin Musa Ɗanƙwairo.
Sankalawa
(1994) ya gudanar da bincikensa a cikin kundin Digiri na farko akan “Nazarin
rayuwar makaɗa sani sabulu” da falsafar waƙoƙinsa marubucin ya yi bayani a kan
rayuwar makaɗa Sani Sabulu a matsayinsa na makaɗi da yanaye-yanayen waƙoƙinsa
ta fuskar turke da awon baka da salo da sarrafa Harshe.
Wannan
aiki yana kama da wannan domin duk aikin ya na magana ne a kan makaɗan Baka na Hausa. Don
haka wannan aikin ya na da alaƙa da wannan sai dai kuma inda suka bambanta shi
ne wannan aikin yana bayani ne akan laluben Al’ada a cikin wasu waƙoƙin Alhaji
Musa Ɗanƙwairo Maradun.
Adama
(2012) a cikin aikinta na kundin Digiri na biyu mai taken “Salo da sarrafa
Harshe a cikin wasu waƙoƙin Jam’iyyun A.N.P.P da P.D.P a jihohin kano da
jigawa” ta yi tsokaci akan a salin rubutattun waƙoƙin siyasa da samuwarsu da
kuma bunƙasarsu. Daga nan sai mai nazarin ta duba ma’anar salo da sarrafa
harshe da ire-irensa bisa ra’ayoyin masana daban-daban.
Haka
kuma ta kawo misalan yadda wasu mawaƙan siyasa musamman a jihar Kano da jigawa
suke sarrafa hikimominsu ta hanyar Salo da sarrafa harshe.
Wannan
aiki yana da alaƙa da wannan. Sai dai yana bayanin laluben al’ada a wasu daga
cikin waƙoƙin Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun.
Yakubu,(2012)
ya gabatar da aikin bincike don neman digiri na biyu mai suna “Adon Harshe a
waƙoƙin Mamman Shata na masu sarauta.” A cikin wannan aiki an fara gabatar da
asali da wanzuwar waƙar baka a ƙasar Hausa. Sannan ya yi bayanin wasu daga
cikin ra’ayoyin masana dangane da haka. Daga nan sai ya duba tarihin makaɗa
mamman Shata, tare da bayani a kan wasu daga cikin nau’oin adon harshe da
Mamman Shata ya yi amfani da su a cikin waƙoƙinsa na masu sarauta.
Wannan
aiki yana da alaƙa da wannan aikin sai dai inda suka bambanta shi ne,
wannan aikin yana magana ne akan laluben
al’ada a cikin wasu waƙoƙin Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun.
A
dunƙule, dukkan waɗannan kundayen bincike da bugaggun littattafai da muƙalu na
ilimi da aka ambata a sama suna da dangantaka ta kusa da wannan aikin da aka
gabatar. Domin kuwa mafi yawansu sun yi bayani ne a kan makaɗa da mawaƙan baka
na Hausa. Haka kuma za su taimaka ƙwarai da gaske wajen fito da martabar wannan
aiki , wanda ya kunshi laluben Al’ada a cikin wasu waƙoƙin Alhaji Musa
Ɗanƙwairo Maradun.
Dumfawa
A.A. (2003) ya gabatar da aikin bincike don neman digiri na uku mai suna “Waƙa
a tunanin Yara” a jami’ar Usmanu Danfodiyo Sakkwato. A cikin wannan aiki
malamin ya yi gabatarwa inda kuma ya kawo ma’anar waƙa tare kuma da yin bayanin
tunanin Yara a game da waƙa.
Wannan
aiki yana da alaƙa da wannan aiki, domin duk suna magana ne akan adabin Hausa,
wanda ya shafi waƙa. In da kuma aikin ya bambanta da nashi shi ne wannan aiki
yana magana ne akan wasu al’adun Hausawa a cikin waƙoƙin Alhaji Musa Ɗanƙwairo
Maradun.
Garba,
S.(2001) ya gabatar da aikin bincikensa don neman digiri na uku. Mai taken
“Salon sarrafa harshe a waƙoƙin Aƙilu Aliyu. Sashen Harsuna da al’adun Afrika,
Jami’ar Ahmadu Bello Jihar Kaduna, Nijeriya. A cikin aikin nasa ya kawo ma’anar
salo da nau’o’insa ya kuma kawo bayanin hikima da sarrafa harshen da shi
mawaƙin ya yi a cikin wasu waƙoƙinsa.
Wannan
aiki ya yi kama da wannan aiki, saboda duk suna magana ne akan adabi a cikin
waƙoƙi. Sai dai inda wannan aikin ya bambanta da nashi shi ne, wannan aikin ya
na magana ne akan wasu al’adu a cikin waƙoƙin Musa Ɗanƙwairo shi kuma nashi
aikin yana magana a kan Salon sarrafa harshe a waƙoƙin Akilu Aliyu.
2.1.3 MUƘALU
Malamai
da masana da dama sun gabatar da muƙalu a kan adabin baka wanda ya shafi waƙar
baka.
Gusau(2013)
ya gabatar da muƙala mai suna “ Dangantakar waƙoƙin Baka da Al’adun Hausawa
Bunƙasa ko koma baya” Wannan takarda cike
take da ɗimbin bayani akan Al’adun Hausawa da matsayin waƙoƙin baka a
wajensu, tare da misalan kaɗe-kaɗen Hausawa. Haka kuma ya nuna irin bunƙasar da
wannan waƙoƙin suka samu tun daga wancan lokaci har komo wa yanzu, sannan kuma
ya rufe takeda da kowa halaye da dabi’u waƙoƙin masu hikima da armashi waɗanda
al’ummar Hausawa za su amince da su.
Aikin
nasa ya yi kama da wannan aiki sai inda suka bambanta shi ne wannan aiki yana
bayani ne akan laluben al’adun a wasu waƙoƙin Musa Ɗankwairo.
Gusau
(2011) ya gabatar da muƙalarsa mai suna tasirin Al’ada da adabin Hausa a kan
tufafin Hausa. Maƙalar ɗauke take da dinbim bayanai akan ma’anar Al’ada da kuma
ire-iren tufafin Hausawa na gargajiya ya rufe takardar da kawo mahimmancin
tufafi ga rayuwar al’umma.
Aikin
nasa yayi kama da wannan domin duk suna magana ne akan Al’ada a adabin Hausa.
Sai dai inda aikin ya banbanta da wannan aikin shi ne aikin yana magana ne akan
laluben al’ada a wasu daga cikin waƙoƙin Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun.
2.2 HUJAR CIGABA DA BINCIKE
Akwai
muhimman hujjoji ko dalilai waɗanda suka sanya a gudanar da wannan aikin na
bincike gasu kamar haka:
Dalili
na farko shi ne akwai matuƙar sha’awar sauraron makaɗa da mawaƙan Hausa,
musamman waƙoƙin Alhaji Musa Ɗanƙwairo. Saboda haka akwai sha’awar gabatar da
bincike a wasu daga cikin waƙoƙin wannan mawaƙi wanda ana iya cewa sananne ne a
waƙoƙin fada.
Wani
dalili kuwa da yasa aka gudanar da wannan bincike akan wannan makaɗi shi ne
domin a ƙara fito da wannan makaɗi a fili duniya ta ƙara saninsa ta kuma ji
irin fasaha da hikimar da Allah (S.W.T) ya ba shi.
Dalili
na gaba shi ne ƙara bada ƙwarin guiwa wajen gudanar da bincike akan wannnan
makaɗi shi ne duk da cewa ya rasu, to don kada a manta da shi da kuma irin
fasahar da Allah ya ba shi saboda a tuna dashi, haka ya dace a ɗauki wasu daga
cikin waƙoƙin da ya yi domin tunawa da shi da kuma nuna ma al’umma irin fasahar
da yake da ita a fagen kiɗa da waƙa.
2.3 NAƊEWA
A
ƙarshe wannan babi na biyu an kawo bayanai da suka shafi bitar wasu ayyuka da
suka yi kama da wannan aikin bincike Inda bayanin ya ƙunshi waiwaye ga wasu
ayyukan makamantan wannan aiki inda suka haɗa da kawo littattafai da kundaye da
kuma muƙalu.
BABI NA UKU
RAYUWAR MAKAƊA
MUSA ƊANƘWAIRO DA MATASHIYA A KAN MA’ANAR AL’ADA.
3.0 SHIMFIƊA
Al’ada wata sabbabiyar hanya ce ta
gudanar da rayuwar kowace al’umma ta duniya. Sai dai kowace al’umma da irin
tata Al’ada, amma kusan akwai dangantaka ta kusanci tsakanin al’adun al’umma. Hausawa mutane ne masu alfahari da tasu al’ada kamar sauran al’umummomi.
3.1 MA’ANAR AL’ADA
Yana da mahimmanci a fahimci
mece ce Al’ada. Ma’ana shi ne madubi da zai haskaka a samu damar ƙyallaro wasu
al’umma da hakan zai yi tasiri a gare su.
Muhammad da Bashar, (2004:21)) suka ce
‘Al’ada ita ce hanyar da mutane suke bi domin tafiyar da rayuwa’.
Umar, (1987). Cewa ya yi “dukkan
abubuwan da akasarin jama’a na kowace al’umma suka amince da yin su, ko yin
amfani da su su ne Al’adunsu’
Bunza, (2006)
shi ko yace “ Al’ada tana nufin dukkan rayuwar ɗan adam tun daga
haihuwarsa har zuwa ƙabarinsa” Sai ya ƙara da cewa ko ina mutun ya samu kansa duk wata dabi’a da
ya tashi da ita tun farkon rayuwa ya tarar a wurin da ya rayu ko yake rayuwa
ita ce al’adarsa da za a yi masa hukunci a kai.
Kuma babu wata al’umma da za
ta rayu a doron ƙasa face tana da Al’adar da take bi, kuma da ita ake iya
rarrabe ta da wata da ba ita ba.
Masana daban-daban
sun yi bayanin abin da suka fahimta ga Al’ada. Alal misali Muhammad Sani
Ibrahim ya bayyana al’ada da cewa:
“Ita kalmar al’ada asalinta larabci ce
amma da Hausa tana nufin hanyar rayuwar al’umma, musamman hanyoyin rayuwa ta
yau da kullum wanda al’umma ta saba da yi” (Ibrahim, 1985:1).
Ya ƙara da cewa al’ada ta kasu kashi
biyu a wurin Hausawa. Akwai Al’adun gargajiya waɗanda Hausawa suka gada tun
iyaye da kakanni, irin waɗannan al’adu yawanci kowace al,umma tana wulaƙanta
wanda ya wulaƙanta su.
Kashi na biyu kuma su ne baƙin Al’adu
irin waɗanda Hausawa suka koya bayan cuɗanyarsu da wasu baƙin ƙabilu musamman
turawa. Irin waɗannan al’adun daga cikinsu akwai masu kyau, akwai kuma munana.
To amma saboda bambancin addini da wayewar kai da ke tsakanin Hausawa da
Turawa, munana da suka koya daga wurin turawa sun fi kyawawan yawa.
Don haka ne a kullum suke ƙoƙarin
kautar da ‘ya ‘yansu daga bin irin waɗannan al’adu.
Shi kuwa Abdulƙadir Ɗangambo ga yadda
ya bada ma’anar al’ada.
“Al’ada ita ce
abar da aka saba yi yau da gobe”
(Ɗangambo, 1980:38)
Ya daɗa faɗaɗa tunaninsa in
da ya ce akwai al’adu da ɗabi’u da yawa da Hausawa suke yi. Misali al’adu da
suka shafi aure ko haihuwa da zumunci da sauransu. Ya kuma ƙara da cewa al’ada
wani yanki ne na rayuwa. Ta ƙunshi wasu halaye da ɗabi’u da aka saba yi yau da
kullum don rayuwa. Akwai masu kyau da marasa kyau.
Shi kuwa Nasiru Ibrahim cewa
ya yi Al’ada ita ce baki ɗayan hanyoyin rayuwar al’umma” (Yaro, 1997:3)
Dangane da wannan bayani za
a fahimci Al’ada ta haɗa baki ɗayan rayuwa tun daga haihuwa zuwa mutuwa. Don
haka ma’ana babu girma babu ƙanƙanta har wayau babu Al’ada guda ɗaya ta dukkan
al’ummomin duniya da ta yi kama da wata wannan shi ya haifar da
bambance-bambance al’ada ta fara da alama tun ran gini tun ran zane, al’ada abu
ne mai yaɗo, Kuma wanda yake tafiya da yanayin rayuwa. Al’ada ta danganci wasu
abubuwa wanda ba za a iya gani ba, ballanta ma a taɓa don haka ta haɗa da
abubuwa irin su matakan rayuwa da haihuwa da aure da mutuwa da hanyoyin gudanar
da shugabanci. Hanyoyin tattalin arziki da zamantakewar al’umma. Haka kuma
al’ada ta tarar ta kuma daddasa duk ra’ayoyinta da halayyarta da sauran
abubuwan da ta ƙunsa. Wannan zai haifar da canje-canje cikin al’adar da aka
tarar, wato ta zama ta sake siffa, ko kuma mu ce ta sami gauraye. Irin
wannan sauyi ya sami Hausawa da Hausa har sau biyu. Kashi na farko, Shi ne
lokacin da musulunci da halayyar Larabawa suka shigo ƙasar Hausa, daga wajen
ƙarni na 12/13 zuwa karni na 19 muka ga yadda suka shafi al’adun gargajiya na
Hausa da rayuwar Bahaushe. Kashi na biyu kuwa shi ne mun ga yadda Turawa da
wasu Al’adu nasu suka shigo ƙasar Hausa da kuma yadda suka shafi Hausawa a
wannan karni na 20 (Ɗangambo,1984:1)
3.3.1 IRE-IREN AL’ADA
Akwai rassan Al’ada guda bakwai.
1. Addini : Abin bauta irin na gargajiya misali, kan gida ko tsafi da bori.
2. Rayuwar Hausawa: Ta fannin sana’oin gargajiya misali farauta, noma kiwo.
3. Tsarin zaman jam’a :
Zamantakewa iyali na gidan yawa, tun daga kakanni da iyaye da tattaɓa kunne.
4. Shugabanci: Tun daga gida,
Maigida, shi ne shugaba mai tsawatarwa har zuwa uwargida, sai a unguwa akwai
mai unguwa da sauransu.
5. Tattalin Arziki : Inda
ake tanadi da adana hatsi (abinci) a rumbu don gaba da kuma asusu a ɗaki domin
ajiye kuɗi.
6. Bukukuwa da wasanni: Wanda
ya shafi tun daga suna na haihuwa da aure, da mutuwa da sarauta da wasanni da
ake yi a wannan lokaci.
7. Magungunna: Na gargaji na
magori na cututtuka iri-iri da na yan bori.
3.2
TARIHIN RAYUWAR ALHAJI MUSA ƊANƘWAIRO
A wannan babi za a yi magana game da wasu
muhimman rukunai na tarihin rayuwar Alhaji Musa Ɗanƙwairo tun daga bayanin
haihuwarsa da ƙurciyarsa da yanayin kiɗansa da sauransu.
Alh Musa Ɗanƙwairo Maradun (1909-1991)
3.2.1
SUNAN MAKAƊI DA LAƘABINSA
Sunan wannan makaɗi
na yanka shi ne Musa wanda mahaifinsa ya zana masa lokacin da sati ya zagayo da
haihuwarsa a ka yanka bisar suna aka raɗa masa suna da “Musa”.
Makaɗa
Musa ya sami laƙabin “Danƙwairo” a sanadiyar sunan wani ƙanen mahaifinsa wanda
ya yi tafiyarsa yawon duniya da ake kira “ƙwairo” shi ne dai ƙwairo yaron usman
ne, kuma yana da zaƙin murya,amma daga baya sai ya bar kiɗa. To bayan da Musa
ya kai kimanin shekara bakwai, sai ya soma karƃi tare da mahaifin nasa, saboda yana da zaƙin
murya kamar ƙwairo, sai makaɗa usman ya ce “ Ga Ɗanƙwairo kuma an mayas. Shi
ken an sai sunan Ɗanƙwairo ya bi makaɗa
Musa ( Gusau,2005:104)
3.2.2 ASALIN IYAYE
DA MAHAIFAN MUSA ƊANƘWAIRO
Sunan mahaifin musa Ɗanƙwairo
shi ne Usman Dan kwanda, mahaifiyarsa kuma ana kiranta ‘yarnunu wadda ta fito
daga ƙauyen goran namaye a cikin karamar hukumar mulki ta maradun a cikin jahar
Zamfara.
Mahaifinsa kuma, wato usman
dan kwanda mutumin dankado ne a cikin yankin karamar hukumar mulki ta Bakura, a
jihar Zamfara.makaɗi Usman Dan kwanda yana kiɗan noma da na Saraki, sai sarkin
ƙayan Maradun Ibrahim I (1903-1923) ya taso ya koma ƙasar Maradun ya zama makaɗin
sa. Anyi wannan hijira ne lokacin da Ɗanƙwairo yake da shekara biyar da haihuwa
watau shekarar 1914. (Gusau, 2015).
3..2.3 SHEKARUN
HAIHUWARSA
Makaɗi Musa Ɗanƙwairo a bisa
zance mafi rinjaye sahihin bincike dangane da inda aka hai fe shi da kuma shekarar da aka haife shi ya nuna
cewa shi makadi Musa Danƙwairo an haife shi ne a shekarar 1909 a ƙauyen ɗan
kado cikin ƙasar Bakura ƙaramar hukumar mulki ta Bakura a cikin jihar Zamfara a
halin yanzu.(Gusau, 2005).
3.2.4 ILIMINSA
Dangane da iliminsa makaɗi
Alhaji Musa Ɗanƙwairo a iya cewa Allah ne ya yi wa Danƙwairo gamon katar da
fahimtar hanyoyin fasaha da hikima , amma bai sami damar shiga makarantar allo
ba , haka ma kuma bai yi boko ba. Allah yakan ba mutun baiwar wani
abu ba sai an koya masa ba. Sannan kuma yana da saurin fahimta da kuma ɗauke
duk wani tarihin abubuwan da yake ji ga manya.
Wata
ƙila wannan shi ne yake ba shi haske ga fahimtar madafar al,amuran da ke afkuwa
yau da kullun.
Ɗanƙwairo dai a taƙaice bai sami
karatun allo ba balantana na zamani sai dai makarantar kiɗa
kawai.(Gusau,2005:105).
3.3.5 RAYUWAR AURE DA IYALIN MUSA ƊANKWAIRO
(Gusau,2005:115)
yace Alhaji Musa Ɗankwairo Allah ya albarkace shi da yin aure. yana da matar
aure guda uku da ‘ya’ya goma sha bakwai (17), goma maza, bakwai mata. ‘ya’yansa
maza su ne:
Alhaji
Muhammadu (daudun kiɗa) – ya rasu
Alhaji
Abubakar (daudun kiƙa -yanzu sarkin kiɗa)
Alhaji
Abdu wakilin kida
Alhaji
Sani marafan kida – ya rasu
Garba
Ciroman kida
Umaru
Muhammad
balarabe
Musa
Ibrahim
Umaru –
ya rasu
Huɗu daga cikin su watau, Umaru
Muhammad Balarabe ,Musa Ibrahim kidan
noma suka yi:
‘Ya ‘yan mata kuwa sune:
Hauwa
Zalihatu
Habiba
Amina
Aishayu
Sa’adatu da
Aminatu
Bayan haka da jikoki maza da mata dari da hudu (104).
3.2.6 FARA KIƊA DA WAƘA
Musa Ɗanƙwairo ya gaji kiɗa gaba da baya kuma ya buɗa ido a cikin sa. Ya
fara koyon kiɗa a gurin ,mahaifinsa Usman tun yana ɗan shekara bakwai wato
wajejen 1916. A lokacin ya soma
da kiɗan kanzagi har ya zo ya karbu kamar dai yadda ake koyon kiɗa.
Bayan mahaifinsa
ya bar kiɗa sai ya hannuntashi ga wansa makaɗa kurna. Awurin Abdu Kurna ya
naƙanci kiɗa sosai ya dinga binsa zuwa wajajen kiɗa daban-daban. Saboda hazaƙar
Ɗanƙwairo sai Abdu Kurna ya bashi muƙamin Daudun kiɗa watau Ɗangaladimansa. Tun
yana Dangaladiman kiɗa aka ga alamar taimaka wa Kurna bayar da waƙa da kuma
ƙari gareta. (Gusau,2005:107)
Mawaƙin ya yi wata waƙa ta sarkin Maradun, “
Gindin
waƙa: Bubakar baban Baraya
Ya riƙa bai san sake
ba
Jagora : Hawanai lafiya
Y/Amshi
:Dattijo hawa nai lafiya sauka da
girma.
A nan
mawaƙin ya nuna mana cewa shi yana ƙari kuma yana yin amshi ga ɗiyan waƙa.
Musa
Ɗanƙwairo duk lokacin da ya sami sauli ba a zuwa wani rangadin kiɗa ko zuwa
yammaci, sai ya dinga waƙoƙin noma tare da yara yan’uwansa.Amma duk lokacin
daya dawo yawon gayauna yana nuna duk abun da ya samo.
Yana
cikin wannan hali, sai makaɗa Kurna ya ba shi izini ya fara yi wa ya’yan sarakuna
waƙa don ya saba da kiɗan sarakuna. Waƙar da ya fara yi ta ya’yan sarakuna ita
ce wadda ya tafi tare da uwargidansa Zemo tana yi masa amshi. Ga waƙar:
Gindin
Waƙa: Dan sarki a gode maka
Jikan dodo ɗan gwamma
Jagora: Ya tafi daji ba shi komawa
Y/Amshi: Kullum
daga duƙe sai duƙe
Gyado mai ƙoƙarin gaske
Jagora: Mijin
diya jikan Nomau
Gwarzon Ango karsanin
Ali
Gungaman Iro ɗan jatau
Y/Amshi: Kullum daga duƙe sai duƙe
cayaɗo mai ƙoƙarin gabce
(Gusau,2005:107-108)
3.2.7 KAYAN KIƊANSA
Makaɗa musa Ɗanƙwairo tun lokacin da ya fara koyon kiɗa yana amfani da
Kotso ne a matsayin abin kiɗansa. Ɗanƙwairo mahaifinsa makaɗin fada ne tun
asali kuma kayan kiɗansa shi ne kotso. Hakama wansa watau Abdu kurna da
mahaifinsu ya ba izinin yin kiɗa shi ma da kotso yake yin kiɗansa.
Haka kuma lokacin da Ɗanƙwairo ya yi kiɗan noma ya yi
amfani kayan kidan da ake kira farar “ganga” da ita ce ya yi amfani a wajen kiɗan
noma.
Makaɗa Usman
mahaifin Ɗanƙwairo shahararren makaɗi ne na noma a Bakura tun kafin ya koma
ƙayan Maradun.
Kuma
yana haɗawa da kiɗan saraki. Sannan yana amfani ne da kayan kiɗan da ake kira farar
“ganga” da “kotso” shi ma waɗannan ya gaje su ne tun daga nasa mahaifin watau
Makaɗa kaka wanda ya yi kiɗan yaƙi da na noma. Saboda haka kayan kiɗan da
Ɗanƙwairo ya yi amfani da su a wajen sana’arsa ta kiɗa da waƙa su ne farar
ganga a wajen kiɗan noma, sai kuma kotso a wajen kiɗan saraki wanda da
shi
aka san shi har ya barkiɗa ya koma ga Allah mahaliccinsa.
(Gusau,2005)
3.2.8 IRE-IREN WAƘOƘINSA
Makaɗa
Musa Ɗanƙwairo yayi waƙoƙi da dama ta fanni iri-iri, ya kuma yi waƙoƙi masu ɗinbin
yawa waɗanda shi kansa ya tabbata bai iya ƙiyasta adadin yawansu. Amma a dunƙule dai ire-iren waƙoƙin daya yi su ne.
:Waƙoƙin noma
:Waƙoƙin ta’aziyya
:Waƙoƙin siyasa
:Waƙoƙin gargaɗi da
faɗakarwa
:Waƙoƙin jama’a
:Waƙoƙin fada na
sarakuna.
Makaɗa Musa Ɗanƙwairo ya yi waƙoƙin noma wanda muna iya cewa su ne ya fara
yi tun lokacin wata waƙa da ya yi ta noma mai Gindin waƙar.
Gindi: :Dan
sarki a gode maka
:Jikan dodo ɗan gwamma
Y/Amshi: :Ya tafi daji bashi komawa
:Kullun daga duƙe sai duƙe
:Mijin diya jikan nomau
:Gwarzon
ango karsanin Ali
Ga kuma misali
wata waƙa mai suna waƙar noma.
Jagora: Noma
babba sana’a
Y/Amshi:
Koway yi ta ya bar rasawa
Jagora
: Ku zan aje noma daidai ne
Kowa aje gero da dawa
Kuzan tsare noma daidai ne
Y/Amshi : Kowa
aje gero da dawa
Wannan ya debe takaici
Waƙar
ta’aziyya: makaɗa Musa Ɗanƙwairo ya yi waƙar ta’aziyya inda ya yi wa Sir Ahmadu
Sardaunan Sakkwato waƙa, yana cewa:
Jagora:Ya wuce reni ba a yi mai shi
Amadu jikan Garba Sadauki
Daudu:Farimiyan jihar Arewa Ahmadu
Abin da kai ma Nijeriya
Har ƙasa ta naɗe, ana tuna ka
Ahmadu jikan
Y/Amshi: Bawan Allah Gamji ɗan ƙwarai
Gohe Allah
Malam Gohe, Allah
gafarta ma.
Waƙoƙin
siyasa: Ɗanƙwairo ya yi waƙoƙin siyasa. Ga misali wata waƙa da ya yi ta siyasar
N.P.N sunan waƙar jam’iyar siyarsa N.P.N mawaƙin na cewa:
Gindin
waƙa: Jamiyar N.P.N
Aminci dai N.P.N
Y/Amshi: Ku ya da karya
Jagora : Ku kamma gaskiya X2
Y/Amshi: ku ya da karya,
Ku
kamma gaskiya X2
Karku
sake don Allah
Mutane
kar ku sake don Allah.
Waƙoƙin Gargaɗi da faɗakarwa:
Mawaƙin
ya yi waƙoƙi da damna gargaɗi da faɗakarwa zuwa ga jama’a ga misalin wata waƙa
da ya yi inda yake cewa:
Gindin
waƙa: Mu bi al’adunmu na gargajiya
Kar mu sake mu mance
Mu bi
al’adunmu na gargajiya
Kasan
arewa Babbar riga
Ga
rawani da taggo
Mu bi
al’adunmu na gargajiya
Waƙoƙin
jama’a: makaɗa Ɗanƙwairo ya yi wa jama’a da yawa waƙoƙi. Ga misalin ɗaya daga
ciki. Waƙar Alhaji Bello maitama Yusufu.
Gindin
Waƙa: Minista na ciniki
:Allah
ya isam ma Bello Maitama Yusuf
Jagora : :Kai minista na ciniki
Y/Amshi : :Allah ya isam ma Bello maitama yusuf
Jagora :
:Taho ga ka ga maza
Y/Amshi: :
Wandara uban Akke Ado sarkin fada
:Minista na ciniki
:Allah ya isam ma Bello maitama yusuf
Sai kuma waƙoƙin fada na sarakuna inda
a nan ne ya shahara kuma a cikin wannan kashi aka saka shi. Watau
makaɗin sarakuna, a cikin rabe-raben mawakan Hausa ya yi waƙoƙin sarauta da
dama. Ga misalin daya daga ciki. Waƙar Aliyu yandato II.
Gindi waƙa :Bida arna bai yarda a kai mai wargiba
Mai wuyya gaba ya hana karya yandoto
Jagora:
Dansabagadi na jekada ya nike maza
Y/Amshi:
Waddara sun lakkwata,duk sun yaushi
Dansabagadi na jekada ya hada maza
Waddara sun lakkwata,duk sun yaushi
(Gusau,2005:108)
3.2.9 MATSAYIN KIƊA A WAJENSA
Hausawa na cewa: “Gado malan” Musa Ɗanƙwairo
ya dauki kiɗa da waƙa a matsayin gado. Saboda ya gaji kiɗa a wajen mahaifinsa.
Haka kuma waƙa a wajen Musa Ɗanƙwairo ya nuna
cewa sana’a ce a wajensa. Saboda ciki ya ke ci kuma ciki yake sha.
3.2.10 TAFIYE- TAFIYENSA.
Tafiya mabuɗin ilimi inji Hausawa. A
sanadiya sana’ar kiɗa makaɗa Musa Ɗanƙwairo ya yi tafiye-tafiye da dama. A
wannan dalili ne na kiɗa da waƙa Ɗanƙwairo ya riƙa bin sardauna Ahmadu har
Kaduna yana yi masa waƙoƙi.
Don
haka anan gida Nijeriya Ɗankwairo ya yawata garuruwa da birane da dama tun a
garinsu Maradun da Tsahe, da Sakkwato, da Daura, da Kano, da Jalingo, da
Gwambe, da Bauchi, da Barno, da Muri, da dai sauransu.
3.3 NAƊEWA
Mun
gabatar da shimfiɗa munyi ma’anar Al’ada da ra’ayoyin masana da ire-iren al’ada
da kuma naɗewa duk acikin babi na uku.
BABI NA HUƊU
LALUBEN AL’ADUN HAUSAWA A CIKIN WASU WAƘOƘIN
ƊANƘWAIRO
4.0 SHIMFIƊA
Babin
yana magana ne a kan Al’adun Hausawa da kuma lalubo wasu waƙoƙi a cikin waƙoƙin
Musa Danƙwairo sai dai Al’adun suna da yawa an lalubo kaɗan daga ciki.
4.1 AL’ADUN HAUSAWA
Kamar
yadda bayani ya gabata, duk abubuwan da akasarin jama’a na kowace al’umma su ka
amince da yin su, ko yin amfani da su ko suka yarda da su, sune al’adunsu. Idan
waɗannan abubuwa sun yi zaune da gindinsu, bayan sun samo asali tun daga kaka
da kakanni, shi kenan sun zama al’adun gargajiya. Da zarar al’ada ta kafu, ta
zama ta gargajiya, yana da wuya a tumɓuke ta farat daya.wannan ya sa da yawa,
akan yi ta ɗauki-ba-ɗadi kafin a sami damar kasha wata al’ada ta gadon-gado
Alal misali, duk da girman tasirin zuwan turawa ƙasar Hausa da yawa daga cikin
al’adun Hausawa na gargajiya, ba su yi wata sakewa ta a zo a gani ba.
Al’ummar
Hausawa mutane ne masu tsananin riƙo da Al’adunsu na gargajiya, sai dai kuma
al’ada aba ce mai rai wadda take tafiya tare da lokaci ko zamani. Don haka tana
iya samun gauraya da wasu baƙin al’adun har su ka ga karƃuwa ga wannan al’umma,
kusan wannan dalili ne ya haifar da karkasuwar ko rarrabuwar al’adun har zuwa
gida uku, wato al’adun gargajiya da gaurayayyin al’adu da kuma baƙin al’adu a
tsakanin al’ummar Hausawa da kuma cikin ƙasar Hausa. (Mu’azu,2013:2)
4.2 LALUBEN AL’ADUN HAUSAWA A CIKIN WASU
WAƘOƘIN ƊANƘWAIRO
A wannan babi za a lalubi wasu Al’adun Hausawa
waɗanda Musa Ɗanƙwairo ya faɗi a cikin wasu waƙoƙinsa tare da yin taƙaitaccen
sharhi na manufar da ta ke ƙunshe a ciki. Hakan ce za ta bamu hasken gane cewa
Ɗanƙwairo makaɗin baka na Hausa ne da ya taimaka wajen raya da taskece wasu
al’adun al’ummarsa.
4.2 WASU AL’ADUN HAUSAWA
Al’adun
Hausawa suna da yawa ga kaɗan daga cikin su.
v Neman Aure- kayan toshi, kayan zance, dukiyar aure, kayan lefe, Daurin Aure, Sa rana , garar Aure sa lalle, kamu,
wankan Amarya tarewa da sauransu.
v Haihuwa- akwai Al’ada kamar haka goyon ciki,kayan kauri, zanen suna, gara, reno,
yaye, kaciya, wankan biki da sauransu.
v Mutuwa- zaman makoki,itama wannan Al’ada ce tana ɗauke da wasu al’adu da ake yi
sun hada da zaman makoki ta’aziya takaba, wankan gawa, sutura da sauran su.
v Addini : Bangaren addini kuwa akwai addinin gargajiyar Hausawa suna da abubuwan
bauta kamar iskoki,magiro, gajimare, tsinburbura da sauransu.
v Abinci : Hausawa suna da abincinsu na gargajiya wadan suke amfani da shi a
rayuwar su tayau da kullum kamar irinsu tuwu,hura, danbu, wake, danwake wasa
wasa da sauransu.
v Bukukuwa : Suna daya daga cikin ire-iren Al’adun da Hausawa suke gudanar wa a
rayuwar su ta yau da kullum sun hada da Bukin budar kai, bukin budar daji,
kalan kuwa, bukin kaciya, bukin aure, haihuwa da sauransu.
v Wasanni : suna daga cikin Al’adar da Hausawa suke gudanarwa a rayuwar su, sun
hada da wasannin da yara suke a tsakanin su na kwaikwayon abubuwan da manya
sukeyi kamar wasar yar tsana, wasan kalan kuwa, dabo
dabo, dan akuyana daku aya, da sauransu.
v Sana’o’i : itama sana’a wata al’ada ce da Bahaushe yake gudanar wa domin samun
abun masarufi a rayuwar sa ta yau da kullum. Akwai sana’ar noma,farauta, kiyo,
kira, saka, dukanci, jima, fawa, kadi,dilanci da sauransu
v Mulki: shi ne shugabanci na jan ragamar al’uma. Wannan wata al’ada ce da Hausawa
suke yi ta hanyar naɗa wani daga cikin su don ya zama shugabansu, tun daga
maigida da iyalan sa. Akwai shugaban gida wato, mai gida da kuma shugaban
al’umma, wato sarki da kuma shugaban wasu ƙungiyoyi, da kuma shugaban masu wata
sana’a da kuma shugabannin siyasa, da sauransu.
v Taimako: Taimako wata dabiace ta Bahaushe, taimako na nufin ka agaza ko ka taya wani yin wani aiki Bahaushe yakan
agazawa gajiyayye ko kasasshe ko mabukaci.
v Atakaice waɗannan su ne kadan daga cikin ire-iren Al’ada Bahaushe, wadda yake
gudanarwa a rayuwarsa ta yau da kullun.
4.2.1 AL’ADUN
HAUSAWA A CIKIN WASU WAƘOƘIN MUSA ƊANKWAIRO
Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun ya ambaci
wasu Al’adun Hausawa a cikin, wasu waƙoƙinsa. Akwai inda yake
ambatar wata sana’a babba ta Bahaushe wato noma.
4.2.2 Noma : Noma
na ɗaya daga cikin al’adar Bahaushe wadda ta shafi sana’arsa da ya fara yi a
doron ƙasa lokacin da ya gama yawonsa na
farauta.
To idan muka duba makaɗa Musa Ɗanƙwairo ya nuna wannan
Al’ada ta sana’ar noma a cikin waƙar da ya fara yi ta ya’yan sarakuna. Mawaƙin
na cewa.
Gindin
waƙar
Ɗan sarki a gode
maka
Jikan Dodo ɗangwamma
Jagora: Ya tafi daji bashi komowa
Y/Amshi : Kullun daga duƙe sai
duƙe
Gyaɗo mai ƙoƙarin gaske. ( Gusau,2019 :54)
A nan makaɗin ya nuna mana cewa
Bahaushe yana da wata Al’ada ta yin noma a matsayin wata sana’a da zai yi domin
samun abincin rayuwa. Kalmar duƙe tana nufin noma,Kamar yadda Bahaushe yake
cewa
“Na duƙe tsohon ciniki kowa ya zo
duniya kai ya tarar.”
Har a
ciki ya ƙara cewa:
Jagora : Jikan
Namadi kullum ango
Y/Amshi: Karsanin Ali
Gungaman Iro dan Jatau
Kullun daga duƙe sai duƙe
Gyaɗo mai ƙoƙarin
gabce.
Dan sarki a gode
maka
Jikan Dodo ɗan
Gwamma. ( Gusau 2019:54)
Abincin Hausawa shi ma wani nau’i ne na al’adun
Hausawa. A cikin waƙar Aliyu na II wato
‘Yandoton Tsafe mawaƙin na cewa:
Gindin
Waka : Bi da arna bia yarda
:
A kai mai wargi
:
mai wuyan gaba
:Ya
hana karya “Yandoto”
Jagora : :Wani ya
barkace
:
Yana shawagi biɗak kaɗe
:
Aljihu twake da kashin bauna
Jagora: Iko
ya yi
Y/Amshi : Gardama, ɗan sarki na bisa kaiwa kullum
Jagora : :
Ina abu !
:
Bi da arna bai yarda
:
A kai mai wargi ba
:
Mai wuyya gaba
:
Ya hana karya ‘ Yandoto
A nan kaɗe
da kaiwa duk wani nau’in abinci ne na Hausawa,
A cikin ƙamusun Hausa,(Hausa. (2006 : 223) an kawo ma’anar kade da
(1) Kadanya (ii) ko mai wanda ake samu daga ‘ya’yan kadanya ‘ Kaiwa’ kuma tana
nufin ‘ya’yan kanya. (ƙamusun Hausa 2006 : 226).
Jagora : Naɗe mani sarkin kiɗi
Y/Amashi :
Na jekada, mui ta duniya
;
Kurna naga sarkin ƙaya
:
Danƙwairo makaɗin ‘yandoto’
;
Bi da arna bai yarda
: A kai
mai wargi ba
:
Mai wuyag gaba
:
Ya hana ƙarya ‘yandoto.
4.2.3
Ubangida: Wannan
wata al’ada ce da aka san mawaƙan Hausawa suna da iyayen gida. Waɗanda su ke ɗauke da nauyinsu. Wannan
al’ada ta fito a cikin wata waƙa da Musa Ɗanƙwairo ya yi wa Alhaji ‘Yandoton
Tsafe.
A nan munga cewa shi Kurna mawaƙin sarkin
ƙayan Maradun ne, shi kuma ƙanensa watau Musa Ɗanƙwairo makaɗin ‘Yandoton Tsafe
ne, Aliyu ‘Yandoto na II. Idan mun duba wannan
al’ada ce ta ta galibin sarakunan ƙasar
Hausa.
4.2.4 TA’AZIYYA: Al’ada ce ta Hausawa
idan mutum ya ƙaura, ko kuma ya rasu to ana yin ta’aziyya, ko gaisuwa da nuna
alhini na rashinsa.To an samu haka a cikin waƙar ta’aziyya ta marigayi Sir
Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato. Mawaƙin na cewa:
Gindin waƙa:
Gindin
waka: Ya wuce raini ba a yi mai shi,
Amadu Jikan Garba Sadauki,
Jagora
: Firimiyan jihar Arewa Amadu
Abin da kai ma Nijeriya,
Hak ƙasa ta naɗe, ana
tuna ka
Y/Amshi : Amadu Jikan bawon Allah
Gamji ɗan ƙwarai
Gohe Allah,
Malam Gohe, Allah gafarta ma.
Jagora : Malam
Y/Amshi : :Amadu Allah
dai ya jikai nai
Jagora : :Gaba
ta wuce,
:Yanzu a samo wani
kamatai
:Ya wuce rani ba a yi
mai shi
:Amadu jikan Garba
Sadauki
To mun ga makadin yayi addu’a irin ta
ta’aziyya haka ya fito a cikin wannan ɗiyan waƙa guda 2 da ya yi wa Sardaunan
Sakkwato, Ahmadu Bello.
4.2.5 GADO: Wannan shi ma wata Al’ada ce ta
Hausawa idan magabaci ya rasu sai ya samu wanda zai gaje shi. To haka
ta samu a cikin wata waƙa da Alhaji Musa Ɗanƙwairo ya yi wa ‘Yandoton Tsafe.
Mawaƙin na cewa:
Jagora :Batun kiɗi ko ba ku nan yi mu kai,
:Kun karantar da mu,
:Mun yi kiɗan baki,
:Mun yi wasulla, mun yi tayi
:Yanzu ilmi mukai tun da mun sabka
:In hwa waƙa ce,
:Duk mun san yadda za
mu ƙulla ta,
:In ance mutum mai
tujara ne,
:Sai ya haihuwa da
mai tujaran nan,
:In Allah ya ba mutum kwazo,
:Ya bar haihuwa da
nai ya lalace
:Tun da gado ne
:Mun gani tun ga
diyan masara,
:Abun goye kowa da
gemu nai.
To anan
mun ga Kalmar gado ta fito a cikin wannan waƙa. Gado kamar yadda aka bayyana a
ƙamusun Hausa (2006: 149) yana nufin, dukiyar da mamaci ya bari ko muƙami ko
hali ko sifa ko kaya da mutum ya gada. Don haka anan za mu ce Musa Dankwairo
yana nuna wannan sana’a ta kiɗa gadar ta suka yi sun kuma ƙware a cikinta, sun
gaji muƙamin yi wa sarakuna waƙa, sun gaji kiɗan kotso da yanayin aiwatar da
waƙar gaba ɗaya.
Idan ba a manta ba a can baya an yi
bayanin yadda ya gaji kiɗan daga kakanni da iyaye har ma da wansa Kurna. Wannan
Al’ada ta gado, Al’adar Hausawa ce tun kafin musulunci sai dai da musulunci ya
zo ta tsara yadda gado yake saƃanin yadda yake a al’ada.
Gindin waƙa:
:Kar
mu sake mu mance
:Ku
bi al’adunmu na gargajiya
:Mu
bi al’adunmu na gargajiya.
Jagora : Kyawon Dan arewa Babbar
Riga
:Ga rawani
da taggo
:Mubi al’adunmu na garagajiya.
Anan mun ga cewa riga da taggo da rawani duk sutura ce
ta Bahaushe. Wanda kuma sutura na ɗaya daga cikin kayan Al’ada na Hausawa, mun
ga yadda suka fito a cikin wannan waƙa ta Alhaji Musa Ɗanƙwairo.
Bangaren
addinin musulinci kuma an san Bahaushe da al’adar riƙa tasbaha (carbi) domin
roƙon Allah. Ɗanƙwairo ya ambaci cewa a riƙa amfani da tasbaha a cikin wannan
waƙa tasa ta al’adun gargajiya. Inda yake cewa:
Jagora:
:Kai abun ga ya ban takaici
:Abun ga ya ban takaici
:Sai ka ga ɗan Musulmi
:Da wandon yadi guda
:Ga‘yar shat ya sa ga
wuyanai
:Ba hulla ga kai nai
:Aljihu nai ba tasbaha
Y/Amshi : : Sai kwalin sigari.
Idan mun dubi wannan ɗan waƙar
Ɗanƙwairo ya Ambato kayan Al’ada na Hausawa kamar Hulla, da kuma tasbaha.
4.2.6 LULLUƁI: Shi ma ɗaya ne daga cikin al’adar Hausawa musamman ga matan Hausawa, idan
za su fita.To haka ya fito a cikin wannan waƙar ta Al’adun gargajiya. Inda
mawaƙin ke cewa:
Jagora : :Ku
ko matan ƙasarmu
:Waɗanda suke ɗiyan musulmi
:Ku zanka yin lulluɓi
:Ban da, sayen ‘yakkanti
:Banda sayen ‘yakkant
:Kuna ta yawo rariya-rariya
Jagora :Abin ga ya bada kunya.
4.2.7 ABINCI: Duk a
cikin waƙar ya ƙara kawo abincin Hausawa na Al’ada. Inda yake cewa:
Jagora : Inda haka gaskiya ne
:Ku mance hura da nono
:Sannan ku mance Tuwo da nama
Y/Amshi : Mu bi al’adunmu na gargajiya,
:Kar
mu sake mu mance,
:Mu bi al’dunmu na
gargajiya.
Tuwu da miya
abincin Hausawa ne wanda suke ci suke sha hura da nono ma haka abincin Hausawa
ne da suke sha domin maganin yunwa wadannan sune abincin Hausawa na Al’ada.
4.2.8 SANA’A: Sana’a Sa’a inji Hausawa, wata babbar al’ada da Alhaji Musa Daƙwairo ya
ambata a cikin wata waƙa da ya yi mai suna “Noma babbar Sana’a” mawaƙin na
cewa:
Gindin
waƙar:
:Noma
babbas sana’a
:Kaway
yi ta ya bar rasawa X 2
Jagora : Ku zan aje noma daidai ne
:Kowa aje gero da
dawa
:Ku zan tsare noma daidai ne
Y/Amshi : :Kowa aje gero da dawa
:Wannan ya ɗebe takaici.
:Noma babas sana’a
Jagora ; :Taimaki bayin ka Allah
:Allah kai a mai iyawa.
:Noma babbas sana’a
4.2.9 ROƘO: Roƙo shi ma wata al’ada ce musamman ga mawaƙanmu na Hausa. Mun ga haka a
cikin waƙar “Alhaji Shehu Shagari, Tsohon Shugaban ƙasa”.
Gindin
waƙar:
Shugaban
ƙasa jikan Sule,
Wada
duk aka so ya kai,
Jagora: Sarkin Gwaram
Y/Amshi: Waziri ban rena mai ba,
Jagora : :Alhaji Baba Umar
:Ya rabbana ya kara
wadata ka
Jagora :Umaru jikan mamman
Y/Amshi: Ya rabbana ya ƙara wadata ka
Jagora : Na zo ka ba ni mota,
Albarkacin girman mai girma,
Na zo ka bani mota ta hawa,
Darajar girman maigirma.
To anan munga cewa duk wata ɗabia
ce mawaƙan Hausa, idan suna waƙa sukan roƙi abu ga waɗanda suke yi wa waƙa. Ko a
bayyane ko a boye. To wannan ita ma wata Al’ada ce ga Hausawa.
Gindin
waƙar:
Na
Alhaji Abba mijin maza
Na yadda da Ado Ɗandawaki
Jagora Kai ne mulki ne ilmi
Ba
a hika taimako ba Addo
Alhaji
Ado ka yi komi
Jagora : Dan dattijo
Y/Amshi: Ni Alhaji Ado ka yi komi
Jagora Taimaki gazajje
Taimaki maraya
Y/Amshi:
Alhaji Ado Ɗandawaki
Jagora : Ya bai wa gazajje
Ya bai wa maraya
Y/Amshi: Alhaji Ado Ɗandawaki
Jagora
Ka ba kuturu
Ka ba makaho
Y/Amshi Alhaji Ado Ɗandawaki.
Gazajje da maraya da kuturu da makoho duk
masu neman taimako ne, don haka Danƙwairo ya nuna Alhaji Ado Dandawaki yana
taimaka musu, ya kuma yabe shi saboda wannan al’ada ta taimako.
A taƙaice waɗannan
al’adu da muka tsakuro muka lalubo a
cikin wasu daga waƙoƙin Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun, Sun isa zama hujja
waƙoƙin makaɗin cike suke da Al’adun Hausawa waɗanda za a yi alfari da su a
kuma nunawa duniya.
4.3 NAƊEWA
Mun gabatar da shimfiɗa a babi na huɗu Al’adun Hausawa da
ire-iren al’ada da laluben wasu al’adu a cikin wasu waƙoƙin Musa Ɗanƙwairo
Maradun duk a cikin babi na huɗu.
BABI
NA BIYAR
SAKAMAKON BINCIKE
5.0 SHIMFIƊA
A
cikin wannan babi za a kawo bayanai ne waɗanda suka ƙunshi taƙaitaccen bayani
dangane da wannan bincike da aka gabatar, sai kuma sakamakon da binciken ya
gano.
Wannan
bincike ne mai suna laluben wasu Al’adu a cikin wasu waƙoƙin Alhaji Musa
Danƙwairo Maradun. A wannan aikin an yi gabatarwa dangane da muhimman matakai
masu nuna alƙiblar da aikin ya dosa kamar taƙaitaccen bayani akan waƙoƙin baka
na Hausa da nuna cewa suna cikin ƃangaren adabi. Haka kuma an kawo muhimmancin
kiɗa da waƙa a ƙasar Hausa. Wannan aiki kuma ya kawo laluben wasu al’adu a
cikin wasu waƙoƙin Alhaji Musa Ɗanƙwairo.
A
babi na ɗaya haka kuma an kawo dalilin bincike da manufar bincike da
iyakancewar bincike da hanyoyin da muhimmancin bincike sai matsalolin bincike
da kuma naɗewa.
A babi na biyu daga nan sai aka yi bitar
ayyukan da suka gabaci, wannan binciken a matakan ilimi mabambanta kamar
rubutattun littafai da muƙalu da kuma kundayen bincike.
A babi na uku daga nan kuma sai aka bibiyi
ma’anar Al’ada da ire-iren al’ada da tarihin rayuwar Makaɗa Alhaji Musa
Ɗanƙwairo Maradun. Kamar sunansa da laƙabinsa da asalin iyayensa da shekarun
haihuwarsa da iliminsa da kuma bayanin rayuwarsa ta aure watau, iyalansa da
lokacin daya fara kiɗa da waƙa. Haka kuma an kawo nau’in kayan kiɗansa da
ire-iren waƙoƙinsa tare da nuna matsayin kiɗa a wajensa da kuma bayanin
tafiye-tafiyen da ya yi a lokacin da yake gudanar da wannan sana’a ta kiɗa da
waƙa.
A cikin babi na huɗu a wannan bincike an
kawo bayani akan al’adun Hausawa, da ma’anar al’ada da kuma ire-iren al’adun
Hausawa haɗi da kawo laluben wasu al’adu a cikin wasu daga waƙoƙin makaɗa
Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun.
Daga
nan sai wannan bincike ya zo da jawabin kammalawa, sai kuma taƙaita bayanin
bincike da sakamakon abin da binciken ya gano sai manazarta.
5.1 SAKAMAKON BINCIKE:
1. Angano
makaɗa Ɗanƙwairo mutum ne mai iya fito da Al’adun Hausawa a cikin waƙoƙin sa
2. Makaɗa
Ɗankwairo yana nuni da ƙyawawan Al’adun Hausawa da nufin zaburarwa.
3. Waƙoƙin
na sa ma’adani ne na ƙunshe Al’adun Hausawa musamman na gargajiya.
4. Waƙoƙin
nasa tamkar madubi ne ga masu son sanin Al’adun Hausawa.
5.2 SHAWARWARI
A sakamakon binciken da aka gudanar a kan
laluben al’adun a wasu waƙoƙin Musa Ɗanƙwairo Maradun da irin tasirin da suke
da shi ga rayuwar al’adun Hausawa. Binciken na ba da shawarwari kamar haka:
-
Dalibai manazarta waƙoƙin Hausa su dage
wurin gudanar da bincike kan waƙoƙin Hausa da ake da su domin fito da irin gudunmuwar
da suka bayar wa da jawo hankalin matasa don kulawa da al’adun gargajiya.
-
Shawara ga makarantun sakandare har zuwa
na manyan makarantu na jami’oi da su rika taskace ire-iren waɗannan waƙoƙin
domin saƙonnin da suke ciki na bunƙasa al’adu.
5.3
NADEWA
A ƙarshen wannan babi na biyar anyi taƙaitaccen bayani dangane da
binciken da aka gabatar sai sakamakon bincike, wannan bincike mai suna Laluben
Al’adu a cikin wasu waƙoƙin Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun anyi shimfiɗa,an kawo
mahimmancin kiɗa, ankawo dalilan bincike sai bitar ayyukan da suka gabata,
tarihin makaɗi da laƙabinsa duk a cikin babi na biyar.
MANAZARTA
Adamu
Aisha Ismail (2002) “ Salo da Sarrafa
Harshe a cikin Wasu Waƙoƙin Jam’iyyun
A.N.P.P da P.D.P a Jihohin kano da jigawa kundin digiri na Biyu. Sashen koyar
da harsunan Nijeriya. Kano Jami’ar Bayero.
Ammani, M. (2009) Nazarin Maganganun Hikima a Waƙoƙin
Aliyu Ɗandawo kundin digiri na biyu sashen koyarda harsunan Nijeriya. Kano.
Jami’ar Bayero.
Auta,
A.L (2017) Fadarkarwa a Rubuttattun Waƙoƙin Hausa. Kano. Jami’ar Bayero.
Bello A. M da Bashir I. (2004) Harshe da al’adun
Hausawa, sashen koyar da Harsunan
Nigeria.Kano : FCE
Bunza, M.A (2006)
Gadon Fede Al’ada. Lagos: Tiwal Nigeriya limited
Bunza,
M.A. (2009) Narambada. Lagos: Ibrash Islamic Publication Centre Limited.
Dangambo, A. (1984) Rabe-Raben Adabin Hausa da
Muhimmancinsa ga Rayuwar Hausawa. Kano:
Triumph Gidan sa’adu zungur.
Dangambo,
A. (2007) Daurayar Gadon Fede waƙa. Kano: Amana Publishers.
Dangambo, A.
(2011) Rabe-Raben Adabin Hausa (Salon Tsari) Zaria; Amana Publishers.
Garba,
M. (1998 “ Azancin Magana a Waƙoƙin Makadan Baka. Kundin Digiri na Biyu. Sashen koyar da Harsunan Nijeriya
Kano: Jami’ar Bayero.
Gusau, S.M (2002) Salihu Jankidi Sarkin Taushi. Kaduna:
Baraka press and Publishers.
Gusau,
S.M (2005) Makada da Mawakan Hausa. Kano: Benchmark Publishers Limited.
Gusau,
U.G. (2012) Bukukuwan Hausawa Gusau. Ol-faith Prints.
Gusau,
S.M (2013) Dangantakar Waƙoƙin Baka da Al’adun Hausawa: Bunƙasa ko Koma-baya
Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya. Kano Jami’ar Bayero.
Gusau,
S.M. (2014) Diwanin Waƙoƙin Baka Juzi’i na Biyu. Kano: Century Research and
Publishers Limited.
Gusau,
S.M. (2015) Abdu Karen Gusau. Kano: Century Research and Publishers Limited.
Ibrahim M.S (1985) Dangantakar Al’ada da Addini;
Tasirin Musulunci kan Rayuwar Hausawa ta
Gargajiya” Kundin Digiri na Biyu. Kano Jami’ar Bayero.
Magaji, A. (Babu shekara) Wasu Al’adun Hausa:
Yanaye-Yanayensu a Ƙasar Katsina. Kundin Digiri na uku. Kano, Jami’ar Bayero.
Ma’azu, A. (2013) Bakin Al’adu a Kagaggun Littafan
Soyayya Na Hausa. Zariya. Ahmadu Bello University Press Limited.
Sankalawa,
I.B (1994) Nazarin Rayuwar Makaɗa Sani Sabulu Kanoma da Falsafar Waƙoƙinsa.
Kundin Digiri na Ɗaya. Sashen Koyar da Harsunan Nigeriya. Kano: Jami’ar Bayero.
Umar,
M.B. (1987) Dangantakar Adabin Baka da Al’adun Gargajiya. Kano: Triumph.
Yahaya,
I.Y da Dangambo, A (1986) Jagoran Nazarin Hausa. Zaria: Northern Nigerian
Publishers Company Limited.
Yakasai,
A.S (2003) “Sadarwa Tsakanin Maza da Mata: Nazarin Dangantakar Harshe da
Daidaituwar Jinsi” Mukala day a gabatar a taron kara wa Juna Sani, Sakkwato. A
sashin koyar da harsunan Nigeria Jami’ar Usman Danfodiya.
Yakubu,
G (2012) Adon Harshe a Waƙoƙin Mamman Shata na Masu Sarauta Kundin Digiri na
Biyu. Sashen Koyar da Harsunan Nigeriya. Kano: Jami’ar Bayero
Yahaya A. D, (1980) The Authority System in Northern
Nigeria (1950 – 70) Zaria, Ahmadu Bello University Press Yohanna, S. (1988) the
Colonial State.
Yaro, S. A. (1997) Development of Pressrout For The
Beneficial of Mallam Ayuba Manganese deposit to penomanganese feedcwado. PHD
thesisi ABU Zaria Unpublished.
RATAYE NA 1
Waƙar al’adun gargajiya.
Gindin waka: : Karmu sake mu mance
:Mu bi
al’adunmu na gargajiya X2
Jagora :Mu bi al’adunmu na gargajiya
Y/Amshi :Kar ku sake ku
mance,
Mu bi al'adunmu na gargajiya. X2
Jagora
: :Niyyah kai !
Y/Amshi :Karmu sake mu mance
:Mu bi al’adunmu na
gargajiya X2
Jagora
: :Kyawon Ɗan 'arewa
babbar riga,
:Ga rawani da
taggo,
Y/Amshi
: :Mu
bi al’adunmu na gargajiya.
Jagora
: :Kyawon Ɗan arewa babbar
riga,
Y/Amshi : :Ga rawani da
taggo.
Jagora
: :Ko ranar suna,
:Ko Jumu’a ka ɗauka,
:Mu bi al’adunmu na
gargajiya.
Y/Amshi : :Mu bi al'adunmu
na gargajiya,
:Kar mu
Sake mu mance,
:Mu bi al'adunmu na gargajiya.
Jagora:
:Yan'arewa da an nan,
:Waɗanda ad ɗiyan
Musulmi,
:Ƙwairo na gargaɗinmu,
:Ku zan azumi da
sallah,
:Ku zan kono da
zakka,
:A zan azumi da sallah.
Y/Amshi
: :Ku bi al'adunmu na
gargajiya,
:Kar mu
sake mu mance,
:Mu bi al'adunmu na gargajiya.
Jagora: :Ku ko matan
kasarmu,
:Waɗanda suke ɗiyan
Musulmi,
:Ku zanka yin lulluɓi,
:Ban da sayan yarkanti,
:Kuna ta
yawo rariya-rariya,
:Abin ga
Y/Amshi: :Ya ba da kunya,
:Mu bi al'adunmu na
gargajiya.
:Kar mu sake mu mance,
:Mu bi al'adunmu na gargajiya.
:Ku ko matanmu
Arewa,
:Waɗanda ad ɗiyar
Musulmi,
Jagora :Ban da sayan siket da
"yarkanti,
:Kuna yawo
rariya-rariya, abin ga ya ba,
Y/Amshi
: ;Mu kunya,
:Mu bi al'adunmu na gargajiya.
:Kar mu sake mu mance,
:Mu bi al'adunmu na
gargajiya. x2
Jagora
: :Abin ga da ban takaici,
x2
:Sai ka ga ɗan Musulmi,
:ga wandon yadi guda,
:Ga 'yar shat ya sa ga wuyana,
:Ba hula ga kai nai,
:Aljihu nai ba
tasbaha sai,
Y/Amshi: :Sai kwalin
sigari.
Jagora: :Aljihu nai
ba tasbaha,
Y/Amshi: :Sai kwalin
sigari,
:Mu bi al adunmu na gargajiya.
Jagora : :"Yan'arewa
Musulmi,
:Kun ce ba ku son
babbar riga,
:Ina ganin ku,
:Kun ce ba ku son
babbat taggo,
:Ina ganin ku,
:Kun ce ba ku son babban wando,
:Ina ganin ku,
:To, in
haka gaskiya ne,
Y/Amshi : :Ku mance hura
da nono,
:Mu bi al'adunmu na
gargajiya,
:Kar mu sake mu mance,
:Mu bi al’adunmu na gargajilya.
Jagora :In haka gaskiya ne,
YAmshi: :Mu mance hura da nono,
Jagora :Sannan a
mance tuwo,
Y/Amshi: :Tuwo da nama,
:Mu bi al'adunmu na gargajiya,
:Kar mu sake mu
mance.
Jagora :Ko da kana da mota,
Y/Amshi
: :Ka sai dokinka ka ɗaure,
Jagora :Ko da kana da mota,
Y/Amshi :Ka sai dokinka
ka ɗaure,
Jagora :Wurin mota
daban ne,
:Kuma,
Y/Amshi: :Wurin doki
daban ne,
Jagora :Wurin mota
daban na,
:Kuma,
Y/Amshi :Wurin doki
daban ne,
:Mu bi al'adunmu na gargajiya.
Jagora : In ka tashi hawan doki,
:Ka hau ka yo,
Y/Amshi : : Kilisa,
:Ka dawo gida ka daure,
:Mu bi al'adunmu na
gargajiya,
:Kar mu sake mu mance,
:Mu bi al'adunmu na gargajiya.
RATAYE NA 2
Makaɗi : :Alhaji Musa
Ɗanƙwairo
Waƙar :
Nona
G/Waka :Noma
babbas sana’a,
:Koway yi ta ya
bar rasawa.
Jagora :Noma babbas sana'a,
Y/Amshi
: :Koway yi ta ya bar rasawa, x2
Jagora: :Ku zan aje noma daidai ne,
Kowa aje gero da
dawa,
:Ku zan tsare noma
daidai ne,
Y/Amshi : Kowa aje gero
da dawa,
:Wannan ya ɗebe takaici,
: Noma babbas sana'a,
: Koway yi ta ya bar rasawa.
Jagora: : Taimaki
bayin ka Allah,
Y/Amshi : Allah kai an mai iyawa,
: Noma babbas sana’a.
Jagora :Taimaki
bayin ka Allah,
Y/Amshi : :Taimaki bayin ka Allah,
: Allah kai am mai
Iyawa,
: Noma babbas
sana'a,
Jagora :Can dauri Nijeriya ƙasarmu,
:Allah ya ba ta
arzikin noma kasan nan,
:Mu noma gero mu
noma dawa,
:Ga shinkafa ga
gyaɗa,
:Ga auduga muna
noma,
:Ga masara kuma ga
shinkafa,
:Ga acca kuma ga
maiwa,
:Ga alkama muna
noma,
:Arkikin man fetur
ya motso,
:kasuwar man fetur tat tashi,
:Duk munka watsar da noma,
:Munka koma a kan kwangiloli,
:To ga shi arzikin fetur,
:Yanzu ya kare kasar nan,
:Can kasan da muke kaiwa,
:Can Kasashen da muke kaiwa,
:Kassuwan mai ta kare
,
:To ku 'yan Nijeriya,
:Yanzu me za mu
komawa,
:Gara mu koma kan
noma,
:Gara mu koma gun
noma,
:Mu tara abinci
ƙasarmu,
:Mu samu abinnci da
za mu ci,
:Mu yi sutura
ƙasammu,
:Mu sami abin yin
sutura,
:Kana sannan mu neme
kuɗɗi,
:Mu kare mutunci na kanmu,
Y/Amshi
: :Mu kare mutuncin ƙasag ga,
Jagora : Mu kare mutunci na kanmu,
Y/Amshi
: :Mu kare mutuncin ƙasar ga,
Jagora : Kun san gero da dawa,
:Da sauran abin za mu ci,
:Shi muka ci a Nijeriya,
:Amma auduga da gyaɗa,
:To ita ce za mu ɗauka,
:Mu kai ta can kasashen waje,
:Mu sayar mu samo
kuɗɗi,
:In dai munka samo
kuɗɗi,
:Mu gina asibiti,
:Domin kiyon
lafiyammu,
:Mu kare mutunci
na kanmu,
Y/Amshi :Mu kare mutuncin ƙasag ga,
Jagora: :In mun samo kuɗɗi mun tara,
:Kana mu gina
godabe,
:Masu zagaya
Nijeya,
:Kayan unhwanin
gona,
:Ko ina aje a kai,
:Mu kare mutuncin
ƙasag ga,
Y/Amshi
: :Mu kare mutunci na kanmu,
Jagora : Mu kare mutunci na Kammu,
Y/Amshi :Mu kare mutuncin ƙasag ga,
Jagora :In dai mun sami kuɗɗi da yawa,
:Sannan mu gine makarantu,
:Gara mu je mu nemi ilmi,
:Mu kai ‘ya ‘yanmu Su sami ilmi,
:Mu kare mutunci na kanmu,
Y/Amshi
: :Mu kare mutuncin ƙasag ga,
Jagora :Kowa ya kare mutunci na kainai,
Y/Amshi :Yakare
mutinci ƙasag ga,
:Noma Babbas
sana'a.
Jagora :Wada duk muka so Nijeriya,
:Mutane dun na hore ku,
:Manyan
garuruwanmu,
:Kowane gari
kazzo,
:Ka hangi dala ta gyaɗa,
:Ka hangi dala ta auduga,
:Kowane dum mun
tara,
:In dai mun mike
mun yi kwazo,
:Mun kare mutunci
na kannmu,
Y/Amshi
: :Mun kare mutuncin ƙasag ga,
Jagora
: :Mun kare mutunci na kanmu,
Y/Amshi
: :Mun kare mutuncin ƙasag ga,
Jagora
: :Darajar Nairammu da tah faɗi,
:To kuma sannan,
Y/Amshi :Za ta dauwa,
Jagora :Darajar Nairammu da
taf faɗi,
Y/Amshi : :To kuma sannan za ta
dauwa,
Jagora :To ku ma'aikatan Nijeriya,
:To ku tsaya kan
gaskiya,
:Kowa ya yi aiki don Allah,
:Kai ka
tsaya ga naka aiki,
:Nima
in tsaya ga nawa aiki,
: ln muyi haka nan mun taimaki
kanmu,
: In muyi haka nan mun yi daidai,
:Kar mu tsaya muna yin ƙeta,
:Muna cutar kanmu
da kanmu,
:Kai babba ka
shirga ɓanna,
:Sannan ka ce yaronka bai yi,
:Kowa duk ya tsaya ya dage,
:Mu kare
mutuncinmu zak kyau,
Y/Amshi
: :Mu kare mutuncn ƙasag ga,
Jagora :Mu kare mutuncinmu zak kyau,
Y/Amshi :Mu kare mutuncin ƙasag ga,
:Noma babbas
sana’a,
:Koway yi ta ya bar rasawa.
Jagora:
:Ku jama'an Nijeriya,
:Talakkawa da
Sarakuna,
:Da ku ma'aikatan Gwamnati,
:Alhaji Musa Ɗanƙwairo,
:Shi ma ya yi horon jama’a,
:Kowa ya kama noma
da gaske,
:Nima Alhaji
Ɗanƙwairo
:Bayan na aje
kotsannina,
:Na je Sakkwato
can gidana,
:Ni ma zan koma gona,
:In kama noma
kwarai da gaske,
:In tara gero in
tara dawa,
:In nemi abinci na
kaina,
Y/Amshi : : In nemi abinci na kaima,
x2
Jagora
: :Na kare mutunci na kaina, X2
Y/Amshi
: :Na kare mutuncin ƙasag ga, X2
:Noma babbas
sana’a,
:Koway yi ta ya
bar rasawa.
Jagora
: :Kowa ya tsaya ya yi aiki,
:Yawon banza,
Y/Amshi
` : Ba a so nai,
Jagora
: :Kowa ya tsaya ya yi
aiki,
Y/Amshi
: :Yawon banza ba a so nai,
:Noma babbas
sana’a,
:Koway yi ta ya
bar rasawa.
Jagora
: :Da ku ma'aikatan
government,
:‘Yan kasuwa da
talakkawa,
:Da manya-manyan
Sarakunanmu,
:Kowa ya ba da
goyon baya, X2
Y/Amshi : Mu taru mu ceto ƙasag ga, X2
Jagora :Jama’a,
YIAmshi : :Mu taru mu ceto ƙasag ga,
:Noma babbas sana'a,
:Koway yi ta ya bar rasawa.
Jagora :Kowa ya kama aikin daji,
: Kowa
nas san bai da aiki,
:Gwamma ya je ka ya
dau fartanya,
:Ya zo ya kama aikin
daji,
:In yai haka nan, x2
Y/Amshi: :Yayi daidai, x2
Jagora : :Kowa naz zan
bai da aiki,
:Yana yawo ga titi banza,
Y/Amshi
: :Irinsu ka ‘yan sace-sace,
. : Noma babbas
sana’a,
:Koway yi ta ya bar rasawa
Jagora:
:Taimaki bayin ka Allah,
x2
Y/Amshi
: :Allah kai am mai iyawa, x2
:Noma babbas
sana'a,
:Koway yi ta ya bar rasawa.
Jagora :Manyan Sojojin Nijeriya,
:Kowa
ya kama noma ƙwairo,
Y/Amshi
: :In kui haka nan kun yi
daidai,
Jagora
: :Manyan ‘Yansandan
Nijeriya,
: :Kowa ya kama noma
ƙwairo,
Y/Amshi
: :In kui hakan nan kun yi
daidai,
Jagora
: :Manyan Kwastanmu na
Nijeriya,
:Kowa ya kama noma
Kwairo,
Y/Amshi
: :In kui haka nan kun yi
daidai,
Jagora :Imagireshan da N.S.O.,
:Kowa ya kama noma
Kwairo,
Y/Amshi
: :In kui haka nan kun yi
daidai,
Jagora
: :Sarakunammu na
Najeriya,
:Kowa ya kama noma
ƙwairo,
Y/Amshi
:In kui haka nan kun yi daidai,
Jagora ‘Yan Kasuwa na Nijeriya,
:Kowa ya kama noma
Musa,
YIAmshi
:In kuyi haka nan kun yi
daidai,
:Noma babbas
sana’a,
:Koway yi ta ya bar rasawa.
Jagora :Sai mun aje gero mun aje
dawa,
:Ga
masara ga alkama,
:Ga shinkafa ga
masara,
:Idan abinci yat
taru,
Y/Amshi
: :In yai haka nan ya yi
daidai,
Jagora :Darajar noma,
Y/Amshi : :Za ta ƙaru,
Jagora :Domin isan
nan,
Y/Amshi: :Darajar Naira
za ta dauwa,
:Noma babbas sana'a,
:Koway yi ta ya bar rasawa.
Jagora: : Mun shirya
mun tara aiki,
:Ga ya nan a gabanmu jibge,
:To ku 'yan Nijeriya,
:Kara mu motsa mu miƙe,
:Mu kare
mutuncinmu ya fi,
Y/Amshi
: :Mu kare mutuncin ƙasag ga,
Jagora :Muna da abin yi ƙasanmu,
:Kun san mun sami
komai,
:Allah ya
albarkato ƙasar Nijeriya,
:Da arziƙi,
:Sai In mun ƙi yin biɗa,
:ln mun ƙi yin biɗa,
:In min miƙe mun nemi na kanmu,
:Allah za ya
taimake mu,
:Kowa nan nemi
taimako gun Allah,
:Sai ya yi mai,
:Diba min faɗin Nijeriya,
:Ko'ina akwai magurzayye,
:Na gurza auduga,
:Ko ina sannan Nijeriya akwai dala ta gyaɗa,
:Sannan akwai
dalan auduga,
:To diba yanzu
babu ko ɗai,
:Gara mu tashi mu kama aiki.
:Mu kare mutunci
na kanmu,
Y/Amshi
: :Mu kare mutuncin ƙasarmu.
Jagora :In munyi haka nan,
Y/Amshi :Mun yi daidai,
Jagora :Yawon banza,
Y/Amshi
: :Ba a so nai,
Jagora
:Yawon,
Y/Amshi
: :Banza ba a so nai,
Jagora :Aiki a yi domin Allah,
:Barna a bari kuma
domin Allah, x2
Y/Amshi
: :In mui haka nan mun yi
daidai, x2
Jagora :A Kama hanyoyin shara'a,
:Sannan shara’a a
kan gaskiya,
:in dai mutum na nashi aiki,
:To, bas shi da
nashi aiki,
:Shi ma shi bari in yi nawa,
Y/Amshi :Kat ma ka bari
1n yi nawa,
:In munyi haka nan
mun yi daidai,
Jagora :Ai in mui haka nan,
Y/Amshi : :Mun yi daidai,
:Noma babbas sana'a,
:Koway yi ta ya bar rasawa.
Jagora :Abin da ak
kyawu gare mu,
:Mu daina sha'awar
kayan waɗansu,
: Mu daina shawar
kayan waɗansu,
: Mu kuma shawar
kayan kasarmu,
: In mui haka nan,
x2
Y/Amshi : Mun yi daidai, x2
Jagora :Jama'a,
Y/Amshi :In mui haka nan
mun yi daidai,
::Noma babbas sana’a,
: Koway yi ta ya
bar rasawa.
jagora : Malam ka ce gyara kakai,
:Wai kai don kana
da mulki,
:Ko ko don kana da
arziki,
:Kaje ka sawo
kayan ƙasashen waje,
:Don ka sanya, ka
ƙi sayen na gidanka,
:Ka ɗau kuɗɗi ka
kai su can waje,
:Ka bar gida ba
komai,
:To wai kai wai
don ka waye,
:To su ko
talakkawa,
:Don sun zo sun yi
sawo can,
:To su ko sai ku ce sun yi laifi,
:Sai in kun kare
mutuncinku,
:Sannan su ma su yi koyi,
Y/Amshi :Su kare mutuncin ƙasag ga,
Jagora :
Su kare,
Y/Amshi : :Mutuncin ƙasag
ga,
;Noma babbas sana'a,
:Koway yi ta ya bar rasawa.
Jagora
: :Ko can gyara ya banna,
:Gwamnati na foron
Jama'a,
:Kowa ya kama aiki
da gaske,
:kowa na zan bai da aiki,
:wannan ya cuci kansa,
:Sannan
Y/Amshi :Ya cuci kainai, x2
Jagora :Sannan kuma,
Y/Amshi :Ya cuci kainai,
:Noma Babbas sana'a,
:Koway yi ta ya bar rasawa.
Jagora :Ɗanƙwairo na
sha dariya,
:Na iske
Bahillacen daji,
:Yana ta kiwon
shanunai,
:An ba shi furag
gero yas sha,
:Da nan sai yac ce miyatti,
Y/Amshi : :Gardi ne yar
ratsi kainai,
Jagora : :Gardi ne,
Y/Amshi : :Yar ratsa
kainai,
:Noma babbas sana'a,
:Koway yi ta ya bar rasawa.
Jagora: :Taimaki
bayinka Allah, x2
Y/Amshi : :Allah kai am
mai iyawa, X2
:Noma babbas sana'a,
:Koway yi ta ya bar rasawa.
Jagora : :Ku dai
manyan Nijeriya,
:Tun farko na ga laifinku,
:Kun kwashe arzikin Nijeriya,
:Wasu masu mugun hali,
:Waɗanda ad da
kishin ƙasa,
:nan sun tara kuɗɗinsu,
:Cikin NIjeriyarmu
daidai,
:Amma wasu ga shi
sun kwashe,
:Sun kai su can
wa' yansu ƙasa,
:Kai mai boyon wuta bonu,
:Ran da duk wutan
nan tak kama,
:Kai ka san,
Y/Amshi : :Ta bab barinka,
Jagora :Ran da duk wutan nan
tak kama,
Y/Amshi :Kai ka san ta bab
barinka,
:Noma babbas sana'a,
:Koway yi ta ya bar
rasawa.
Jagora :Kai ku zan riƙa noma
daidai ne,
:Kowa aje gero da
dawa,
Y/Amshi :Ka san ya ɗebe takaici,
:Noma babbas sana'
a,
:Koway yi ta ya
bar rasawa.
Jagora: :Tsohon aiki noma na
duƙe,
:Tsohon aiki,
Y/Amslhi :Noma na duƙe,
Jagora : :Tsohon aiki,
Y/Amshi :Noma na duƙe,
:Koway yi ka,
:Ya bar rasawa,
Jagora :Tsohon aiki,
Y/Amshi : :Noma na duƙe,
Jagora
: :Koway yi ka,
Y/Amshi :Ya bar rasawa,
:Noma babbas sana'a,
:Koway yi ta ya bar
rasawa.
Jagora: : Ga mai abinci yana jin daɗi,
:Ga raggo yana
Kallo,
:In lokacin damina
ta kama,
: Da lokacin
damina ta kama,
: Da Allah ya yi
ruwan sama,
:Kowa ya ɗauki
kwashe,
:Ya je gona ya
kama aiki,
:Shi ko raggo yana
kwancinai,
:Ga lokacin ɗiba
abinci,
:Ya zo kowa yana ɗiba
abinci,
:Raggo yana kallon su,
: :Domin
ba ya da komi Ɗanƙwairo,
:Domin Ka cuci Kanka,
:Ka ƙi aiki na daji,
:Kuma ba ka da aiki birni raggo,
:Amman Ka cuci,
Y/Amshi :Kanka,
Jagora : Raggo,
Y/Amshi : :Amman ka cuci
kanka,
: Noma babbas sana’a,
: Koway yi ta ya
bar rasawa.
Jagora
: :Noma tsohon aiki, x2
Y/Amshi :Koway yi ka ya bar rasawa, x
Jagora : Muna da arziki nan ƙasarmu,
:Allah Sarki ya
bar ga,
: Allah Sarki ya
albarkace mu,
: Da alhairin hatsi da auduga,
:Had da gyaɗa
Allah ya ba mu,
:Kowak kag ga yana
wahala,
Wannan bai yarda da Allah ba,
Ya ki
biɗar aiki da kyawo,
:Ya ki tsare aiki
da kyawo,
Y/Amshi
:Yawon banza yake yi,
Jagora :Wannan,
Y/Amshi
: :Yawon banza yake yi,
Jagora Yawon banza, X2
Y/Amshi
: :Ba a so nai, x2
Jagora :Daga yawo Sai,
Y/Amshi: :‘Yan sace-sace,
:Noma babbas
sana'a,
:Koway yi ta ya
bar rasawa.
Jagora:
:Taimaki bayin ka Allah,
Y/Amshi
:Allah shi am mai iyawa.
:Makaɗi Alhaji
Musa Ɗanƙwairo
:Wakar Gargaɗin
jama'a
G/Waƙa :A
yi aiki na gaksiya,
:Kam mu ɓatad da
kanmu.
Jagora
: :Kowa nab bi gaskiya,
:Ya kyauta,
Y/Amshi :Ma kai nai,
Jagora :Kowa nab bi gaskiya,
Y/Amsai: :Kowa nab bi
gaskiya,
:Ya kyauta ma kai
nai,
:A yi aiki na gaksiya,
:Kam mu ɓatad da kanmu.
Jagora
: :In dai nik kama waƙa,
Y/Amshi : :Ni kai ba, x2
Jagora
: :Kai ban his sad da kai
ba,
:Ni ban,
Y/Amshi: : His sad da kai na.
Jagora :Ban his sad da kai ba,
Y/Amshi :Ban his sad da kaina,
Jagora :Ke ban his sad da ke ba,
Y/Amshi
: :Ni ban his sad da kaina,
RATAYE NA
3
Makadi : Alhaji Musa
Ɗankwairo Maradun
Wakar :
'Yandoton Tsahe Alhaji Aliyu 1l (1960-1991)
G/Waka : Bi da arna bai yarda,
: A kai mai wargi da,
: Mai wuyag gaba,
: Ya hana karya
‘yandoto.
Jagora : Bi da arna bai yarda,
Y/Amshi : Bai yarda a kai mar
wargi ba,
: Mai wuyag gaba,
: Ya hana karya ‘Yandoto,
: Bi da arna bai yarda,
: A kai mai Wargı ba,
: Mai wuyag gaba,
: Ya hana karya ‘Yandoto.
Jagora : Dan Sabon Gari na Jekada,
: Ka nike maza,
Y/Amshi : Waddare sun lakkwala duk sun
yaushi,
Jagora : Dan sabon Gadi na Jakada,
: Ya haye maza,
Y/Amshi : Waddare sun lakkwata duk sun
yaushi,
: Bi da arna bai yarda,
: A kai ma wargi ba,
: Mai wuyag gaba,
: Ya hana karya
‘Yandoto.
Jagora : Wani ya barkace,
Y/Amshi : Yana shawagin bidak kade
: Aljihu twake da
kashin bauna,
: Bi da arna bai yarda,
: A kai mai wargi ba,
: Mai wuyag gaba
: Ya hana Karya
‘Yandoto.
Daudu : Iko ya yi,
Y/Amshi : Gardama, dan Sarki na bisa kaiwa kullum,
Jagora : Ina
abu!
: Bi da arna bai
yarda,
: A kai mai wargi
ba
: Mai wuyag gaba,
: Ya hana Karya
‘Yandoto.
Jagora : Ko can samu ka Jan sarauta,
Y/Amshi : Bakumbushi da za a nadi
: Ta ce masu sai kun dawo,
: Bi da arma bai yarda,
: Kai mai wargi ba,
: Mai wuyag gaba,
: Ya hana Karya ‘Yandoto.
Jagora : Ya hau da lahiya,
Amshi : Sabka lahiya, uban Sarkin Kofa ci maraya,
: Dodo wandara gwarzon Sani,
: Bi da arna bai yarda,
: A kai mai wargi ba,
: Mai wuyag gaba,
: Ya hana karya
‘Yandoto.
Jagora : Hawan da kay yi,
: Kai je Bilbis ran Talata,
: Ali dan Muhammadu,
Y/Amshi : Ka dibge
daji da doki,
: Sai ta jin nai kai,
: Bayanai gami da
barwa
: Sai hattara su kai,
: Kotsanni da masu gangumma duka suna hwadin,
: Ga bajimin
Garewa ya darzazo,
: Dimau na Amadu,
: Dan Shehu
tarnaki hanani,
: Ka bige Kangara,
: Ya koro makiya
duk sun bi,
: Bi da ama bai yarda,
: A kai mai wargi ba,
: Mai wuyag gaba,
: Ya hana karya
‘Yandoto.
Daudu : Ko can wargi.
Y/Amshi : Wuri garai,
: Mussar Jibda aka garkewa,
:Har ai mata iko,
: Kwa ishe damisa
hay yai izgilin da yag dwagas,
: Sai ya ci wuyatai danya,
: Bi da arna bai yarda,
: A kai mai wargi ba,
: Mai wuyag gaba.
: Ya hana karya
‘Yandoto.
Jagora : Nada mani Sarkin Kidi, x2
Y/Amshi : Na Jekada, mui ta duniya,
: Kurna na ga Sarkin Kaya,
: Dankwairo makadin ‘Yandoto,
: Bi da arna bai yarda,
: A kai mar wargi
Da,
: Mai wuyag gaba,
: Ya hana karya
‘Yandoto. x2
Jagora : Hadari kashe kaifin rana,
: Ci gari Ali gandon Gura-Guri
: Hadari,
Y/Amshi : Kashe karfin rana,
: Ci gari Ali gandon fashin tama,
: Bi da arna bai yarda,
: A kai mai wargi ba,
: Mai wuyag gaba,
: Ya hana karya
‘Yandoto.
Jagora :
Tsahe
gidan mai Kano ya yi kyau,
‘Y/Amshi : Ali ya dada shi bai rage masu,
: Alu ya rika karfi da masu,
: 'Yan jira dole sai kui ta hankuri.
Jagora : Cigari Ali,
‘Y/Amshi : Dutsin fashin tama,
Jagora : Zakı hadari kashe kaifin
rana,
‘Y/Amshi : Ci gari Ali dutsin tashin tama,
: Bi da arna bai yarda.
: kai mai wargi ba,
: Mai wuyag gaba,
: Ya hana karya ‘Yandoto.
Jagora : Wajen yaki Ali ka dauki girma,
: An san da
Yandoton Tsahe,
: Tun da fa Ali shi,
Y/Amshi : Bai fada su,
: Ya kari gaba na
Bubakar,
: Bai dauki reni ba mai masa,
: ‘Yandoto ka gaji kokari,
: Ya kori gaba na Bubakar
: Bai dauki reni ba mai masa,
: Yandotso ka gaji kokari,
: Bi da ama bai yarda,
: A kai mai wargi ba,
: Mai wuyag gaba,
: ‘Ya hana karya
‘Yandoto,
RATAYE NA 4
Makadi : Alhaji Musa Ɗankwairo Maradun
Wakar :
Alhaji
Ahmadu Bello, Sardaunan Sakkwaio
G/Waka :Ya wuce raini ba a yi mai shi,
: Amadu jikan
Garba sadauki,
Daudu : Ya wuce raini,
Y/Amshi : Baa yi mai shi,
: Amadu jikan
Garba sadauki,
: Ya wuce raini ba
a yi mai shi,
: Amadu jikan
Garba sadauki.
Jagora : Gungurun,
Y/Amshi : Kashin giwa na Alu ba ka haduwa,
: Kowac ci ka sai
ya cake makoshi,
Jagora : Gabas da yamma, kudu da arewa,
: An san kai ne Sardauna mai kwana kyauta,
Y/Amshi : Saboda baiwa, Amadu saboda
hairi aka sakanı ma,
: Yawuce raini ba ayi mai shi,
: Amadu jikan Garba sadauki.
Daudu : Firimiyan Jihar Arewa Amadu,
: Abin da kai ma Nijeriya,
: Hak kasa ta nade ana tuna ka,
: Amadu jikan,
Y/Amshi : Bawan Allah, gamji dan kwarai,
: Gamji na kwarai, gohe Allah,
: Malam Gohe Allah gafarta ma,
: Ya wuce raini ba
a yi mai shi,
: Amadu jikan
Garba sadauki.
Zwali :Firimiya mai halin
waliyyai,
: Sui maka shairi ka mai da hairi,
: Sui maka hairi ka
rama hain,
Y/Amshi : Wanga halin Shehu ya gado,
: Mahassada dai ka ta jidali,
: Amadu dan Iro ba
ruwanai,
: Ya wuce raini ba
a yi mai shi,
: Amadu jikan
Garba sadauki.
Daudu : Malam,
Y/Amshi : Amadu, Allah dai ya
jikai nai,
Daudu : Gaba ta wuce,
Y/Amshi : Baya ad da saura,
: Yanzu a samo wani kamatai,
: Ya wuce raini ba a yi mai shi,
: Amadu jikan
Garba sadauki.
Daudu : Gaba
ta wuce,
Y/Amshi : Baya ad da saura,
: Yanzu a samo
wani kamatai,
Jagora : Gaba ta wuce,
Y/Amshi : Baya ad da saura,
: Yanzu Ku nemo
wani Kamatal,
: Ba tsoro ba kariyaz
zucci,
: Ya gwada Jikan
Shehu,
: Amadu ya gwada
jIKan Shehu na shi.
: Ya wuce raini ba
a yi mai shi,
: Amadu jikan
Garba sadauki.
Jagora : Shi Amadu ya samu duniya,
: Ya kau gwada ya
samu duniya,
: Yai alheri ya rika kanne,
: Ya rika 'ya'ya,
ya rIka barwa,
: Ya rika bayi da,
Y/Amshi : Talakkawa,
: Ran Juma'a da
karhe biyu,
: Rannan yaki yac ci Amadu,
:Niy kuka niy
bakin rai,
: Nit tuna Allah, nim mashi muna,
: Da walakanci gara shahada ga Musulmi,
: Don ba illa ne ba,
: Da walakanci gara shahada ga Musulmi,
: Don ba illa ne Da,
: Ya wuce raini ba a yi mai shi,
: Amadu jikan Garba Sadauki.
: Bangon tama mai wuya iza,
: Bajimin Sir
Kashim,
: Uban Zagi Bello
dan Hassan,
: Mai martabar Danhodiyo,
: Mai martabar Mamman Bello,
: Mai martabar Abdulalhi,
: Mai martabar Attahiru,
: Mai martabar Moyi da Alto
‘Yan/Amshi : Da uwar Daje,
: Mai martabar Isan Kware Autan Shehu,
: Mai martabar Ibrahimu mai kahon kero,
: Sadauki dan
Sadauki,
: Kakaninka
waliyan Allah ne,
: Ba ba’a ba ko
can,
: Ya wuce raini ba
a yi mai shi,
: Amadu jikan
Garba sadauki.
RATAYE
NA 5
Makadi : Alhaji Musa Ɗankwairo Maradun
Wakar : Alhaji Bello Maitama Yusufu, Sardaunan
Dutse
G/Waka : Minista na Ciniki,
: Allah ya isam ma
Bello Maitama Yusut.
Jagora : Minista na ciniki,
: Allah ya isam ma
Bello Maitama Yusufu,
: Minista na
Ciniki,
: Allah ya isam ma
Bello Maitama Yusuf.
Jagora : Minista na ciniki,
: Allah ya 1sam ma
Bello Maitama Yusulu,
: Minista na
Ciniki,
: Allah ya isam ma
Bello Maitama Yusuf
Jagora : Kai Minista na ciniki,
Y/Amshi : Alah ya isam ma Bello Maitama Yusufu,
: Minista na
Ciniki,
: Allah ya 1sam ma
Bello Maitama Yusut.
Jagora : Taho ga ka ga maza,
Y/Amshi : Wandara uban Akka Ado Sarkin Fada,
: Minista na
Ciniki,
: Allah ya isam ma
Bello Maitama Yusuf.
Jagora : Dutsin fashin tama,
Y/Amshi : Sardauna uban Akka Ado Sarkin Fada,
: Minista na
Ciniki,
: Allah ya isam ma
Bello Maitama Yusuf.
Jagora : Dutsin fashin tama,
Y/Amshi : Sardauna uban Akka Ado Sarkin Fada,
: Minista na Ciniki,
: Allah ya isam ma Bello Maitama Yusuf.
Jagora : Gagarau sa maza gudu,
Y/Amshi : Ba a jan ka ranar yaki,
Jagora : Ki sake sa maza gudu,
: Ba a jan ka
ranar fada,
: Minista na Ciniki,
: Allah ya Sam ma
Bello Maitama Yusuf.
Jagora :
Wataranaa Alhaji
Ɗankwairo,
: Ina can Sakkwato
na shiga mota,
: Na dora kewayar
Dirmi,
: Sai nih hangi
jam mota,
: Da nig ga lambar
sano gare la,
: Sai nij ja birki
Ɗankwairo,
: Da nil leka,
: Han na yi zaton Maitama Bello ne,
: Ba Maitama Bello ne ba,
: Ashe Yusufu Matama nc,
: Da yaj je Sakkwato yad dawo0,
: Ya isko ni
gidana,
: Sai yad debo
kuddi da yawa yab ban,
Y/Amshi : Don Bello Maitama yab ba ni,
Jagora : Yac ce mani,
: Minista na Ciniki,
: Allah ya isam ma Bello Maitama Yusuf.
Y/Amshi : Don Bello Maitama yab ba ni,
Jagora : Yas sake debo kuddi,
: yac ce amshi
Ɗankwairo,
: Wannan kuddin,
kuddin, kudin mata ne,
: Yac ce wannan
kuddin,
Y/Amshi : Kudin mata ne,
: Minista na Ciniki,
: Allah ya isam ma Bello Maitama Yusuf.
Jagora : Ranar Karamar Sallah da anka
yi,
: Ina Sakkwato Ɗankwairo,
: Muhammadu Bello ya je Gwaram,
: Rannan ka yi
hawan yaki,
: Ni ban je ba nij ji labari,
: In ji 'yan
birnin Kano,
Y/Amshi : Duk sun je Gwaram,
: Wurin kallonka,
: Duk sun tafi
Gwaram,
: wurin kallonka,
Jagora : Zaki,
Y/Amshi : Duk sun tafi Gwaram,
: Wurin kallon ka,
: Minista na
Ciniki,
: Allah ya isam ma
Bello Maitama Yusuf.
Jagora : Da nid dade ban ga Bello ba,
: Sai nid dauko
mouata,
: Naj je ano wurin
nemanshi,
: Gurgura duisi
wargi gare ka,
: An san manya
suna cikin gimansu,
: Gurgura dutsi
wargi gare ka,
: An san manya
suna cikin gimansu,
: Ko can an san,
Y/Amshi : Manya suna cikin girmansu,
: Minista na
Ciniki,
: Allah ya isam ma
Bello Maitama Yusuf.
Jagora : Alhaji uban Alhaji Sadauki,
Y/Amshi : Alhaji uban Alhaji Sadauki,
Jagora : Alhaji uban Alhaji Sadauki,
Y/Amshi : Alhaji uban Alhaji Sadauki Mamman,
: Minista na
Ciniki,
: Allah ya isam ma
Bello Maitama Yusuf.
Jagora : Gagarau mai ban tsoro,
: Ki sake ba a jan
ka,
Y/Amshi : Ranar yakl,
Jagora : Zaki
Y/Amshi : Ki sake ba a jan ka yakı,
: Minista na Ciniki,
: Allah ya isam ma
Bello Maitama Yusuf.
Jagora : Giwa ba ta Kaho,
: Kowac ce ta yi
Kaho,
Y/Amshi : Karya ne, x2
Jagora : Giwa,
Y/Amshi : Kowac ce ta yi Kaho,
: Karya ne,
Jagora : Dutsin fashin tama,
: Sardauna uban Akka Ado Sarkin Fada,
: Taho ga ka ga maza
Y/Amshi : Sardauna uban Akka Ado Sarkin Fada,
Jagora : Dutsin tashin tama,
: Ci fansa
Y/Amshi : Uban Akka Ado Sarkin Fada,
Jagora : Taho ga ka ga maza,
Y/Amshi : Sardauna uban Akka Ado Sarkin Fada,
Jagora : Mamman Bello,
Y/Amshi : Uban AKka Ado Sarkin Fada,
: Minista na
Ciniki,
: Allah ya isam ma
Bello Maitama Yusuf.
Jagora : Da nid dade ban ga Bello ba,
: Sai nid dauko
motata,
: Niz zo Kano
Y/Amshi : Wurin nemansa,
Jagora :
A
niz zo Kano,
Y/Amshi : Wurin nemansa,
Jagora : Sai Sarkin Gida yac ce min ai
Sardauna,
Y/Amshi : Ba ya nan ya tashi,
Jagora : Ai Sardauna ba ya,
Y/Amshi : Nan ya tashi,
: Minista na Ciniki,
: Allah ya isam ma Bello Maitama Yusuf.
Jagora : Muhammadu ya shiga jirgin
Lagos,
: Ko ko ya shiga jirgin yawo,
: ko ko ya shiga
jirgi Lagos
Y/Amshi : Ko ko ya shiga jirgin yawo,
Jagora: : Da nij je Lagos Dankwairo,
: Na tambayi Shehu
Shagari,
: Yac ce manı wa
kake nema,
: Nac ce Sardauna Muhaamdu Bello,
: Yac ce Alhaji Dankwairo,
: Ka ga dubu biyar ka koma,
: Sardauna ya zo ya kwana,
Y/Amshi : Amma ba shi gida ya zarce,
Jagora : Amma ba shi,
Y/Amshi : Gida ya zarce,
: Minista na ciniki
: Allah ya isam ma Bello Maitama Yusuf.
Jagora : Yaje Amirka da London,
: Dac can zai wuce Birnin Makka,
: Domin ya yo ziyara,
: Sai nit ta rokon Allah, Allah,
Y/Amshi : Kawo Bello gida laliya,
Jagora : Mamman,
Y/Amshi : Allah kawo ka gida lafiya,
Jagora : Shugaban bikin Filanin Yola,
‘Yan/Amshi : Had da Barebari
sun san shi,
Jagora : Muhammadu
Y/Amshi : Had da Barebari sun san shi,
: Minista na ciniki
: Allah ya isam ma
Bello Maitama Yusuf.
Jagora
:Kaji
irin kidin,
Y/Amshi : Kidin da kan fi karifin yaro,
: Minista na
Ciniki,
: Allah ya isam ma
Bello Maitama Yusuf.
Jagora : Kun ji irin kidin da kan fi karfin
yaro,
Y/Amshi : Karfin yaro,
Jagora : in dai kaj ji tambura,
: Kotsanni suna
kara,
Y/Amshi : To wanga nan kidi,
: Na dan Sarki ne,
: To wanga nan
kidi,
: Na Dankwairo ne,
Jagora : Duk in da kaj ji tambura na kara,
: Sannan kidi na
Kotso ne,
Y/Amshi : To wanga nan kidi na Dankwairo
ne,
Jagora : Ta tabbata,
Y/Amshi : Wanga nan kidi na Dankwairo ne,
: Minista na Ciniki,
: Allah ya isam ma Bello Maitama Yusuf
Jagora : Ranar karamar sallah ta
bana,
: Muhammadu ka yi hawan yaki,
: Ni ban je ba nij ji labari,
: Da kaj je can
birin Gwaram,
: ‘Yan birnin Kano
sun je,
Yan/Amshi : Gwaram wurin kallonka,
: Minista na
Ciniki,
: Allah ya isam ma
Bello Maitama Yusuf.
Jagora :
Yan
birnin Kano gaba ɗaya,
Y/Amshi : Duk Sun je Gwaram wurin
kallonka,
Jagora : Ga bindiga tana hannunka,
: Ga zagaigai suna
a gabanka,
: Baya gare ka
bayin Sarki,
: Baya gare ka
bayin Sarki,
: Ga makada nan
sun jera,
: In ji tsoffin
Kano suna faɗin,
: Kamad dai Sule
Sarkin Yaki,
: Irin Hausan,
Y/Amshi : Kamad dai Sule Sarkin Yaki,
: Minista na Ciniki,
: Allah ya isam ma Bello Maitama Yusuf.
Jagora : Yadda ka ba ni mamaki,
: Muhammadu da kat
taho Kan0,
: Ka shiga mota za
ka Argungu,
: Tun da kaf fito
Kano,
: Da kaj je cikin
garin Gwarzo,
: Duka sun zo
wurin taron dattijo,
Y/Amshi : Sun zo wurin taron dattijo,
: Minista na
Ciniki,
: Allah ya isam ma
Bello Maitama Yusuf.
Jagora : Yad
da kaf fito gidanka lafiya,
: Ka dawo gidanka
lafiya,
: Da yaj je can
birnin Dayi,
: Duk sun je wurin taron dattijo,
: Yadda kaf fito
gidanka lafiya,
Y/Amshi : Allah mai she ka gida lafiya,
Jagora : Da kaj je gidanka laliya,
: Yadda kaj je
gidanka laiiya,
: Ka dawo gidan,
: Minista na
Ciniki,
: Allah ya isam ma
Bello Maitama Yusut.
Jagora : Da yaj je cikin garin Funtuwa,
: Duk sun fito
taron dattijo,
Y/Amshi : Yadda kat ito gidanka lafiya,
: Ka dawo gidanka
lafiya,
: Minista na
Ciniki,
: Allah ya isam ma
Bello Maitama Yusufu.
RATAYE
NA 6
Makadi : Alhaji Musa Ɗankwairo Maradun
Wakar : Alhaji Ado Ɗandawaki
G/Waka : Na Alhaji Abba Mijin Maza,
: Na Yadda da Ado
Ɗandawaki.
Jagora : Na yadda da Ado Ɗandawaki,
Y/Amshi : Na Alhaji Abba Mijin Maza,
Jagora : Mai yabo gun Allah,
‘Y/Amshi : Na Alhaji Musa Da'u ka huce hushi,
: Na Alhaji Abba
Mijin Maza,
: Na Yadda da Ado
Ɗandawaki.
Jagora : Ado mahassadanka sun yi ga
banza,
Y/Amshi : Don na ce masu sun yi ƙarya,
: Na Alhaji Abba
Mijin Maza,
: Na Yadda da Ado
Dandawaki.
Jagora : Allah,
Y/Amshi : Don na ce musu sun yi karya,
: Na Alhaji Abba
Mijin Maza,
: Na Yadda da Ado
Dandawaki.
Jagora : Kai ne mulki kai ne ilmi,
: Ba a hi ka
taimako ba Ado, x
Y/Amshi : Alhaji Ado ka yi komi, x
: Na Alhaji Abba
Mijin Maza,
: Na Yadda da Ado
Dandawaki.
Jagora : Dan dattijo,
Y/Amshı : Ni Alhaji Ado ka yi komi,
Jagora : Taimąki gazajje,
: Taimaki maraya,
Y/Amshi : Alhaji Ado Ɗandawaki,
: Na Alhaji Abba
Mijin Maza,
: Na Yadda da Ado
Ɗandawaki.
Jagora : Ya bai wa gazajje,
: Ya bai wa maraya,
Y/Amshi : Alhaji Ado Dandawaki,
Jagora : Ka ba kuturu,
: Ka ba makaho,
Y/Amshi : Alhaji Ado Ɗandawaki,
: Na Yadda da Ado
Ɗandawaki.
Jagora : Dattijo,
Y/Amshi : Alhaji Ado Ɗandawaki
: Na Alhaji Abba
Mijin Maza,
: Na Yadda da Ado
Ɗandawaki.
Jagora : Can Sakkwato garin Shehu,
: Suna da Ado zad
dama,
Y/Amshi : Ba su da Ado Dandawaki,
Jagora : Can da nij je Jihar Neja,
: Suna da Ado zad
dama,
Y/Amshi : Ba su da Ado Dandawaki,
Jagora : Na zo Jihar Kaduna,
: Suna da Ado zad
dama,
Y/Amshi : Ba su da Ado 1Dandawaki,
Jagora : Sai nil leka Jihar Benuwai,
: Suna da Ado zad
dama,
Y/Amshi : Ba su da Ado Dandawaki,
: Na Alhaji Abba
Mijin Maza,
: Na Yadda da Ado
Dandawaki
Jagora : Sai nit tali Jihar Kwara,
Y/Amshi : Suna da Ado zad dama,
: Ba su da Ado Dandawaki,
Jagora : Jihar Plateau na duba,
: Suna da Ado zad
dama,
Y/Amshi : Ba su da Ado Dandawaki,
Jagora : Jihar Bauchi na duba,
: Suna da Ado zad
dama,
Y/Amshi : Ba su da Ado Dandawaki,
Jagora : Jihar Gongola nid duba,
: Suna da ado zad
dama,
Y/Amshi : Ba su da Ado Dandawaki,
Jagora : Kar Nijeriyag ga na duba,
: Kowace Jiha na je,
: Suna da Ado zad dama,
Y/Amshi : Ba su da Ado Dandawaki,
Jagora : Sai da nit taho Jihar Kano,
: Kano akwai dubun komai,
Y/Amshi : Nan anka yi Ado Dandawaki,
Jagora : Da Allah yay yi Annabi Adamu,
: Allah yay yi Ado
Bayero,
Y/Amshi Yay yi Ado Dandawaki,
Jagora :
Sai
Haliku,
Y/Amshi : Yay yi Ado Dandawaki,
: Na Alhaji Abba
Mijin Maza,
: Na Yadda da Ado
Dandawaki.
Jagora : Wani kyandir dai hitilab banza,
: Ko da ba lhitila
gidana,
: Ka san ba ni
sayen kyandir,
: Sai in sai
hitila in kunna,
: Sharrin kyandir
in ka saya,
: In ka kwanta ka
yi bacci,
: In dai kyandir
yaf fadi,
Y/Amshi : Yanzu ya kone ma gida,
: Na Yadda da Ado
Dandawaki,
Jagora : Yanzu ya jawo gobara gida,
: Mijin Hajiya Ni'ima,
YAmshi : Alhaji Ado Dandawaki,
Jagora : Mijin Hajiya Ni'ima,
Y/Amshi : Alhaji Ado Dandawaki,
Jagora : Mijin Alhajiya Jabba,
Y/Amshi : Alhaji Ado Dandawaki,
Jagora : Mijin
Alhajiya Jabba,
Y/Amshi : Alhaji Ado Dandawaki,
: Na Alhaji Abba
mijin maza,
: Na yadda da Ado
Dandawaki.
RATAYE NA 7
Makadi : Alhaji Musa Ɗankwairo Maradun
Wakar :
Jam'iyyar
siyasa ta N.P.N
G/Waka : Jam iyyar N.P.N,
: Aminci dai N.P.N.
Jagora : Ku ya da karya.
Y/Amshi : Ku kamma gaskiya,
Y/Amshi : Ku kamma gaskiya,
Jagora : Ku ya da karya,
Y/Amshi : Ku kamma gaskiya,
: Kar ku sake don Allah,
: Mutane kar ku sake don Allah,
: Jam iyyar N.P.N,
: Aminci dai N.P.N.
Jagora : Ki yini lafiya,
: Ki kwana lafiya,
Y/Amshi : Ki tashi lafiya N.P.N.
Jagora :
Kowash shiga,
Y/Amshi : Ya sha dadi,
: Daki da masara N.P.N.,
Jagora : Kui ta tunani,
: kui ta hankali,
: kai dun,
Y/Amshi : Mutumin N.P.N.,
: Bai zan mutumin banza ba,
Jagora : Wannan,
Y/Amshi : Bai ya da hwadin karya ba.
: Jam iyyar N.P.N,
: Aminci dai N.P.N.
Jagora : Ko ni makadin N.P.N,
Y/Amshi : Ban san sukak kowa ba,
Jagora : Sannan ban san,
Y/Amshi : Zagin kowa ba,
Jagora : Sai dai wanda yab bace hanya,
: Dankwairo in
mashi roko,
Y/Amshi : Ya Allah mai so shi,
: Shi taho ya bi
babbar hanya.
Jagora : To kun ji tamburan N.P.N,
Y/Amshi : Haji Dankvairo ya shirya,
Jagora : Ita Jamiyag ga ta N.P. N.,
: Duk inda taj je kafa reshe,
Y/Amshi : Ko da birmi ko da daji,
: Magana ta gaskiya take fadi
: Ba ta ya da fadin karya ba,
Jagora : Ita hay yau,
Y/Amshi : Ba ta ya da fadin karya ba,
Jagora : Kabiru Direba na gode,
Y/Amshi : Domin dai ban ram mai ba,
: Domin darajar N.P.N,
Jagora :Ya ban,
Y/Amshi : Domin darajar N.P.N.,
Jagora : Sarkin Gwaram Muhammadu
Sani,
Y/Amshi : Ya ban domin darajar N.P.N.
: Jam iyyar N.P.N.
: Aminci dai N.P.N.
Jagora : Alhaji,
‘Y/Amshi : Sarkin Gwaram Muhammadu
Sani,
: Ya ban don darajar N.P.N.,
Jagora : Na
gode ya ban,
Y/Amshi : Don darajar N.P.N.,
Jagora : Kabiru,
Y/Amshi : Dircba na gode maka,
: Ya ban don darajar N.P.N.
Jagora : Na gode wa Damburan na
Katagun,
Y/Amshi : Ya ban don darajar N.P.N.,
Jagora : Haji Babani ya ban,
Y/Amshi : Don darajar N.P.N.,
Jagora : Dan Waziri,
Y/Amshi : Jikan Waziri uban Batulu,
Jagora : Ban ram mai ba,
: Dan Waziri baban Waziri,
Y/Amshi
Jikan
Waziri baban Batulu,
: Ban ram mai ba,
'Y/Amshi
: Jikan Waziri
baban Batulu,
Jagora : Ban ram mai ba.
: Jam iyyar N.P.N,
: Aminci dai N.P.N.
Jagora : Ita Jam iyag ga ta N.P.N.,
: Duk inda taj je Kala reshe,
: Ko da birni,
Y/Amshi : Ko da daj
: Magana ta gaskiya taka ladi,
: Ba ta ya da fadin,
Jagora : ita hay yau,
Y/Amshi : Ba ta ya da fadin karya ba,
Jagora : Ya ba ni Naira dari gaba dai,
Y/Amshi : Ya ni Damburan,
: Domin darajar N.P.N.,
Jagora : Na gode ma Shugaban N.P.N.,
Y/Amshi : Allah ya rika ma,
Jagora : Lawali
‘Y/Amshi : Allah ya
rikama
: Jam’iyyar N.P.N
: Aminci dai N.P.N.
Jagora : Dan Buran,
Y/Amshi : Babani Allah ya rika,
Jagora : Ku mutane yan Nijeriya,
: Dankwairo na horon ku,
: Kak Ku sai da mutuncinku,
: Kak ku sai da mutuncin,
Y/Amshi :’Ya’yanku, ku yi hankali don
Allah,
Jagora : Na ce ku,
Y/Amshi : Mutane "yan Njeriya,
: Dankwairo nai maku horo,
: Kak ku sal da mutuncinku,
: Kak ku Sai da mutuncin ‘ya’yanku,
: Ku yi hankali,
Jagora : Na ce,
Y/Amshi : Ku yi hankalı don Allah,
Jagora : Kowa na son ya rika gaskiya,
‘Y/Amshi : Komi yac ce zai yi da kai,
: To ban ce mai a a.
Jagora : Shi President mu na N.P.N.,
: Alhaji Shehu Shagari,
: Yaro ne ba tsoho ba ne,
: Ga shi da arziki da ilmi,
Y/Amshi : Sannan da sanin dattako,
: One Nation One
Destinty,
: Kasa daya ce a
gu daya,
: Nigerian
National Party,
: Akwai farin jini gare ta,
: Jam'iyyar N.P.N,
: Aminci dai N.P.N.
Jagora : Ba Nijeriya kadai ba,
: Kai duk Afurka
baki daya,
: Sunai mana latan alheri,
: Wajen jama'an N.P.N.,
: Jam iyyar N.P.N,
: Aminci dai N.P.N.
Jagora : Amma,
Y/Amshi : Wajjan jama'an N.P.N.,
Jagora : Ni Alhaji Musa Dankwairo,
: Da ni da magoyd,
Y/Amshi : Bayana duka muna cikin N.P.N.,
Jagora : Siyasa ba gaba ba ta,
: Kai ku ji domin siyasa,
Y/Amshi : Ku dubi haramun danbil’amu,
:Wai shi ka gamin mai waka,
Jagora : Ka je ka bayyana halina,
Y/Amshi : In dora fadin halinka,
Jagora : Ni kau,
Y/Amshi : In dora fadin halinka,
: Ka dora fadin ina waka,
: In dora fadin
kai sata.
: Jam'iyyar N.P.N,
: Aminci dai
N.P.N.
Jagora : Shi kalwani ba dan goyo ba ne,
Y/Amshi : Kwag goye ka kana yasshe shi,
Jagora : Alhaji Adamu Mohamnmed,
: Ya ban,
Y/Amshi : Don darajar N.P.N.,
Jagora : Kayan da amale yad dauka,
: In yat tafi yak
kai zang0,
: In dai an aza wa
jakı,
Y/Amshi : Ba zai iya dagawa,
Jagora :
Ka san,
Y/Amshi : Ba zai iya dagawa nan ba,
Jagora : Da kare da biri,
Y/Amshi : Da bakar mussa,
: Barnar da kukai an gane,
Jagora : Tun da,
'Y/Amshi : Duniya tag gane,
: Gobe ba biya sai duka
: Jam'iyyar N.P.N,
: Aminci dai N.P.N.
Jagora : Ai ga giwa tai ruri,
Y/Amshi : Sai zaki yab boye,
Jagora : Kuma ga zaki ya yi babbaki,
Y/Amshi : Sai kura tab boye,
Jagora : Kuma ga kura ta nisa,
Y/Amshi : Awaki
duk sun boye,
: Tumaki duk sun
ruga,
Jagora : Jihar Sakkwato na leka,
Y/Amshi : Masu hankali masu ilmi,
: Duka suna cikin
NP.N.,
Jagora : Jahar Kaduna da nit leka,
Y/Amshi : Masu hankali masu ilmi,
: Duka suna cikin
N.P.N.,
Jagora : Jihar Kano da nid diba,
Y/Amshi : Masu hankali masu ilmi,
: Duka suna cikin
N.P.N.,
Jagora : Jihar Bauchi da nid dira,
Y/Amshi : Masu hankali masu ilmi,
: Duka suna cikin
N.P.N.,
Jagora : Jihar Gongola da ail Ieka,
Y/Amshi : Maşu hankali masu ilmi,
: Duka suna cikin
N.P.N.
: Jam iyyar N.P.N,
: Aminci dai N.P.N,
RATAYE NA 8
Makadi : Alhaji Musa Ɗankwairo Maradun
Waƙar : Alhaji Shehu Shagari, Tsohon
Shugaban Kasa,
: Turakin Sakkwato
G/Waƙa : Shugaban Kasa jikan Sule,
: Wada duk aka so
ya kai.
Jagora : Shugaba mai cikakken iko,
Y/Amshi : Shugaba mai cikkaken iko,
Jagora : Shugaba mai cikakken iko,
Y/Amshi :Wada duk aka so
ka kai,
: Shugaban Kasa
jikan Sule.
Jagora : Dadin da ny Jiya Haji Dankwairo,
: Tutaru wadda a
kasar Makka,
: Da Alhaji Musa
kwance take,
: An tasshe ta ta koma tsaye,
Y/Amshi : A wajcn fuskar Musulunci,
: Yau Nijeriya ita ta daya,
Jagora : Ranad dai ga watan goma,
: Cikin wata
Oktoba,
: Cikin 1979,
: Rad da Shehu yaz
zamo,
: Shugaban kasa
mai cikakken iko,
: Duk Afurka ga
baki daya,
: Duk inda
Shugaban kasa yake,
: Wasu sun aiko da
takardu,
: Wasu sun turo
wakilansu,
: Wasu sun yo
wayat tangaraho,
: Wasu sun aiko da
takardu,
: Wasu sun shigo
cikin Nijeriya,
Y/Amshi : Su yi ma murnar samun girma,
Jagora : Sun zo,
Y/Amshi : Su yi ma murnar samun girma,
Jagora : Hadarin kasa maganin mai
kabido,
: Yaki mai yada
gidan gona,
: Kauce yaro kauce
giwa,
‘Y/Amshi : In ka kiya tana tattaka ka,
: Shugaban Kasa
Jikan Sule,
:
Wada duk aka so ya ka
Jagora : Sarkin Musulmi na murna,
: Na Sardauna ka
goge makiyansa,
Y/Amshi : Sun taru Ssun koma baya,
: Shugaban Kasa
Jikan Sule,
: Wada duk aka so
ka kai.
Jagora : Yawo yana kara ilim,
: Yawo yana kara
hankali,
: Yawo yana kara
tunani,
:To ko ban yi
karatu ba,
: Na ji dadin nau
yawo,
: Amma ga Wani yat
yawon banza,
Y/Amshi : Bai yiy haske ba Kara duhu yay yi,
: Shugaban kasa
jikan Salc,
: Wanda duk aka so
Ka Kai.
Jagora : Adamu AIiyu ban raina mai ba,
: Na yi godiya dan
AIkali, x*
: Alhaji Danburan
Na Katagun,
Y/Amshi : Jikan Waziri ban rena mai ba,
Jagora : Dan Waziri,
Y/Amshi : Ban rena mai ba,
Jagora : Dan Muhammadu jikan Mamman,
: Sarkin Gwaram,
Y/Amshi : Waziri ban rena mai ba,
Jagora : Sarkin Gwaram,
Y/Amshi : Waziri ban rena mai ba,
Jagora Sarkin Gwaram,
Y/Amshi : Ban rena mai ba,
Jagora Alhaji Baba Umar,
Y/Amshi : Ya Rabbana ya kara wadata ka,
x2
Jagora : Ummaru jikan Mamman,
Y/Amshi : Ya Rabbana ya kara wadata ka,
Jagora : Na zo ka ba ni mota,
Y/Amshi : Albarkacin girman mai girma,
Jagora : Na zo ka ba ni mota ta hawa,
Y/Amshi : Darajar girman mai girma,
Shugaban Kasa
jikan Sule,
Wada duk aka so ya
kai.
Jagora :Abin da nis sani,
:Ni nawa sani,
:Yawo yana kara ilmi,
:Yawo yana kara hankali,
:Yawo yana kara tunani,
Y/Amshi : :Kai ko ban yi karatu ba, x2
Jagora : :Na ji dadin nai yawo,
Y/Amshi : :Amma ga wani yay yawon banza,
Jagora : Shi
bai y1 haske ba,
YIAmshi : : Kara
duhu yay yi,
Jagora :Ni ai wuya ta da duniya,
:Ga wani don
tsananin mulki,
: In yak kwanta
sai an tassal,
:1o mulkin nashi
ya kare,
Y/Amshi : Yayi kwance ya rasa mai tassai,
Jagora
Y/Amshi: :Yayi kwance,
:Yanzu,
:A
riasa mai tassa1,
:Agora Ko kuwakka tai kyawu zaki,
:kuwakka tai ky
:Kada maza dal 2aki,
:ga wani na ei adi,
Jagora: :Sai
yana tadin ban yarda ba,
YAmshi : Sai a sake sabuwar kokuwa,
Jagora: :Shi ba kab bs wa,
Y/Amshi : : Ya
Rabbana ya kara wadata ka,
:Bai
bakinai,
Jagora :Shugaba mai cikakken iko,
Jagora : :Uban Bala uban dan na Hude,
YAmshi : :Alhaji Shehu giwa sha masu,
Jagora :Alhamdu Lillahi sai Hamdala,
:Nasara tare da adalci aminci,
:Sun Koma wguda,
Y/Amshi : : Shehu Shagari ka sa su
aljihu
,
Jagora :Maganar tsari na Nijeriya,
:Abin da kal fadi
tilas aka dauka,
Y/Amshi : :Yanzu ina wani ba kai ba,
Jagora :Shehu Aliyu,
Y/Amshi :Ina wani ba kai ba,
Jagora :Duka Shugaban da anka yi Nijeriya,
:In bayan Prime Minister Tafawa,
:Sai Shugaban "Northern Nigeria,
:Ahmadu Bello Sardauna Sakkwato,
:Ba wani shugaba mai cikakken Iko,
Y/Amshi : : Sai
kai Alhaji Shehu amintacce,
Jagora" :Field Marshal namu na Nijeriya,
:Shi ne shugaban "National Party,
:Bawan Allah dan bawan Allan,
Y/Amshi : :Jikan bawan Allah ne shi,
:Shugaban Kasa jikan Sule,
:Wada duk aka so ya kai.
Jagora: :Shehu,
Y/Amshi :Jikan bawan Allah ne shi,
:Jagora Gaskiya kak ku hada ta da karya,
:Kowas samu tuwan masara,
:Idan dai yac ci ya Koshi,
Y/Amshi : :To kun san bai cin kwakwa danya, x
Jagora :Sar am sami gida na shiga,
:ldan dai an shiga
an gine,
:Sannan za a nemi makulli,
:Idan dai babu
gida na shiga,
Y/Amshi : : Makullin ka ya zan,
Jagora : Kai kan Malam,
Y/Amshi : :Makullinka
ya zan kam banz4,
:Shugaban Kasa jikan Sule,
:Wada duk aka so ya kai.
Jagora : Ga zaki nan,
Y/Amshi : : Yai tsaye gun mashigi,
Jagora: : Wani wawa ya gitta mai,
Y/Amshi : : Shi kau zaki yat tattaka shi,
:Jagora Na ci dariya
Dankwairo,
:Wasu sun yi butulcCi gun Allah,
Y/Amshi :Murnarsu ta koma kuka,
Jagora : :Sabgar kwarai,
Y/Amshi : :Ad da dadi, x2
Jagora : :Ai gwanin tainyar kura,
Y/Amshi : :Yana gaba ya koma baya,
:Shugaban Kasa jikan Sule,
:Wada duk aka so ya kai.
Jagora : :Haji Baba Umar,
Y/Amshi : :Ya Rabbana ya kara wadata ka,
:Shugaban Kasa
jikan Sule,
:Wada duk aka so
ya kai.
Jagora : :Na zo ka ba ni
mota,
: Dalilin Gwamna Tatari Al,
Y/Amshi : :Dalilin
girman mai girma,
Jagora : : Na zo ka ba ni mota,
:Darajar Tatari Ali,
Y/Amshi : Darajar
girman mai girma,
Jagora : :Darajar,
Y/Amshi : :Girman mai girma,
:Shugaban Kasa jikan Sule
:Wada duk aka so ya kai.
Jagora : :Sai ya ba ka mota,
:Sai ka ba ni mota 504,
:Station Wagon,
Y/Amshi : :Duk in shige,
:Ina ta bugun tur,
Jagora : :Kuma ka ba ni mai
tanhwal,
Y/Amshi : Ta dauki kaya,
:Ta dau 'yan yarana,
:Shugaban Kasa jikan Sule,
:Wada duk aka so ya kai.
Jagora : : Dattijo dan dattijo,
:Ran da yah hau mulkin Nijeriya,
:Ya taho Jihar Sakkwato,
Y/Amshi : :Domin ya duba
mutanenai,
:Sannan ya gai da
masoyanai,
:Jagora Ya tati Jihar
Kaduna,
Y/Amshi: :Domin ya duba
mutanenai,
:Sannan ya gai da masoyanai,
Jagora :Ya tafi Jihar Kano,
Y/Amshi : :Domin ya duba
mutanenal,
:Sannan ya gai da masoy anai,
Jagora :Ya tafi Jihar Kano,
Y/Amshi : :Can domin ya duba
mutanenal,
:Sannan ya gai da masoyanai,
Jagora :Ya tafi Jihar Bauchi,
Y/Amshi : :Can domin ya duba
mutanenal,
:Sannan ya gai da masoyanal,
Jagora :Ya tafi Jihar Borno,
Y/Amshi: :Can domin ya duba
mutanenal,
:Sannan ya gai da masoyanai,
Jagora :Ya tali Jihar Gongola,
Y/Amshi : :Can domin ya duba mutanenal,
:Sannan ya gai da masoyanai,
Jagora: :Ya tali Jihar Benuwe,
Y/Amshi : :Can domin ya duba
mutanenai,
:Sannan ya gai da
masoyanal,
Jagora :Ya tali
Jihar Rivers,
Y/Amshi : :Can domin ya duba
mutanenai,
:Sannan ya gai da masoyanai,
:Shugaban Kasa
jikan Sule
:Wada duk aka so
ya kai.
Jagora :Ya tafi Jihar Bendel,
Y/Amshi :Can domin ya duba
mutanenai,
:annan ya gal da masoyana,
:Shugaban Kasa Jikan Sule,
:Wada duk aka so ya kai.
Jagora: :Jihar Imo ya zo ya duba,
Y/Amshi : :Domin ya duba mutanenai,
:Sannan ya gai da
masoyanai,
Jagora Ya tafi Jihar lmo,
Y/Amshi: :Can domin ya duba
mutanenai,
:Sannan ya gai da
masoyanai,
Jagora : Jihar Ogun ya zo ya
duba,
Y/Amshi : :Domin ya duba
mutanenal,
:Sannan ya gai da nasoyanal,
Jagora: :Jihar Ondo ya zo ya leka,
:mutanenai.
YAmshi :Domin ya duba
mutanenai,
:yanai,
Jagora :Jaay y ya icha,
Y/Amshi :Domin ya duba
mutanenai,
:Sannan ya gai da ma
:Sannan ya gar da
masoyanai,
Jagora :Ya tati Jihar Lagos,
Y/Amshi : :Can domn ya duba
mutanenai,
:Sannan ya gal da masoyanai,
:JagoraYa tali Jahar Kwara,
Y/Amshi : :Can domin ya duba
mutanenai,
:Sannan ya gai da
masoyanai,
Jagora :Ya tati Jihar
Lagos,
Y/Amshi: :Can domin ya duba
mutanenai,
:Sannan ya gai da masoyana,
Jagora :Ya tali Jihar Bendei,
Y/Amshi : :Can domin ya duba
mutanenai,
:Sannan ya gai da masoyanai,
Jagora :Jihar mo ya zo ya
duba,
Y/Amshi : :Domin ya duba mutanenai,
:Sannan ya gat da nasoyanai,
Jagora :Ya
tafi Jihar Imo yanai,
Y/Amshi : :Can domin ya duba
mutanenai,
: Sannan ya gar da masoyanai,
Jagora :Jinar Ogun ya zo ya
duba,
Y/Amshi: :Domin ya duba mutanenai,
:Sannan ya gai da
masoyanai,
:Shugaban Kasa jikan Sule,
:Wada duk aka so ya kai.
Jagora :Jihar Ondo ya z0 ya leka,
Y/Amshi :Can domin ya duba mutanenai,
:Sannan ya gai da masoyanai,
Jagora: :Jihar Oyo ya zo ya
duba,
Y/Amshi : :Domin ya duba
mutanena,
:Sannan ya gai da
masoyanai,
:Shugaban Kasa jikan Sule,
:Wada duk aka so
ya kai.
Jagora: :Ya tafi Jihar Lagos,
Y/Amshi : :Can domin ya duba
mutanenal,
:Sannan ya gai da masoyanal,
Jagora :Ya tafi Jihar Kwara,
Y/Amshi: :Can domin ya duba
mutanenai,
:Sannan ya gai da masoyanai,
Jagora :Ya tafi Jihar Lagos,
Y/Amshi : :Can domin ya duba
mutanenai,,
:Sannan ya gai da
masoyanai,
Jagora : :Nijeriyag ga ta zama
taka,
:Kai ko Shehu ka
zama nasu,
Y/Amshi : :Kowa ba ya gudun
Shenu,
:Kuma Shehu ba ya
gudun Kowa,
:Kowa ba ya gudun shehu,
:Kuma Shehu ba ya gudun kowa,
Jagora : Dan Aliyu ban,
Y/Amshi :Rena mai ba,
Jagora :Adamu Aliyu,
Y/Amshi : :Ban rena mai ba,
Jagora: :Ina ta godiya dan Alkali,
: Muna ta godiya,
Y/Amshi :Dan Alkali,
:Shugaban Kasa
jikan Sule,
:Wada duk aka so
ya kai.
Jagora : :Babban Manajan Airport,
:Muhammadu Yola na
Hadeja,
Y/Amshi : :Ya Rabban ya kara wadata ka,
Jagora :Babban Manajan Airport,
:Muhammadu Yola Hadeja,
:Dan Malam Muhammadu,
Y/Amshi: :Ya Rabbana ya kara,
Jagora :Mijin Uwani,
YIAmshi: :Ya Rabbana ya kara,
Jagora: :Mijin Uwani,
Y/Amshi: :Ya Rabbana ya kara,
Jagora: :Baban A'i,
Y/Amshi: :Ya Rabbana ya kara
wadata ka,
:Shugaban kasa Jikan Sule,
:Wada duk aka so ka kai.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.