Ticker

6/recent/ticker-posts

Ido Mudu Ne, Ko Bai Ci Ba Ya San Abin Da Ke Cika Masa Tumbi




Ƙoshin lafiya shi ne makamin farauto kowane irin amfani a rayuwa. Wadataccen hankali shi ne maganaɗisun zamantakewa. Ilmi wani babban gamji ne na hutawar masu lafiya da hankali, domin more abubuwan da lafiya da hankali suka kalato. Haƙiƙa, biri ya yi kama da mutum, a tarihin farfajiyar ƙasar Illela, ba a taɓa taro na nuna farin ciki a kan samun ƙoshin lafiyar mutanen Illela ba. Ko shakka babu, ba mu taɓa taruwa a Illela ba domin bukin kasancewarmu masu hankali. Cikin…….
---------------------------------------------------
DAGA
ALIYU MUHAMMAD BUNZA
Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya,
Jami’ar Umaru Musa ‘Yar’adua, Katsina.
--------------------------------------------------------


Takardar da aka gabatar a buki na musamman domin karrama Farfesa Aminu Abubakar da Alhaji Bello Isah Ambarura da Sanusi Umar Illela da Jama’ar Ƙaramar Hukumar Illela, Jahar Sakkwato suka shirya ranar Asabar, 14 ga Disamba, 2013 a farfajiyar Ƙaramar Hukumar Illela.
Gabatarwa
          Ƙoshin lafiya shi ne makamin farauto kowane irin amfani a rayuwa. Wadataccen hankali shi ne maganaɗisun zamantakewa. Ilmi wani babban gamji ne na hutawar masu lafiya da hankali, domin more abubuwan da lafiya da hankali suka kalato. Haƙiƙa, biri ya yi kama da mutum, a tarihin farfajiyar ƙasar Illela, ba a taɓa taro na nuna farin ciki a kan samun ƙoshin lafiyar mutanen Illela ba. Ko shakka babu, ba mu taɓa taruwa a Illela ba domin bukin kasancewarmu masu hankali. Cikin ikon Allah, a yau, ga mu hallare domin bayyana wa duniya wata ɗaukaka da Allah Ya bai wa ‘yan’uwanmu ta ilimi da ɗaukakar da suka samu sanadiyyarsa. Ashe ban yi kure ba, idan na ce, ƙoshin lafiyarmu ya yi muna akala zuwa halartar wannan taro. Hankalinmu ya nuna muna irin muhimmancinsa. Don haka, ku bari in faɗi da babbar murya cewa, da lafiya da hankali talakawa ne, ilmi ne uban ƙasa domin shi kowa ya tabbatar da lafiyarsa da hankalinsa da basirarsa. A gai da iyayen ƙasar Illela, Allah Ya yi muku jagora.
Mene ne Ilmi?
        A Hausance, “Ilmi” baƙuwar kalma ce mai ƙoƙarin yi wa kalmar “sani” tawaye. A fayyace abu ta fuskar ƙwanƙwance amfanoninsa, da ƙididdige illolinsa, da ƙyallaro dambarwarsa, da sarrafa fuskokinsa, da yin kane-kane cikin zarafinsa, masaninsa ya zamo hannu ya iya jiki ya saba, ko an daka cikin turmi da su cikin masu fita. Wannan shi ne taƙaitaccen li’irabin sani a wajenmu ɗalibai. Idan ba ku manta ba, mukan ji magabata na cewa, sanin wurin bugu shi ne ƙira. Sanin asali kan sa kura cin kanjilo (ƙonannen kashin shanu). Dillalin wada shi ya san kuɗin jariri. Rashin sani ya fi dare duhu. Ban sani ba ta raba ka da kowa. Sanin halin direba sai fasinja. Ƙaramin sani ƙuƙumi ne. Ke nan, “sani” shi ne fahimtar abu na ƙin ƙarawa har a zama malaminsa. Wannan ita ce fatar duniyar ƙarninmu (ƙarni na 21), kuma kowace ƙasa ta kasa biya wa mutanenta wannan buƙata durƙusasshiyar ƙasa ce.
          Masana na cewa, daga cikin ma’anonin sani (ilmi) akwai aiki da shi. A ga ya bayyana ga mai bayar da shi. A ga nasonsa ga mai karɓarsa. A ga tasirinsa ga wurin da ake aikata shi. A ji samatarsa ga zantukan al’ummar da ya wanzu. A ga haskensa ga fuskokinsu. Yadda za a tabbata waɗannan batutuwa shi ne, bai wa ma’abota sani gabaci ga abin da suka sani. Idan aka yi haka, an yi wa sani adalci. Ma’abota ilmi na duniya (UN da UNESCO) sun yi canjaras a kan sakaɗa fasahar karatu da rubutu cikin shikashikan ilmi. Don haka, ga musulman Nijeriya ilmin boko ba komai ba ne face cikon sunna makaho da waiwaya, domin ko kafin a haifi uwar mai sabulu balbela tana da farinta.
Ƙalubalen Ilmi a Ƙarni na 21
        Kowace nahiya ta duniya da irin ƙalubalen da suke fuskanta na ilmi. Da Turai da Asiya da Ƙasashen Larabawa da Afirka duk ƙarancin kuɗi na yi wa ci gaban ilminsu barazana. Akwai matsalar kayan aiki, idan aka dubi yadda ilmi ke bunƙasa. Wadatattun malamai ƙwararru wata babbar matsala ce. Yalwataccen muhallin bayar da shi da karɓarsa shi ke hana ruwa gudu ga bunƙasarsa. Rashin aikin yi ga waɗanda suka sauke karatu na hana wa mai niyyar shiga miƙa wuya bori ya hau. Yawaitar manyan makarantu da Jami’o’i masu zaman kansu a duniyar ƙarni na 21 ya yi wa ilmi babban cikas na rage masa daraja da gwaɓi da kauri da inganci da kwarjini da ɗaukaka ga idon na bayan fage. Bai wa samun takardun shaida muhimmanci shi ya haifar da maguɗin jarrabawa, samun takardar shaidar zur, digirorin girshi da digirorin gado, ga su nan dai. Waɗannan matsalolin ruwan dare ne a duniyar zamaninmu.
          Tattare da waɗannan matsalolin ilmin ƙarninmu da ya fuskanci duniyar zamaninmu gadan-gadan idan muka dubi fannonin fasaha da kiyon lafiya da ƙere-ƙere da tattalin arziki da sufuri da kimiyyar noma da gine-gine da sadarwa da dai sauransu. Abin baƙin ciki, an bar Afirka da ilmin takarda na rubutun jarrabawa, Turai da Asiya suka ɗauki alƙalamin sarrafawa. Ina tsoron in ce, an bar mu da karatun Aku, domin ina jin har yanzu babu ƙasar da ake ƙera keke abin a zo a gani a nahiyarmu. Gwanjon tsumma na bura-bura da akirka su ne kangararrun matasanmu ke ƙawa da su, wai su gayu. Taɓa jikin motoci da babura su ne masu halinmu ke taƙama da su ana doro wai an take. Magungunansu na gargajiya yau su ne namu na zamani. Kaɗe-kaɗensu da bushe-bushensu da waƙoƙinsu da raye-rayensu yau su muka ara muka yafa muka watsar da namu. Harshensu shi ne ma’aunin gane ma’ilmanci a cikinmu. Tsarin siyasarsu ta aljanna ta mai ƙarfi ce sai in ba a yi shigan shanu ba, yau ita ce addininmu. Masarautunmu na asali mun tozarta su. Yau shugabanninsu su ne shugabannin duniya, namu masu yi musu gadi ne. Rayuwarsu ita ce rayuwa, wadda ba ita ba dabbanci ce. Addininsu shi ne addini, kininsa sunansa ta’addanci. Kaico! To, ina amfanin ilminmu na asali da na ƙaddara muke hura hanci da shi a yau?
          Hangen waɗannan matsaloli muka shirya wannan gagarumin buki na nuna farin cikinmu ga samun kujerar Shaihin Masani Aminu Abubakar, na Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato, da Magatakardan Dindindin, Alhaji Bello Isah Ambarura, da Mataimakin mai kula da Taskar Tarayya ta aikin ƙasa, Alhaji Sanusi Umar Illela. Da na jinjina takardun waɗannan managarta sai na ga, bai kamata mu yanke ƙauna ba, in da rai da rabo. Fatarmu ita ce, Farfesa Aminu ya fito da wani sabon salon da zai bai wa ‘yan bokon Illela ƙarfin guiwan burin kai ga irin matsayinsa. Alhaji Bello Isah da ya riga ya kai sin-wau-ra-takuri a cikin ofis ya sama wa matasan Illela gurabun aikin more wa karatunsu da suka yi. Alhaji Sanusi Umar ya mara musu baya a tabbata Illelawa ba su yi karatun Aku ba, bale a bar su a baya ga garaɓasar kimiyyar ƙarni na 21. Ku sani haihuwa hutawa ce, kuma samun ɗa nagari nagartacce irinku a irin wannan zamani shi ake ce wa tsintuwar guru cikin suɗi.
Lokacin Abu a yi shi
          A duniyarmu ta yau, boko ne makamin yaƙi. Boko ne hajar kasawa a kasuwa. Boko ne noman rani da damina. Boko ne sarauta, kuma shi ne siyasa. Don haka, babu makawa gare mu face buɗe gaba (ƙirji) ga kibiyar da ba ta kure. Wajibi ne ga hukuma ta kyautata makarantun Firamare yara su samu tushe nagartacce ga ilminsu. A inganta makarantun gaba ga Firamare da ƙwararrun malamai da kayan aiki. A fito da wata dabara ta bai wa ɗaliban digiri tallafi daga ƙananan hukumomi. Masu hannu da shuni su fara kafa gidauniya ta musamman domin agaza wa haziƙan ɗalibai su samu manyan digirori. A tilasta wa manyan ma’aikatan kowane gari sa hannunsu tsamo-tsamo ga tafiyar da makarantun da ke ƙarƙashin riƙonsu ko gundumarsu. A sake tunanin yadda za a kyautata wa malamai albashi da rayuwarsu domin sai in an yi shuka ake zancen tumu. Idan aka fito da tsarin tabbata wa duk wani ɗalibin da ya kammala karatu da nasara sama masa aikin yi, tsaron ƙasarmu da tarbiyyarmu za su inganta. A haramta kowane ofishin siyasa ga duk wanda ba ya da takardun shaidar ya ci jarrabawar da ya sauke. Da dai za a keɓe kujerar Shugaban ƙaramar hukuma da kujerar Majalisa ta kowane mataki ga masu digiri kawai, da za mu tabbata hutawa ka alewa man gyaɗa ka tuyar ƙosai.
          A fahimtata, taɓarɓarewar tarbiyyar yaranmu rashin tsaftataccen ilmi ya haddasa shi. Rashin tsaro da ta’addanci kuwa, talaucin da ke cizon matasa da rashin aikin yi ya ba su damar shiga Jami’ar Aljanna gafara wuta salamu alaikum (ƙundumbala). Matsalar da wannan ƙasa tamu take ciki a yanzu babban makamin fuskantar masu son su yi wa kaburburan kakanninmu fitsari da tsaye shi ne ilmin boko. Mu yi tsayin daka, mu yi shi ido buɗe, muna sara muna duban bakin gatari. A wajenmu ɗalibai, duk garin da ya samu ɗan bokon da ya hau kujerar Farfesa sun riga sun yi wa jahilci ƙofar raggo. In jahilci matar aure ce, sun yi mata saki uku. In jahilci dabba ce, sun yi mata duka/bugun kawo yuƙa. Daga yau masu lissafa Illela cikin ƙananan hukumomin da aka baro baya ga Ilmin boko an sa wa bakinsu takunkumi, daɗa babu sauran kukurukudu Inyamuri ya harbe kurciya.

Dare ka yi Maraice ya yi
          Hausawa na cewa, hankali ka gani ba ido ba. Mun san abin da wayo ya ɓoye hankali na gano shi. Abubuwan da ke faruwa a ƙasarmu sun fara zarce aya zaƙi. Kisan gilla da cin zarafi da wulaƙancin da ake yi muna da sunan ƙabilanci da bambancin addini da ɓangaranci ƙarƙashin yaudarar dimokoraɗiyya ya wuce gona da iri. Ala tilas mu yi amfani da bokonmu da addininmu da siyasarmu mu ‘yantar da kanmu cikin wannan bala’i. Dole mu yi watsi da bambance-bambancen fatin siyasa, da ƙabilanci, da saɓanin fahimta ta addini da wayewa, mu fuskanci bala’in da ake son a haddasa wa yankunanmu saboda ƙiyayya da mu da addininmu. Mu kafirce wa kowane fatin siyasa da ke cikin ƙasa mu kafa sabon fati mai take: YANKINMU ADDININMU AL’ADUNMU DA ‘YANCINMU. Abin da ya gabata ba mu yafe ba Allah Ya isa. Abin da ake ciki yanzu Allah Ya yi muna maganinsa. Shirin da aka yi na gaba Allah Ya wargaza shi. Addu’a makami ce, amma waɗanda ke gallaza muna yau ba da addu’a suke gallaza mu ba. Don haka, karen da duk ya yi cizo da gashinsa ake magani. In til in kwal rinin mahaukaciya. In ta yi ruwa rijiya, in ba ta yi ba masai. Haƙiƙa Larabawa sun faɗi gaskiya:
Mallam ya mut bis saifi
     Maata bi gairihi
Tanawwa’atul asbaabu
    Wal mautu wahidun

Ashe gaskiyar Ɗan’anace bai yi laifi ba da yake ce wa Shago:
Jagora: Tafi a kashe ka gaba ɗai,
          : Wandara mi kakai da rai ga arna,
          : Ai ko an kashe ka ba a da suna,
          : Don ɓannad da kay yi ta aka gyara,
          : In ko ka kashe su ka yi gaba ɗai,
        : Wandara maso rai wawa!

Matsoraci da raggo ba su da rana ga addininmu da al’adunmu. Hatta a fagen rashin gaskiya in ta yi cin alewar kuturu. Dubi yadda Alhaji Gambo ke ce wa ƙwarinsa:
Jagora: Mi kaka shakka ga ni ga ka!
          : Ɗauri kaka shakka ko kashewa?
          : Kaicon na kaina!
          : Gambo mai taɓa turayen mugunta.
 Naɗewa
        Bokonmu ba ya da amfani in bai ƙwato muna ‘yancinmu ba. Al’adunmu ba su amfane mu ba, in ba su kare mutuncinmu ba. Harshenmu ba ya da wata rana, in bai ɗebe muna takaicin maƙiyanmu ba. Wayonmu bai amfanar da mu da komai ba, in mun kasa ƙwace goriba hannun kuturu. Yawanmu bai amfane mu ba, idan mun kasa fitar da suhe wuta. Wace sabuwar waƙa za a sake ji idan maƙoƙo ya fito a bakin zabiya? Mun gaji da aikin banza wa kare wanka. Da ƙarfinmu da lafiyarmu a sa mu jiran gawon shanu. Wane sakaci ya fi wannan gyaran zama na baya ga walle. Haba! A ce ƙaton raggo da bai taɓa kashe wa kansa nama ba, mu kamo mu ba shi, ya cinye, ya sa wawayen makaɗansa yi muna kiɗa har da rawa da waƙa:
: Kai mai kiɗi kiɗa in jiya,
: Ba ka da aiki mu ba mu da,
: Mu taru mu lalace mu duka.
: Kai! Kakanti! Katingam! Tingam!

Post a Comment

0 Comments