Jagora:
Ya shiryi zama daku mutanen kudu,
Duk ku kiyaye hali nai
Y/Amshi:
Baya cema bara nai
tahi samo man rance,
Baya cewa yau wane ina kai ma malka,
Babu mai tcira wargi
yaji tsoron ɗamri nai.
Haka dai ☝️☝️Makaɗa Alh. (Dr.) Ibrahim
Narambaɗa Tubali ya faɗa a faifansa na Marigayi
mai girma Uban Ƙasar/Hakimin Gundumar Gusau wato Sarkin Kudun Gusau, Alh.
Sulaiman Ibrahim mai amshi:
"Mai Gusau raba kaya,
Ba a kaimaka wargi,
Mai rabo da yawa
gamda'aren S/Gobir".
Shi ne Sarkin Gusau/Uban Ƙasar
/Hakimin Gundumar Gusau na 13 tun daga Malam Muhammadu Sambo Dan Ashafa da ya ƙirƙiri
Gusau ya kuma yi mulki daga 1806 zuwa wafatinsa a shekarar 1827 (shi Malam
Muhammadu Sambo Dan Ashafa).
Shi dai ne Sarkin Gusau na 6 daga
cikin tsarin Sarakunan Gusau da ba daga gidan Mal. Muhammadu Sambo Dan Ashafa
suka fito ba, wato tun daga shekarar 1917 da aka fara naɗa wasu mutane daga Sakkwato ana kai su a
matsayin Sarakuna /Uwayen Ƙasar /Hakiman Gundumar Gusau kuma shi ne na ƙarshe
a wannan tsari domin bayan rasuwarsa a ranar 1/7/1984 sarautar ta dawo gidan
Sarki Malam Muhammadu Sambo Dan Ashafa ya zuwa yau.
A waɗannan ɗiyan
waƙa
☝️☝️Makaɗa Ibrahim Narambaɗa Tubali ya taskace wasu
daga cikin kyawawan halayen Sarkin Kudun Gusau Sulaiman Ibrahim.
Yana bayyana cewa koda aka kawo
shi a matsayin Sarki a Gusau ya shiryawa zaman sarauta (Narambaɗa ya kira mutanen Gusau da
mutanen kudu) domin Gusau tana kudu maso gabas da Sakkwato ne.
Gusau tana da attajirai sosai da
suka shahara a lokacin da aka naɗa
shi sarautar garin a ranar 1-8-1951. Amma kamun kai da riƙe
girma irin nasa ya hana masa neman buƙata koda ta rance ne ballantana ya yi kwaɗayin abun hannun talakansa.
Ibrahim Narambaɗa ya ci gaba da nuna halin
dattako da tawali'u da zuhudu na wannan Basarake ta hanyar nuna duk yadda
tsanani ya kai bai taɓa
nuna zuwa gidan wani mai abun hannunsa daga cikin talakawan dake ƙarƙashin
ikonsa ba domin ya taimaka masa da abinci koda kuwa an shiga yanayin
malka/marka, wato a lokacin damina da ake tsulla ruwan sama kamar dai watan
Agusta da Bahaushe ke kira watan ruwa( a wasu yankuna na Jihar Zamfara ana
kiran wannan yanayi da malkac ci kashin ka) saboda sama ruwa ƙasa
ruwa ne, ko kana da hatsi a rihewa /rumbu /sito idan ba a buhu yake ba ruwan da
ake yi bazai bari ka samu damar a sussuka maka shi ba ballantana ka samu na
kalaci.
A daidai irin wannan yanayi ne
masu ɗan ƙaramin
ƙarfi
da maras sa dangana da kwaɗayi
ke ƙoƙarin
zuwa gidajen masu abun hannunsu /attajirai da waɗanda
ke da abinci a ajiye domin su samu fita daga cikin wannan mawuyacin hali.
Wannan shi ne dalilin da yasa ake faɗar
"Zan kai wa wane malka/marka".
Saboda zamansa kamilallen mutum
wanda ya san daga gidan da ya fito sai Makaɗa
Narambaɗa ya bayyana
cewa "Baya cewa yau wane ina kai ma malka". Tun da ya kame kansa daga
abun hannun talakawansa ba zai yi ƙasa a gwiwa ba wajen ladabtar da duk
wanda ya saɓa dokoki
ko ƙa'idar
zamantakewar yau da kullum ba.
An haifi Marigayi Alhaji Sulaiman
Ibrahim a shekarar 1909 a garin Isa ta Jihar Sakkwato. Mahaifinsa shi ne Sarkin
Gobir /Uban Ƙasar
/Hakimin Gundumar Isa Malam Ibrahim ɗan
Sarkin Gobir na Isa Umaru ɗan
Sarkin Musulmi Aliyu ƙarami ɗan
Sarkin Musulmi Muhammadu Bello ɗan
Mujaddadi Shehu Usman Danfodiyo Tagammadahullah Birahamatihi.
Yayi sarautar Gusau daga ranar
1-8-1951 zuwa wafatinsa a ranar 1-7-1984.Ya bar matan aure da ya'ya da jikoki
da tattaɓa kunne masu
dama.
Daga cikin ya'yansa akwai mai
girma Ɗangaladiman
Sakkwato, Alh. Shehu Sulaiman da Bunun Sakkwato, Alhaji Aliyu Sulaiman da kuma Ɗan
Amar na Sakkwato, Alh. Yusuf Sulaiman.
Marigayi mai girma Sarkin Kudun
Gusau Alhaji Sulaiman Ibrahim ne a wannan hoto.
Allah SWT ya jaddada masa rahama
shi da sauran dukan magabatanmu ya sa mu wanye lafiya mu cika da kyau da imani
Alfarmar Fiyayyen Halitta Rasulallahi Sallallahu Alaihim Wasallam, amin ya
rabbal alamin.
Daga taskar
Hon. Ibrahim Muhammad (Ɗanmadamin Birnin Magaji) Jihar Zamfara, Nijeriya.
13/07/2026.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.