Ticker

6/recent/ticker-posts

Auren Gargajiya A Garin Kwatarkwashi (4)

Kundin Binciken Neman Digirin Farko (B.A Hausa) Wanda Aka Gabatar A Sashen Harsuna Da Al’adu, Jami’ar Tarayya Gusau.

Auren Gargajiya A Garin Kwatarkwashi (4)

NA

NURA SANI KOTORKOSHI

 

Dakin amarya

BABI NA UKU

3.0 TAƘAITACCEN TARIHIN MASARAUTAR KWATARWKASHI

Kwatkwarshi gari ne mai daɗaɗɗen tarihin asali da jaruntaka. An samu kafuwar kwatarkwashi a cikin ƙarni na goma sha huɗu (14) kimanin shekara ɗari shida da goma sha ɗaya (611) da suka wuce (1,400 zuwa yau), sunan Kwatarkwashi dutse da ganuwa inda maiki ya shahara, saboda yawan duwatsun da Allah ya albarkaci wurin da su. Garin Kwatarkwashi ya yi iyaka ne da masarautar Mada daga gabas. A kudu maso gabas kuma garin ya yi iyaka ne da masarautar Tsafe. Ta arewa kuwa garin ya yi iyaka da masarautar Kaura Namoda. Har wayau garin ya yi iyaka da Gusau babban birnin jahar Zamfara daga yamma.

 

Kasancewar garin na kewaye da duwatsu masu ƙawatarwa, wanda ya ba garin martaba da tsaro, haka kuma baƙi masu yawon shaƙatawa sukan ziyarci garin domin ganarwa idanunsu abubuwan sha’awa da mamaki.

 

Sunan Kwatarkwashi ya samo asali ne daga wanda ya kafa Kwatarkwashi tun farko mai suna (Mangul). Shi wannan bawan Allah ya yi ƙaura ne daga Katsina a bisa ga sana’arsu ta harbi, lokacin sarkin Katsina kumiyo, da sunan Mangul ya ɓata sanadiyar kyautatawa da alherin da yakan kai wa Sarkin Katsina a cikin wani baho da ake kira Kwatashi. Bisa haka ne, Sarkin Kwatarkwashi ya canza daga Kwatashi zuwa Kwatarkwashi.

A cikin sana’arsu ta harbi, sun fara zama ne ƙarƙashin dutsin da ake cema kundun, cikin ƙasar Katsina, wanda suka zauna har tsawon shekara huɗu daga nan suka yi hijira zuwa Dungal ‘Dungal’ na nan gabas da Kwatarkwashi cikin yankin Gulubba ta yanzu), sun yi zama na shekara uku daga nan sai suka isa wani wuri da ake kira dukura (Dutsi mai daɗaɗɗen tarihi wurin da Kwatarkwashi take a yanzu.

 

Kamar yadda tarihi ya nuna zamansu a Dungai ya jawo jama’a suka yi ta karuwa har ya zamanto wurin ya zama gari. A nan ne, jama’ar suka ga yadace su naɗa shugaba a cikinsu. Duk da suke Maharba ne, an nuna Mungul (Kwatashi) yana sana’ar Koli, sanin da aka yi mashi mai son zama lafiya ne da haba-haba da mutane da jaruntaka, sai suka zaɓeshi ya zama shugabansu (Kuma Sarki).

 

Bayan sun cimma matsaya ta ƙashin kansu a kan zaɓen Mangul a matsayin Sarki sai suka yi tawaga zuwa Katsina domin gabatar da shi ga Sarkin Katsina Kumayo tare da kyauta ta Kwatashi (Kwatashi wani abu ne da mata ke sa kaya a ciki). Nan take Sarkin Katsina yaba Mangul Sarkin Kwatashi a Sanadiyar wannan Kwatashi da aka zo mashi da shi.

 

Tun da aka kafa Kwatarkwashi ba a taɓa cinta da yaƙi ba, saboda Jaruntakar al’ummar mu da kuma kyakykyawan jagoranci da suka samu na shugabanni. Duk da yawan kawo hari da Namoda da Banaga ɗan Bature na Morai suka kawo mata. Hasali ma dai lokacin mulkin mallaka, Kwatarkwashi ta yi fice sosai inda har aka kai ga anajin tsoron auka mata ta hanyar hari, tsangwama ko kwace, cikin wannan hari ne a cikin watan Juli na (1903) aka yi arangama da wasu sojojin Turawan Mulkin Mallaka ƙarƙashin (Captain Wallale Wright) inda suka sha kashi har daga baya aka ci Kwatarkwashi tarar hwan talatin da biyar (35), a wannan faɗa da nasara da Kwatarkwashi ta yi. Bayan rasuwar Kwatashi a shekara ta (1420) sai Gazara ya zamo Sarkin Kwatarkwashi, wanda ya yi har na tsawon shekara 37 (1430 – 1469).

 

Bayan rasuwar Kwatarkwashi Gazara (1469) sai sarautar ta koma ga Kwatarkwashi Mayaƙi (Gemen Dodo), inda ya yi shekara talatin dai-dai yana sarauta (1470 – 1500). Kwatarkwashi Mayaƙi ya samu wata matsala wadda tasa yabar Sarauta ya koma gida Katsina.

 

Bayan komawarsa Katsina ya taras da wani jarumi wanda ya fitini Katsina mai suna Kuyafa, wannan magana ta kaiwa Sarkin Katsina, inda ya aika aka kira mayaƙi Ɗanjaji daga bakinsa, kuma Mayaƙi ya tabbatar mashi da wannan magana. Daga nan Sarki ya bashi abin da ya nema aka fita fagen fama, Mayaƙi ya nuna jaruntakarsa inda aka fafata kuma cikin yardar Allah ya zo da kan Kuyafa. Bayan an samu nasara, Sarkin Katsina ya saka masa wato ya mayar da shi ga Sarautarshi watau Kwatashi.

A nan ne Mayaƙi ya nemi a kaishi Tsafe a matsayin Sarkin Tsafe na farko. Kuma wannan shi ne dangantakar Tsafe da Kwatarkwashi. Babban abin sha’awa a nan shi ne tunanin faɗar Sarkin Katsina ya ta’allaƙa ne akan jaruntakar mayaƙi ta kawo kan Kuyafa, da kuma tsoron karɓar Sarautar Katsina daga hannunsu. Jin haka, suka ga ya dace a mayar da shi ga sarautarshi ta Kwatarkwashi.

 

Samun nasarar da Mayaƙi ya yi a Katsina da kuma kwazon Jaruntaka daya nuna, da kuma dalilan da aka bayyana a sama, yasa mayaƙi ya dawo gida, amma kasancewar ƙanensa ke sarautar Kwatarkwashi a wancan lokaci watau Bita da ƙasari sai ya wuce gaba inda wasu duwatsu suke inda ake kira tsafe a yau. Nan ya kafa nasa jagoranci kuma shi ne ‘Yandoton Tsafe na farko, wannan shi ne dangantakar Kwatarkwashi da Tsafe. Abdulkadir (2018) Tarihin Mai Martaba Sarkin Kwatarkwashi, Alh. Ahmad Umar Mai Kwatarkwashi.

 

3.1 MA’ANAR KALMAR KWATARKWASHI

Tarihi ya nuna cewa daga cikin waɗannan mutane da aka faɗi a sama akwai wani mutum mai girman jiki baƙi, ƙaƙƙarfa wanda aka fi sani da suna “Kwatashi” to, wannan mutum kusan shi ne jagorancin wannan ayari da suka taso. Bugu da ƙari ma daga wannan sunan ne aka samu sunan da ake kiran wannan gari da shi a yanzu wato Kwatarkwashi. Dantiye (2019).

3.2 KAFUWAR GARIN KWATARKWASHI

Kamar yadda aka sani cewa kowace ƙasa, haka kuma kowane gari yana da tarihin kafuwarsa da irin ci gaban da ya samu, da irin mutanen da suka fara zama a cikinsa. Haka ma garin Kwatarkwashi na da nasa tarihin, saboda haka wannan shimfiɗa ce a kan tarihin garin Kwatarkwashi da kafuwarsa.

 

Tun daga farkon tarihin wannan gari an gano cewa mutanen da suka kafashi sun fito daga ƙasar Katsina. A cewar wasu masana babban dalilin da ya rabo da waɗannan mutane daga Katsina ya ƙunshi waɗansu muhimman abubuwa da suka haɗa da ƙabilanci da siyasa da bambancin addini da kuma rashin damuwa da ba’ayi da su a ƙasar da suka baro ba. Dantiye (2019).

 

3.3 ADDININ GARGAJIYA

Tarihin addinin waɗannan mutane ya nuna cewa babban abun da suka mayar da hankali a kan bautawa su ne waɗansu iskoki guda uku watau Magiro da Kyauka da kuma Ɗanƙunƙurutu.

 

To amma duk da haka shi wannan addinin nasu ya ƙunshi waɗansu abubuwa da suka nuna yadda ake shigarsa da kuma hanyoyin bautarsu. Da farko dai shiga wannan addini bai ƙunshi wani abu ba, illa in mutum yana son shiga sai kurum ya raƙa bin sauran mutane wato masu wannan addini zuwa wata kwama ta cikin dutsin Dukura wadda ake cewa kwamar Wuliga. Ba a bin da suke yi sai shan giya da kuma yanke-yanke kamar su kaji, awaki ko raguna musamman ma baƙaƙe don baiwa Ɗanƙunƙurutu jinni ya sha.

 

Bayan waɗannan abubuwa da waɗannan addinai suka ƙunsa, akwai kuma buki na shekara-shekara don murnar kewayowar shekara dangane da kungiyar masu bautar kowane addini na gargajiya da na faɗa a baya. Haka kuma shi wannan addini baya da wani suna da aka laƙaba masa, amma masu yinsa ana kiransu da Arna ko Maguzawan Kwatarkwashi. Dan Azumi (1992).

 

3.4 SANA’O’I

Kamar dai yadda muka sani cewa duk inda al’umma ta taru, kuma har aka ce ta samu wurin zama daram da gindinta to haƙiƙa ita wannan al’umma ba za ta ji daɗin gudanar da sha’anin rayuwarta ba, dole ne sai ta tanadi wata hanya domin neman abincinta

 

Saboda haka, babbar sana’ar mutanen wannan gari ta kasance noma ga baki ɗaya. Amma duk da haka akwai waɗansu dake yin saƙa da jima da ire-iren kasuwanci baki ɗaya. Bala Dawai Sankalawa (2019).

 

3.5 ZANEN SUNA

Zanen sunan waɗannan mutane acan da ya bambanta da yadda muka san ana yinsa a yanzu. Dalili kuwa shi ne, a yanzu ana bin ƙa’idojin da addinin musulunci ya bayar, kafin mutane su karɓi addinin musulunci, suna bautar wasu iskoki ne guda uku wato Magiro da Kyauka da kuma Ɗanƙunƙurutu.

 

Don haka suna bin ƙa’idojin zanawa ‘ya’yansu suna ne dangane da yadda suka tarar iyaye da kakanninsu suna yi game da ɗabi’o’insu na gargajiya. Kamar ga masu bautar Magiro da Kyauka zanen sunansu kusan ince duk ɗaya ne; domin su waɗannan mutane ba suna yiwa ‘ya’yansu suna ba ne bayan kwana bakwai da haihuwa, wannan ko alama ba haka bane. Ga tasu al’ada sukan tara fiye da yaro huɗu ko biyar a raɗa masu suna gaba ɗaya.

 

Amma a nan ba wai suna barin sai bayan kwana goma sha huɗu ba, sannan a raɗa sunan ba, ya danganta ne, yawan yaran da aka samu a wannan makon. Wato su waɗannan mutane ba sukan raɗawa yaro ɗaya suna ba, kome tsawon lokaci, to, lallai sai sun kai huɗu ko biyar har abin da ya wuce haka.

 

Idan kuwa za’a raɗa wannan suna akan ajiye ranar da za ayi, da lokaci ya ƙaato duk ‘yan uwansa maza da mata duk zasu haɗu ayi ta shaye-shaye na giya da kuma yanke yanken kaji da awakai.

A wannan lokaci ne bayan kakan yaron ya sha giya yayi tatil sai kurum a ji ya ce “Na sanya wa yaron da wane ya Haifa suna Kaza” shi ke nan ta zauna babu mai ikon canza masa wani suna.

Amma ga al’adar masu ɗaukar maiki su nasu ba haka ba ne. Idan ɗaya daga cikin matarsu ta haihu to kafin a raɗa suna sai an tabbatar cewa yaron baya da garwaye, wato sai an gane cewa ko wani namiji ya takata bayan mijinta. Ko kuma wata hanya ta gane haka kuwa ita ce, sai a ɗauki jinjirin a buga shi a kan dutse, idan yaron ya liƙe a kan dutsin kuwa a kwai garwaye to zai faɗo. Tun daga can wajen gwajin sai a nufo uwar yaron a gaya mata jinjirin da ta Haifa ɗan zuriyarsu ne, idan kuwa ya faɗo sai a shaida mata ba cikin zuriyarsu yake ba.

 

Daga nan ita kanta matar mai haihuwar a saketa, ta fita daga gidan. Idan an tabbatar da yaro ya zama nasu ne, sai bayan kwana goma sha huɗu, sannan a shirya gagarumin shagali da shaye-shayen giya.

 

Su masu wannan addinin yaro ne zai zanawa ɗansa suna, bayan ya sha giya ya ƙoshi, sai kurum ya ce “sunan ɗana wane”. Bayan an gama shagali sai kowa ya watse. Aminu (2008).

 

3.6 KACIYA

A zamanin da Maguzawan wannan ƙasa suna yiwa ‘ya ‘yansu maza kaciya a lokacin da yaran suka shekara biyar ko bakwai. Su kan yi wannan kaciya a lokacin huturu wato a lokacin ɗari.

 

Idan za ayi wannan kaciya akan tara ‘yan unguwa ɗaya ko gida ɗaya ayi masu gaba ɗaya. Kamar misali masu bin addinin Ɗanƙunƙurutu da Ɗaukar Maiki da Magiro kusan mataki ɗaya suke bi, idan za su yiwa ‘ya’yansu kaciya, su kan tara fiye da yara hamsin su yi masu kaciya gaba ɗaya.

 

Haka kuma ranar da za a yi kaciya danginsu za su taru ashirya wani gagarumin buki, har da makaɗa. Bayan wannan kuma za a dafa giya da yanke-yanken kaji ayi ta sha, ana kuma rawa. Dangi kuma za su dinga baiwa makaɗa da wanzamai kari da bacaka da kuɗi.

 

Bayan an yi wa yara kaciya wanzame zai dinga zagayawa bayan ‘yan kwanaki kaɗan domin ya duba yaran. In akwai wanda yake buƙatar wani magani ya bashi. Haka zai tayi har yaran su warke. Idan sun warke sai wanzame yasa musu ranar da zai zo ya yi masu wanka a sa musu bance ko kuma warki. To wannan rana za a shirya wani buki, shi ne suke kira bukin fito.

 

Saboda haka, a wannan buki za a yi tanadin abinci da giya wadda jama’a za su sha. Haka kuma ‘yan uwan yara za su yita tara wa yaran gudummawa kamar awaki da kaji, domin ayi masu kiwo. A wannan rana ne za a salami shi wanzamen da ya yi wa yaran kaciya.

 

Amma al’adar masu bin addinin Kyauka ta bambanta da ta masu ɗaukar maiki da Magiro da kuma Ɗanƙunƙurutu, domin su masu bin addinin Kyauka, Kyauka ne yake yiwa yaron kaciya, kuma sukan tara kamar yara talatin a yi masu kaciya gaba ɗaya.

 

Haka kuma suma su kan dafa giya da kuma yanka kaji da awakai, domin baiwa jama’ar da suka halarci wannan buki na kaciya. Wannan ita ce hanyar gargajiya ta yiwa yara kaciya a ƙasar Kwatarkwashi. DAyyabu (2019).

 

3.7 KAMMALAWA

Kamar yadda aka gani a cikin wannan babi an yi magana a kan, taƙaitaccen tarihin masarautar Kwatarkwashi, inda mai bincike ya kawo ra’ayoyin wasu masana daban- daban dangane da taƙaitaccen tarihin masarautar Kwatarkwashi. Wannan ya nuna mana cewa sarauta kalma ce babba mai ƙima da kuma mu’ujiza ga dukkan jinsi na al’ummar duniya.

A gaba kuma mai bincike ya yi bayanin ma’anar Kalmar kwatarkwashi. Mai bincike ya ci gaba da yin bayani a kan yadda garin Kwatarkwashi ya samu kafuwa.

 

A gaba kuwa mai bincike ya yi bayanin yadda Kwatarkwashi suke aiwatar da ire-iren addinansu na gargajiya, domin gudanar da bautar su. A gaba kuma mai bincike ya yi bayani a kan sana’o’in mutanen wannan gari na Kwatarkwashi iri daban-daban. A ƙarshe mai bincike ya yi bayanin irin yadda Kwatarkwasawa suke aiwatar da al’adunsu na yiwa yara kaciya.

Post a Comment

0 Comments