Ticker

6/recent/ticker-posts

Mijina Yana Kiran Aurenmu Da Auren Ƙaddara, Kuma Ba Ya Salloli Biyar Na Farilla, Ya Hukuncin Zaman Aure Da Shi?

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu Alaikum, Malam dan Allah ya hukuncin auren da miji yake kira da Auren kaddara? Kuma ya halasta mace ta ci gaba da zama da mijin al'halin bai kiyaye hamsu salawat?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa'alaikumus Salam, baiwar Allah don miji ya kira aurensa da matarsa a matsayin auren ƙaddara wannan bai ɓata auren ba, sai dai kawai wata ƙila yana yi ne don ya ɓata wa matar rai, kuma kuskure ne mutum ya aikata wani aiki don ya ba wani Musulmi haushi ba tare da cancantar yin hakan ba, amma hakan bai ɓata aure ba a magana ta gaskiya.

A dangane da zaman aure da mijin da ba ya yin salloli biyar na kowace rana kuwa, to da farko dai matar ya wajaba ta yi masa nasiha a kan hakan, ta kuma nuna masa ƙin yin sallah kaɗai yana iya mayar da mutum kafiri, idan an yi an yi da shi ya gyara, kuma an kai shi ƙara wajen duk waɗanda ake ganin zai ji maganarsu amma ya ƙi gyarawa, to daga nan sai ta kai shi ƙara wurin hukuma ta raba wannan aure, saboda ba ya halasta mace Musulma ta yi zaman aure da kafiri, duk da wasu malaman suna da fahimtar wanda ba ya sallah, kuma bai yi inkarin wajabcinta ba, bai kafirta ba, amma fahimtar da ta fi dacewa da ayoyin Alƙur'ani da Hadisan Manzon Allah , da kuma fahimtar Sahabbai ita ce duk wanda kwata-kwata ba ya sallah to ya kafirta, saboda faɗin Annabi cewa:

"Alƙawarin da ke tsakaninmu da su (kafirai) shi ne sallah, duk wanda ya bar ta ya kafirta".

Musnadul Imami Ahmad (22937), Tirmizhiy (2621), Ibn Majah (1079).

Domin meman ƙarin bayani duba Majmu'u Fatáwá na Ibn Uthaimeen (21/46 - 51). Ko a duba: Hukmu Tárikis-Salati shi ma na Ibn Uthaimeen. Ko a duba Hukmu Tárikis-Salati na Almuhaddis Nasirud-Deen Albániy.

Allah ne mafi sani.

Jamilu Ibrahim Sarki, Zaria.

Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin mu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/Du5LNx31U9hDi6RƘbbrzgW

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Questions and Answers

Post a Comment

0 Comments