DAGA
Abdulbasir Ahmad Atuwo
Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya
Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato.
07032492269
atuwo@yahoo.com
Da
Dano Balarabe Bunza
Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya
Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato.
07035141980
danobunza@yahoo.com
Tsakure
Waƙa na ɗaya daga cikin abubuwan da ke bayyanar da abin da ke cikin rayuwar
mawaƙi musamman abin day a shafi mu’amalarsa ta yau da kullum.Ilimin addini da
na gargajiya na tasiri cikin rayuwar mawaƙi musamman dangane da abubuwan da ya
rayu a kansu. Hausawa sun ce “Kowa da kiyon day a karɓe maƙwabcin mai akuya ya
sayi kura”. Wannan takarda ta ƙunshi bayanin luguden nassi Allah ta Maharazu
Barmu Kwasare. Haka kuma wannan takarda na ɗauke da taƙaitaccen tarihin
Maharazu Barmu Kwasare da aka yi amfani da wasu baitoci daga cikin wasu waƙoƙinsa.
1.0
Gabatarwa
9. Ku bar ɓata ku yi tcinka bayi,
Ku bar faɗin wani bawa ya yi,
Ai ba a yi sai Allah ya yi,
Abin da duk kaka dubin ka yi
Shi yan nufe ka da yi nai Allah.
Marubuta waƙoƙin Hausa sun daɗe suna rubuta waƙoƙi sai dai kowa da irin kiyon
da ya karɓe shi, maƙwabcin mai akuya ya sayi kura. Wasu sun raja’a kan rubuta
waƙoƙin addini, a yayin da waɗansu suka yi wa na hululu bante daidai da
kwankwasonsa. Waƙoƙin da wasu suka rubuta na gargaɗi da wa’azi ne da sauran
karantarwar addini, a inda za a sami waƙoƙin da wasu suka rubuta na shiryar da
masu sha’awarsu kamar daga duniya sai Kaduna. Ma’ana, wasu waƙoƙi na shiryarwa
ne ga jama’a, a inda waɗansu kuwa, lamurran duniya kaɗai suka fuskanta. Ganin
kasuwar da marubuta waƙoƙin Hausa ke ci ta wannan fuskar da aka yi bayani a
sama ya sa aka hango cewa waƙoƙin Maharazu na cikin waƙoƙin da ke jan hankalin
al’umma kan nuni da a rinƙa sara ana duban bakin gatari. Waƙoƙi ne da ke
tattare da rakiyar nafsoshin Alƙur’ani da Hadisai da kuma bayanin magabata, har
ya kasance da wuyar gaske a ɗaga waƙar Maharazu daga farko har zuwa ƙarshe ba
tare da an sami luguden nassi a ciki ba ko wuri ɗaya. Ganin haka ya sa na ƙudurci
nazarin luguden nassi a cikin waƙoƙinsa domin ko ba komi an ce malami ya
kasance rahama ga al’umma ba ya zama musiba gare su ba. Ganin ƙoƙarin da
Maharazu ya yi a fannin amfani da nassoshi a cikin waƙoƙinsa tare da la’akari
da alfanun da ake samu a ciki ya sa na ɗauki wannan ɓangare domin nazarinsa,
domin Hausawa sun ce “Ana bukin duniya, akan yi na ƙiyama”. Ganin salon luguden
nassi a cikin waƙoƙin Maharazu na tabbatar muna da cewa akwai tausaya wa
al’umma tare da lallashin zukatansu da cewa kowa ya shiga taitayinsa ga ayukan
da yake aikatawa, su kasance na alheri tare da guje wa na sharri. La’akari da
haka ya sa Maharazu ya ja kunnen al’umma a cikin wasu baitoci uku na waƙar
Allah yana cewa:
55. Ni ban da ilimi balle jidda,
Hankali kurum in yo muku fa’ida
Ilmi kaɗan na nir rida,
Na ji maza na nan su shidda,
Duk ba su ganin Manzon Allah.
56. Mai cin riba shi af farkonsu,
Da mai barin salawatul khamsu,
Gami da mai ƙarya babbansu,
Ga uku nan wada munka faɗe su,
Saurammu ukku da ikon Allah.
57. Mai yanke ƙauna gun ‘yan’uwa,
Mai canye zakkatai shi ƙi fissuwa,
Da mai barin mata tashi kassuwa,
Kun ji ukun suna bisa ɗemuwa,
Gidansu nesa ga Manzon Allah.
Kafin shiga cikin wannan takarda ya dace a bayyana ma’anar nassi da luguden
nassi tare da nau’o’insa tukuna.
2.0 Ma’anar Nassi
Kalmar nassi na ɗauke da bayanin cewa kalma ce ta suna kuma mai jinsin namiji,
kuma tilo. Jam’in wannan kalma shi ne nassoshi. Tare da haka kuma an ba da
ma’anar nassi da cewa, (i) ayoyin ƙur’ani ko Hadisi (ii) matani . Ita kuma
kalmar matani an ba ta ma’anar littafin da ba a yi wa sharhi ba . A wani wuri
kuma cewa aka yi nasi na nufin (noun, musculine). Any passage of the koran or
other Arabic book. Ana iya fahimtar ma’anar nassi daga littattafan da aka kawo
a sama da cewa madogara ce ko hujja ko dalili na faɗar wata magana ko aikata
wani aiki daga littafin Allah (Alƙur’ani) ko kuma daga maganar da fiyayyen
halittu ya faɗa ko aikin da ya aikata ko kuma aiki ko maganar da aka yi a
gabansa bai ce komi ba (Hadisi/sunna).
Aro nassoshin ƙur’ani da Hadisi da littattafan Furu’a da tarihi da adabi na
Larabawa ana lugude bayan bayyanar Musulunci da samuwar karatu da rubutu, ake
kira luguden nassi . Ana kiran sa “Iktabas” a cikin tsarin waƙoƙin Larabci ko a
ce da harshen Larabci..
3.0 Taƙaitaccen
Tarihin Maharazu Kwasare
Bayyana ko wane ne Maharazu baki ɗaya ba zai yiwu a cikin wannan takarda ba.
Akan iya yin tsakuren ko wane ne shi, sannan a ba da manazarta domin mai buƙatar
haka. Za a sami gamsasshen bayanin Maharazu a cikin , da kuma littafin Ibrahim
Yaro Yahaya za a sami sunansa ne na 12 a cikin marubuta waƙoƙi a jihar
Sakkwato.
Duk da haka ya dace a ji wani abu dagane da Maharazu. An haifi Maharazu a garin
Kwasare (wani ƙauye kusa ga garin Acida da ke ƙarƙashin ƙaramar Hukumar Mulkin
Wurno, a shekarar 1916). Ya tashi gidan karatun addini ya kuma yi karatun sosai
har ya kai an san shi a matsayin babban malami. Ɗankasuwa ne, mai sana’ar koli,
ya yi saƙar hula ƙube yana sayarwa. Allah ya yi masa baiwa a fagen rubuta waƙa
sai dai da Ajami yake rubuta waƙoƙinsa, kuma bai yi karatun boko ba. Ya yi
tafiye-tafiyen cin kasuwannin jihohin Sakkwato da Kebbi da Zamfara. Idan aka
sami waƙoƙinsa za a ga haka. Ya wallafa waƙa fiye da talatin.
Ba wannan kaɗai ba, Maharazu ya kawo ɗan bayanin kansa a cikin wasu bitocin waƙoƙinsa.
Za a ga wannan a waƙar masallaci da kuma waƙar da ya yi ta ta’aziyyar Malam
Babi. Ga abin da ya ce a cikin waƙar masallaci kamar haka:
Tammat daɗa Barmu ya cika wanga littafi,
Sunansa Maharazu halshenai da Hausanci.
Garinsu Kwasare, nasbatai guda biyu ta,
Abbun Eulatiyyi, ummu haƙiƙa Gobarci.
A cikin waƙar da ke biye kuwa, Maharazu ya faɗa da bakinsa domin ya kira kansa
sha’iri, almajiri, da ƙara nanata sunan garinsu. Ga baitocin da ke ɗauke da
zancen kamar haka:
Tammat daɗa waƙa ta cika,
Daga Barmu, Mahrazu sha’iri.
Birnin Kwasare nan yaf fita,
Wani mai yawo almajiri.
Wada anka nufai da hususiya,
A nufai da zamowa ɗahiri.
A cikin waɗannan baitoci akwai abin riƙawa dangane da ko wane ne Maharazu. Ko
ba komai, Hausawa sun ce “Waƙa a bakin mai ita ta fi daɗi”. Haka kuma, sunan
mahaifinsa Abdulbaƙi (Labbo Ɗanmariya), mahaifiyar sa kuma Rahamatu. Sunan ƙanensa
Malam Shehu. Maharazu ya rayu a duniya da shekara 63, sannan ya rasu a shekarar
1979. Ya shekara 36 da rasuwa a wannan shekara.
4.0
Nau’o’in Luguden Nassi
Kawo nassi a cikin waƙa nau’i-nau’i ne. Masana sun yi bayanin cewa akwai
nau’o’in salon luguden nassi iri uku aƙalla. Gas u nan tafe kamar haka:
1. Jawo nassi (kawo nassi kai tsaye)
2. Fassara nassi
3. Ishara zuwa ga nassi.
4.1 Jawo
Nassi:
Wannan na nufin marubuci ya kawo gundarin nassi daga Alƙur’ani ko Hadisi ko
kuma littattaffan Furu’a kai tsaye cikin gundarin nassin asali. A nan ne za a
ga aya cikakkiya ko sashenta domin kafa hujja ko yankar wani hukunci. A nan sai
an kawo ayar ko haidisin da Larabci kai tsaye. Misali duk lokacin da ake son
kawo nassin da ke tabbatar da kaɗaitar Allah idan aka ce Allah ahad ko kuma
Allah shi kaɗai yake ba ya da abokin tarayya, sai an kawo su cikin nassi
gundarinsa. Za a zo da wannan a cikin zuciyar takarda a ɓangaren luguden
nassin.
4.2
Fassara Nassi:
A nan ba jawo nassi ake yi ba tsagaronsa. Haka kuma ba ishara ake yi ba. Abin
da ake nufi da fassara nassi shi ne, kawo magana wadda da mai karatu ko sauraro
ya ji, zai gano bayanin ne kai tsaye daga Al’ƙur’ani ko Hadisi ko kuma ijma’in
da malumma masana suka yi a kan wata matsala domin samar wa alɗumma mafita..
Haka kuma idan aka ce fassara ana nufin mayar da ma’anar wata magana daga wani
harshe zuwa wani harshe. Yakan iya kasancewa daga harshen Larabci zuwa Hausa ko
kuma daga wani harshe zuwa wani. Misali, Allah bai haifa ba kuma ba a haife shi
ba. Kai tsaye akan iya gano fassarar ayar Alƙur’ani ce inda aka ce: (Lam yalid
walam yulad) idan aka sami haka a nassin Alƙur’ani ko Hadisi ko kuma maganar
magabata, shi ake nufi da fassara nassi.
4.3
Ishara zuwa ga Nassi:
Ishara zuwa ga nassi shi ne ambatar wata madogara ba tare da an jawo nassin ba.
Idan marubuci ya ambaci sunan wani littafi kowane iri ne idan dai ya yi hakan
ne domin kawo hujja to, ishara ce zuwa ga nassi. Misali duk marubucin da ke
magana har ya faɗi cewa a dubi Alƙur’ani ko Hadisi ko wani littafin Furu’a
domin ganin hujja, ishara ce zuwa ga nassi. Aikin da wannan takarda ke buƙatar
bayyanawa a nan shi ne ta ɗauki waɗannan nau’o’in luguden nassi da aka yi
bayanin ma’anarsu a sama kuma, a ga yadda Maharazu ya yi luguden su a cikin waƙarsa
mai suna ‘Waƙar Allah’. Ga abin nan zuwa kamar haka:
5.0
Luguden Nassi a Cikin Waƙar Allah Ta Maharazu Barmu Kwasare
Akan sami luguden nassi a cikin waƙoƙin waɗansu marubuta da waɗanda ba rubutawa
suke yi ba sai dai, amfani da nassi da ake samu cikin waƙoƙin waɗansu ya fi na
waɗansu yawa. Haka kuma akan iya tantance wanda yake almajiri daga wanda ya ɗauki
abin daga sama. Ko shakka babu, duk lokacin da aka ɗaga waƙoƙin Maharazu aka
duba za a tabbatar da almajiri ne ke magana kuma tare da tabbatar da cewa akwai
albarkar almajirci a ciki. Idan aka dubi Waƙar Allah da ya rubuta za a fahimci
cewa Maharazu ba ɗan haye ba ne a wurin amfani da nassoshi a cikin waƙar ba.
Duk wanda ya karanci Waƙar Allah la shakka zai fahimci malami ya yi wannan
rubutu. Ga yadda abin ya kasance:
5.1
Jawo/Kawo Nassi:
Wannan ɗaya ne daga cikin nau’o’in luguden nassi da wannan takarda ta duba.
Bayanin ma’anarsa ya gabata sai dai abin da ya rage shi ne fitowa da shi a gan
shi daga cikin Waƙar Allah. Ba kamar fassara nassi da ishara ba, jawo nassi na
tabbata ne da kawo tsagaron aya ko sashenta, hadisi ko sashensa da kuma
zance/maganar magabata kan wani abin da shari’a ke son yi wa matsayi.
Wata matsala da ke hana marubuta kawo tsagaron nassi a cikin waƙoƙinsu ita ce
tsoron lalacewar karin waƙarsu da suke yi. Maharazu ma bai kawo nassoshi da
yawa a cikin waƙarsa da yawa ba kamar yadda ya kawo luguden nassin ishara da
fassara nassi ba. Duk da haka ba a rasa ɗaya ko biyu da za a kawo a matsayin
misali ba. Ga misalin jawo nassi/kawo nasis daga Waƙar Allah ta Maharazu Barmu
Kwasare kamar haka:
23. Sarkin da anka yi ko na ina na,
Duk wanda anka naɗa sarki na,
Allah gwani babban sarki na,
Don shi ka kama wata haka rana,
Shi ad da kunfayakunu Allah.
Za a iya fahimtar cewa, gutsuro nassi ne aka yi a cikin wannan baiti, domin ba
aya ce gaba ɗayanta aka kawo ba. Rashin kawo ayar baki ɗaya kuma ba zai hana
abin ya sake ɗaukar wata fuska daga barin kasancewar sa jawo nassi ko kawo
nassi ba. Yana nan zamansa kawo nassi/jawo nassi sai dai kuma a matsayin
gutsurowa.
Maharazu ya yi amfani da sashen ƙarshe na ayar ya kawo domin za a tabbatar da
haka idan aka ga ayar baki ɗaya. Yadda ayar take shi ne: Iza arada shai’an fa
inna ma yaƙulu lahu kun fa yaku. Ma’ana Allah ya ce: Idan muka yi nufin wani
al’amari ya kasance, abin da za mu ce shi ne zamo sai kawai ya zamo/kasance,
sai ya kasance. Ga wani baiti da ke ɗauke da jawo nassi, wanda wannan nassi ne
na hadisi.
62. Ai mai kuɗi in ba shi da fashi,
To ko batun nassi bai tashi,
La’anahullahu rashi wal murtashi,
In kun duba sai ku gane shi,
Cikin iziyya bayin Allah.
Marubucin ya kawo nassi tsagwaronsa a layi na uku. Za a ƙara fahimta a nan
cewa, jawo nassi ko kawo nassi shi ne ɗauko hujja ko nassi a cikin kalmomin
asali ba tare da an canza ko ƙara komi ba, kuma idan aka koma ga tushe ya
kasance an same shi hakanan babu ragi babu ƙari. Misalan da aka kawo na jawo
nassi da ke sama haka za a tarar da su idan aka dubi wuraren da suke tun asali,
wato misalin farko an same shi cikin Alƙur’ani, na biyu kuma a cikin littafi
mai suna iziyya.
5.2 Fassara Nassi:
Bayanin ma’anar fassara nassi ya gabata a sama wanda ke nufin abu ɗaya idan aka
ce kawo ma’anar nassi. Akwai wannan nau’in luguden nassi a cikin waƙoƙin
Maharazu ƙwarai, sai dai za a yi la’akari da waƙar da ake magana a kai wato Waƙar
Allah. Maharazu na yawan fassara nassin Alƙur’ani a cikin Waƙar Allah, wanda
sai dai a ba da misalai kaɗan ba domin a kawo su duka ba. Idan kuma aka ce a
kawo su baki ɗaya abin zai yi yawa. Ga wasu misalai domin tabbatar da abin da
ake magana a kai.
5.2.1 Kaɗaitar Allah
Ko shakka babu Allah shi kaɗai yake, ba shi da abokin tarayya, kuma bai yi kama
da komi ba. Wannan na nuna ƙarfin imanin bayi ne a fagen kaɗaita Allah da suke
da a cikin zukatansu. Dangane da haka ne ya sa Maharazu ya fassara nassoshi kai
tsaye a cikin waƙarsa tare da tabbatar da kaɗaitar Allah wanda duk wanda ya
rasa wannan nau’i na imani sai dai a sake lale ɗan caca ya ga an yi masa coge.
Ga wasu baitoci tafe da ke nuna kaɗaita Allah a wurin bawa:
4. In za ni yin abu in ce Allah,
In nig gama in gode Allah,
In niy yi samu in ce Allah,
In nir rasa kuma in ce Allah,
Don babu mai komi sai Allah.
5. Ya sahibina in hore ka,
Al’amari in ya same ka,
Ɗayanta Allah shi ka isak ka,
In ko mutum ya zalunce ka,
Sa mai ido da amanar Allah.
15. Allah guda na shi yay yo mu,
Ya san yinimmu da ko kwanammu,
Shina matsuwammu shi koma ji ƙanmu,
Shina kashe mu shi ko tashe mu,
Sarkin da bai da magada Allah.
25. Sarki guda na ba shi da ɗan’uwa,
Shi da kowa bai tarewa,
Tashi sarauta ba ta misaltuwa,
Haƙiƙa bai gada ba ga kowa,
Balle a yo gadon ta ga Allah.
Da za a nazarci baitocin da ke sama a natse, za a tabbatar da Maharazu ya yi
amfani da nau’in fassara nassi daga cikin nau’o’in luguden nassi guda uku da
aka ambata a sama. Ayoyin Alƙur’ani ne da kuma Hadisai zalla ya kawo idan aka
tsaya aka tantance sosai. A baitin fakro, layi na farko Maharazu ya fassara
Bismillahi ne da kuma hadisin da Annabi SAW ya ce, “Duk aikin da za a fara ba
tare da an fara da sunan Allah ba, ya zan mai yankakken albarka”. Layi na biyu
kuwa marubucin ya fassara alhamdu lillahi ne. Ga shari’a idan za a fara cin
abinci an ce a kira/fara da sunan Allah. Idan aka ƙare cin abincin kuma sai a
gode wa Allah ta hanyar faɗar alhamdu lillahi. Layi na uku da na huɗu kuwa
fassarar hadisin Annabi SAW ne hadisi na biyu a ɓangaren bayanin abin da ake
nufi da imani tare da ginshiƙansa. A nan Maharazu na fassara yin imani da ƙaddara
mai kyau da maras kyau ne. A layin ƙarshen baiti kuwa ya ƙara jaddada muna cewa
yana da imanin komi da kowa na Allah ne. Duk abin da ka gani ga wani na Allah
ne ya ba shi in kuma rashi ne, daga Allah yake.
A baiti na biye kuwa daidai layi na uku, Maharazu na fassara ayar nan inda
Allah ya ce “Waman yatawakkal alallahi, fa huwa hasbuhu’. A baitin da ke biye
da wannan kuma, layi na huɗu fassara ce ta Yuhyi wa yumitu, a matsayin gutsuro
sashen aya. A baitin ƙarshe kuwa ya nuna Allah shi kaɗai yake ba ya da abokin
tarayya, tare da ba da tabbacin Allah bai gadi mulki ga kowa ba balle ya bar wa
wani gado. Ba ya da farko kuma ba ya da ƙarshe. A layin farko za a fahimci
fassarar ƙulhuwallahu ahad ce. Dangane da siffofin Allah kuma, Maharazu bai ƙyale
ba sai da ya kawo fassarar wata ayar da ke cikin suratul iklas a daidai layi na
uku kamar haka:
29. Har abada shi ke ikon nashi,
Bai gado kuma ba a gade shi,
Bai haifi kowwa ba a haife shi,
Shi agazan kar in saɓe shi,
Ba mai ƙidaye sarautar Allah.
A gundarin ayar ga yadda take:........................................... A
wani baiti da Maharazu ya kawo na abin da ya shafi ayukan Allah, ya kawo cewa,
Allah ke rayawa kuma shi ke kashewa. Maganar na nan daidai layi na huɗu kamar
haka:
15. Allah guda na shi yay yo mu,
Ya san yinimmu da ko kwanammu,
Shina matsuwammu shi koma ji ƙanmu,
Shina kashe mu shi ko tashe mu,
Sarkin da bai da magada Allah.
Wannan ya yi daidai da wurin da Allah ya ce:...................................
Haka kuma akwai fassarar wata aya da Maharazu ya kawo a layuka biyu na ƙarshen
baiti na 30 wurin da ya fassara Lahaula wala ƙuwwata illa billah. Ga baitin
kamar haka:
Yawan tsaro da yawaita dubara
Duk ba su kauda mutum ga hasara,
Babban tsari na nan ga Tabara,
Babu tsimi kuma babu dubara,
Sai wadda yay yi ma bawa Allah.
5.3 Ishara Zuwa ga Nassi:
Akan sami marubuta waƙa na yawan amfani da ishara zuwa ga nassi domin yin nuni
ga madogarar da suka gani kuma suka dogara a kai. Bayyana wurin da aka ga hujja
tare da ambaton suna ake kira ishara zuwa ga nassi. Ba a kawo nassin gundarinsa
sai dai a faɗi sunan abin da nassin ke ciki domin mai buƙata ya je ya samu ya
duba. Shi ma wannan nau’i na luguden nassi akwai shi a cikin waƙar Maharazu mai
suna Waƙar Allah. Ga misalai kamar haka:
58. Ku hau batun ga ƙwarai ku riƙe shi,
Ku tabbata ba ni na faɗe shi,
Wada nig ganai haka niw waƙe shi,
Cikin hadisi nis same shi,
Zancen Muhammadu Manzon Allah.
A nan Maharazu ya yi ishara da nassin hadisi a cikin wannan baiti tare da nuna
nan ne madogarar da ya laɓe gare ta. Idan aka kula sosai ishara ce ko nuni zuwa
ga nassi kai tsaye, wato nassin hadisin Manzon Allah (SAW). Akwai wani baiti da
ke ɗauke da irin isharar da ta gabata, mai zuwa kamar haka:
33. Ni jahili nike ba masani ba,
Amma batuna ba ƙarya ba,
Duk wanda ya ce ba hakanan ba,
To duk shi bar ratce shi bi turba,
Shi dubi Alƙur’anin Allah.
122. Uwat tawaye mil labari?
Aljanna kiy yi biɗa ko nari?
Kina bara da ɗiya jariri,
Batunki babu shi tun daf fari,
Da na ganai ga farillar Allah.
123. Cikin iziyya duk na duba,
Cikin Risala duk na duba,
Lawal da Sani duk na duba,
Kai! Had da ƙur’ani na duba,
Duk ban ganai ba ga ayar Allah.
A baiti na 33 da aka kawo, layin ƙarshe ne ishara zuwa ga nassi. Ya yi nuni da
a dubi Alƙur’ani za a ga hujja a ciki. Ita kuma farillar Allah da ke ƙarshen
baiti na 122 na nufin abin da aka wajabta da a yi, idan ba a yi ba kuma, an yi
laifi. Haka ma a baiti na 123, kawo sunan Iziyya da Risala da Lawali da Sani da
ƙur’ani da ayar Allah duk ishara ce zuwa ga nassi Maharazu ya yi. Ta kawo waɗannan
misalai da ke sama, ya yiwu a sami wani ya ƙaru da abin ta hanyar fa’idantuwa.
6.0
Kammalawa
Yin la’akari da muhimmancin da salon luguden nassi a ickin rubutattun waƙoƙin
Hausa ke ɗauke da shi ya sanya aka duƙufa a wajen nazarin Waƙar Allah ta
Maharazu Barmu Kwasare domin a fito da shi. An dubi ma’anarsa (luguden nassi)
da nassi shi kansa. Haka kuma takardar ta zo da bayanin ko wane ne Maharazu, keɓance
daga bakinsa cikin wasu baitocin waƙoƙinsa. Haka kuma akwai bayanan da aka samo
daga waɗanda suka san shi. har yanzu takardar na ƙunshe da nau’o’in luguden
nassi manya guda uku fassara nassi da ishara zuwa ga nassi da kuma jawo nassi
kai tsaye, tare da bayanin kowane da misalai gwargwado ta yadda za a nazarci
abin cikin sauƙa ba tare da samun ruɗewa ba. hasali ma, za a tarar mafi yawan
murubuta waƙoƙin da ke amfnai da salon sarrafa nassi cikin waƙoƙinsu almajirai
ne. wanda ba haka ba kuma sai dai ya rubuta waƙarsa ba tare da ya taɓo assi ba
balle ya yi lugudensa a cikin waƙarsa.
Karanta wani
https://www.amsoshi.com/2017/07/18/isa-rasco-dangoma-ayyukansa-duniyar-adabin-hausa/
Manazarta
Ainu, H. (2006), “Rubutattun Waƙoƙin Addu’a na Hausa”: Nazarin Jigogi da
Salonsu”. Kundin digiri na Uku da aka gabatar a sashen Nazarin Harsunan
Nijeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato.
Birnin Tudu, S.Y. (2002), Jigo da Salon Rubutattun Waƙoƙin Furu’a na ƙarni na
Ashirin”. Kundin digiri na uku, Sashen Koyar da Harsunan Nijeirya, Jami’ar
Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato.
Birniwa, H.A. (1987), “Conservatism And Discent”. A Comparative Study of
NPC/NPN and NEPU/PRP Hausa Political Verse from Ca 1946-1988. Kudnin digiri na
uku, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato.
Birniwa, H.A. (2003), “Tasirin Matanin Alƙur’ani da Hadisi Cikin Trubutattun Waƙoƙin
Ashirin da biyu na Marubuta goma sha huɗu masu tsokaci daga ko dai Ayoyin Alƙur’ani
ko kuma Hadisai.
Birniwa, H.A. (2002), “Salon Riwayar Hadisi a cikin Imfiraji na Dr. Aliyu
Namangi, Sashen Koyar da Harsunan Nijeirya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato.
Amin M.L. (2001), ‘Waƙoƙin Jihadi Goshin ƙarni Na 21’. Mujallar Hausa Studies
Vol. II No 2.
Birniwa H.A. (1981), ‘The Infiraji of Aliyu Namangi’ Kundin digiri na biyu
(SOAS), University of London.
Birniwa H.A. ( ), ‘Tasirin Matanin Alƙurani Da Hadisi Cikin Rubutattun Waƙoƙi
Ashirin Da Biyu Na Marubuta Goma Sha Huɗu, Masu Tsokaci Daga Ko Dai Ayoyin Alƙur’ani
Ko kuwa Hadisai’.
Bugaje H.M (2010), ‘Wa’azi A Rubutattun Waƙoƙin Mata Na ƙarni Na Ishirin’.
Kundin Digirin MA Jami’ar Ahmadu Bello, Zariya.
Bunza A.M (2009), Narambaɗa, Ibrash Islamic Publications center, Lagos.
Ɗangambo A. (1980), ‘Hausa Wa’azi Verse From Ca 1800-1970. a Critical Study of
Form, Content, Language And Style’ Ph D Thesis, S.O.A.S, University of London.
Ɗangambo, A (1981), Ɗaurayar Gadon Feɗe Waƙa.
Funtua, A.I. (30th June 2003 – 4th July), ‘The Contribution Of Abdullahi B.
Fudi To The Development OF Hausa Verse. A Study Of Their Form, Theme And
Stgle’. Being A Paper Presented At A National Conderence, Organised By School
Of Arts And Social Sciences Federal College OF Education, Katsina.
Galadanci, M.K.M (1975), ‘The Poetic Marriage Between Arabic And Hausa’, Maƙalar
da aka gabatar a cikin mujallar Harsunan Nijeriya V 1-16 CNHN Jami’ar Bayero,
Kano.
Gummi, A.M. (Babu Shekarar Bugawa), Alƙur’ani Mai Girma Da Kuma Tarjamar
Ma’anoninsa Zuwa Ga Harshen Hausa Wurin Da Aka Tanada Musamman Don Buga Alƙur’ani
Mai Girma, Na Mai Kula Da Masallatai Biyu Masu Tsarki, Fahad, Madina.
Hiskett M. (1969), ‘Hausa Islamic Verse: Its Sources And Development Prior To
1920’, Ph D SOAS. University Of London.
Hiskett M. (1975), A History OF Hausa Islamic Verse, University Of London SOAS.
Malet Street,London WCIE 7HP.
Ibrahim A. (2005), ‘Waƙoƙin Kungiyoyin Mawallafa Bege Da Gargaɗi Ta Birnin
Sakkwato’.Kundin Digirin farko, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato.
Jami’ar Bayero Kano (2007), ƙamusun Hausa, Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya,
B.U.K.
ƙaura H.I (1994), ‘ƙawancen Salo A Tsakanin Rubutattun Waƙoƙi’
. Kundin Digirin farko, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato.
Maigandi A. (2009), ‘Sharhin Waƙoƙin Da Aka Rubuta A Kan Jigon Addini Da
Muhimmancinsu’. Kundin digirin farko, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato.
Malumfashi, A.I. (1983), ‘Wa’azi A Rubutattun Waƙoƙin ƙarni na Ashirin’. Maƙalar
da aka gabatar a taron kara wa juna sani da Hukumar Fasaha da Al’adun Gargajiya
ta Jihar Sakkwato ta shirya a ƙarƙashin ƙungiyar Manazarta Waƙoƙin Hausa.
Muhtar I. (1984), ‘Nahawun Waƙa: Yanaye-yanayensa Da Sigoginsa Cikin Rubutattun
Waƙoƙin Hausa’. Kundin MA Jami’ar Bayero, Kano.
Omar, S. (1983), ‘Style And Theme in the Poems of Mu’azu Haɗeja’. Kundin digiri
na biyu, SOAS University of London.
Sa’id B. (2002), ‘Rubutattun Waƙoƙin Hausa na Karni Na IShirin A Sakkwato Da
Kebbi Da Zamfara’ Kundin Digiri na uku, Sas
hen Nazarin Harsunan Nijeriya Jami’ar Beyero. Kano.
Sarɓi S.A (2007), Nazarin Waƙen Hausa Samarid Publishers A Division Of Samarid
Ventures LTD Plot 326, Sallari, Babbangiji Kano, Nigeria.
Usman, B.B. (2008), ‘Hikimar Magabata: Nazari A Kan Rayuwar Malam (Dr.) Umaru
Nassarawa Wazirin Gwandu (1916-2000) da Waƙoƙinsa’. Kundin Digiri na uku,
Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato.
Usman B.B (1997), ‘Poetry As A Source Of Historical Records: Umaru. Wazarin
Gwandu Poem Of Shago Famine’ Takardar Da Aka gabatar A Taron Na 41 Da 42 Na
Congress Of The Historical Society Of Nigeria A Jami’ar Maiduguri, Daga 27 Zuwa
30 Ga Satumba.
Yahya A.B (1982), Jigon Nazarin Waƙa, FISBAS Media Service, Kaduna.
Yahaya A.B. (1995), ‘Kwatancen Jigo Tsakanin Waƙoƙin Sarauta Na Baka Da
Rubutatun Cikin Harsunan Nijeriya’, 17.34-56. CNHN Jami’ar Bayero, Kano.
Yahya A.B (2001), ‘Dangantakar waƙa Da Tarbiyar ‘Ya’yan Hausawa’ Cikin Harsunan
Nijeriya XIX” 94-108, CNHN Jami’ar Bayero, Kano.
Yahya A.B. (2001), Salo Asirin Waƙa, FISBAS Media Services, Kaduna.
Yahya A.B. (1983), ‘A Critical Anthology Of The verse Of Alhaji Bello Giɗaɗawa’
Kundin digiri na biyu, Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero, Kano.
Yahya A.B. (1989), ‘The Verse Category of Madahu With Special Reference To
Theme, Style And Background Of Islamic Source And Belief’ Kundin digiri na uku,
U.D.U. Sokoto.
Yahya A.B.( ), ‘Rubutattun Waƙoƙin Nasiha: Wani Ɓangare Ko Kuma Sauyin Salo A
Cikin Rubutattun Waƙoƙin Hausa Na Wa’azi’ Cikin Algaita, Jami’ar Bayero, Kano.
Yahaya I.Y (1988), Hausa A Rubuce: Tarihin Rubuce-Rubuce A Cikin Hausa, NNPC
Zaria.
Zurmi A.D (2006), ‘Tsoratarwa A Cikin Waƙoƙin Wa’azi Na Nana Asma’u ‘Yar Shehu,
Usmanu Danfodiyo’ kundin digirin farko, U.D.U. Sokoto.
Zungur A.M.S (1976, 77,81, 2008), Waƙoƙin Sa’adu Zungur NNPC, Zaria.
2 Comments
[…] Karanta wani […]
ReplyDeleteI enjoy the article
ReplyDeleteENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.