Ticker

6/recent/ticker-posts

Hukuncin Sanya Hoton Mamaci A Social Media

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

As Salamu Alaikum Wa Rahmatul Laahi Wa Barakatuh. Da fatan malam yana lafiya. Please, malam ya halatta a sa hoton mamaci a social media kamar a profile ko status?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikumussalam warahmatullahi wabarakatuhu

A Musulunci, malaman addini sun bayyana cewa bai halatta a riƙa saka hotunan mutane, ciki har da na mamata, a shafukan sada zumunta kamar DP (Profile) ko Status ba.

Abin da Malamai suka tabbatar a nan shi ne: Idan dai ba da larura (kamar na passport don shiga makarantu ko neman aiki ko fita ƙasashen waje da makamantansu) ba, musulmi ba ya yin harka ko muamala da hotuna na abubuwa masu rai (kamar mutum, dabba, tsuntsu, ƙwaro da sauransu), ko masu inuwa ne (kamar sassaƙaƙƙu ko ginannu), ko marasa inuwa (kamar waɗanda aka zana da hannu ko aka ɗauka da kyamara (camera). Saboda irin kausasa magana da tsawa mai tsanani da shari’a ta yi a kan haka:

Abu ne sananne cewa: Hotuna su ne dalilin farko na kaucewar mutane daga kan hanyar Allaah tun a zamanin Annabi Nuhu (Alaihis Salaatu Was Salaam). Mutanen zamaninsa su ne suka sassaƙa hotunan manyan malamansu domin tunawa da su a farko, amma daga baya sai suka zama abubuwan bauta ba Allaah ba!

Daga ƙarshe kuma da aka turo Manzon Allaah Mai waazi na farko a duniya: Annabi Nuhu (Alaihis Salaam) domin ya hana su, sai kawai suka kangare kuma suka taurare, har ma suka riƙa faɗa wa mutanensu, kamar yadda Allaah Ta’aala ya ambato daga gare su:

وَقَالُوا لَا تَذَرُنَّ آلِهَتَكُمْ وَلَا تَذَرُنَّ وَدًّا وَلَا سُوَاعًا وَلَا يَغُوثَ وَيَعُوقَ وَنَسْرًا

Kuma suka ce: Kar ku yarda ku rabu da Waddu da Suwaa’u da Yaguthu da Ya’uqu da Nasru.

A ƙarshe ƙissar dai hallaka ce ta same su, kamar yadda Allaah ya ce:

مِمَّا خَطِيئَاتِهِمْ أُغْرِقُوا فَأُدْخِلُوا نَارًا فَلَمْ يَجِدُوا لَهُمْ مِنْ دُونِ اللَّهِ أَنْصَارًا

Saboda irin laifuffukansu sai aka nutsar da su a cikin ruwa kuma aka shigar da su cikin Wuta, kuma ba su samu wani mataimaki ba a bayan Allaah.

Sannan a cikin Hadisai sahihai Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya yi tsawa a kan al’amuran hotuna, kuma bai bambance ba a tsakanin nau’ukansu, kamar inda ya ce:

أَشَدُّ النَّاسِ عَذَاباً الَّذِينَ يُضَاحُونَ بِخَلْقِ اللهِ

Mafiya samun tsananin azaba daga cikin mutane su ne: Waɗanda suke kwaikwayon halittar Allaah Haka kuma inda ya ce:

أَشَدَّ النَّاسِ عَذَابً يَوْمَ الْقِيَامَةِ الْمُصَوِّرُونَ، يُقَالُ لَهُمْ أَحْيًون مَا خَلَقْتُمْ

Mafiya samun tsananin azaba daga cikin mutane a Ranar Ƙiyamah su ne: Masu yin hotuna, za a ce da su: Ku raya irin abubuwan da kuka halitta.

Al Imamul Bukhaari (3226) da imam Muslim (2106) sun ruwaito hadisi daga Abu Talhah (Allah ya ƙara masa yarda) cewa Manzon Allah (Sallallahu alaihi Wasallam) ya ce; Mala'iku basa shiga gidan da da akwai hoto acikinsa.

Al Imamul Nawawi (Allah yaji kansa da rahama) ya ce: Malamai sun ce: Dalilin da ya sa basa shiga gidan da akwai hoto acikinsa saboda akwai zunubi mai raɗaɗi, kuma gasa ne da halittar Allah.

Don haka, ba daidai ba ne musulmi ya riƙa amfani da hotunan mutane (rayayyu ko matattu, manya ko yara, kuma maza ko mata, haka ma sauran dabbobi ko tsuntsaye da sauransu) a cikin social media kamar yadda aka bayyana a cikin tambayar, ko kuma a wani wurin da ba wannan ba, in dai ba da wata larura mai ƙarfi ba.

Maimakon sanya hotunansu wanda zai iya zama laifi a shari'a, ana ƙarfafa musulmi da su maye gurbinsa da; Yin musu addu'ar neman rahamar Allah da gafarar zunubai. Yimusu sadaka domin samun ladan da zai kai gare su.

WALLAHU A'ALAM

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.

    ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam 

Post a Comment

0 Comments