Ticker

6/recent/ticker-posts

Ma’anar Aure

Daga

Shafa'atu Salihu Labbo
Abu-Ubaida Sani

Aure a Kunshiyar Karin Magana

Babban gurbin da aure yake da shi a al’adun Hausawa ya sa masana da manazarta da dama sun yi rubuce-rubuce game da shi. Yana ɗaya daga cikin batutuwan da aka fi yawan nazartar su a fannin ilimin al’ada. A ƙamusun Hausa (CNHN, 2006 sh. 22) an bayyana aure a matsayin “Dangantaka tsakanin namiji da mace ta hanyar shari’ah.”

Alhassan da wasu (1982 sh. 9) sun bayar da ma’anar aure da cewa “... alaƙa ce ta haliccin zaman tare tsakanin namiji da macce.” Idan aka lura, wannan ma’ana ta yi daidai da wadda aka kawo a cikin Ƙamusun Hausa na Jamiar Bayero.

Da alama mafi yawan manazarta sun aminta da wannan ma’ana. Za a iya fahimtar hakan yayin da aka yi la’akari da yadda ma’anar da Yahaya da wasu (1992) suka bayar ta bi sahun waɗannan da aka kawo a sama. Sun bayyana aure da cewa “... wata hanya ce ta ƙulla zaman tare tsakanin namiji da mace ba tare da iyakancewa ba, sai in mutuwa ta raba wanda ake tabbatarwa ta amincewar maaurata da waliyansu da kafa shaidu.” (Yahaya da wasu, 1992 sh. 94). Duk da haka, a cikin wannan ma’ana ta su Yahaya, za a iya lura da ƙarin da aka samu wanda ya faɗaɗa ma’anar. Ƙarin ya shafi zayyano wasu ƙaidoji da suke kai ga tabbatuwar aure, wato:

a.      Amincewar ma’aurata

b.      Amincewar waliyyai

c.       Kafa shaidu

Babu shakka wannan ma’ana ta samu tasirin addinin Musulunci. Abubuwan da aka ambata a sama suna daga cikin sharuɗan cikan aure da addinin Musulunci ya gindaya.

A wata ma’ana da Muhammad ya bayar, an sake samun batun addinin Musulunci kai tsaye.[1] Ya bayar da ma’anar aure da cewa: “Aure wani zama ne halastacce tsakanin mata da miji wanda al’ada da addini suka yarda da shi” Muhammad (2020 sh. 50). Duba da wannan za mu fahimci cewa aure wani lamari ne na zaman tare da cuɗanya da juna wanda aka gina shi a kan fatar ɗorewar zamantakewa.

A tunanin Hausawan ƙarini na 21, ana iya cewa aure na nufin wata yarjejeniya ta musamman da ake ƙullawa tsakanin namiji da mace bisa wasu sharuɗa da ƙaidoji da suka fara tun daga nema har zuwa ɗaurawa da tarewa da abubuwan da ke biyo baya da suka shafi zamantakewa a matsayin miji da mata bisa waɗansu ƙayyadaddun tanade-tanaden alada da addini.



[1] Duk waɗannan suna nuna yadda Musulunci ya yi tasiri ga rayuwar Hausawa. Ya yi tasiri ga kowane fanni, har da al’adunsu da suka shafi auratayya.

Manazarta

Labbo, S.S. & Sani, A-U. (2025). Aure a ƙunshiyar karin magana. Amsoshi Academic Publishers. ISBN: 978-1-257-07209-5. DOI: https://doi.org/10.5281/zenodo.19513449 

Post a Comment

0 Comments