𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
As-Salaam Alaikum Wa Rahmatul Laah. Mahaifiyarsa ta umurce shi ya sake ni, amma dayake bai iya rubutu ba sai matarsa (kishiyata) ta rubuta. Da ya miƙa mini takardar sai na ga saki uku ne, shi kuma ya ce saki ɗaya ne kawai ya ce. To, mene ne matsayin wannan?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikumus Salaam
Wa Rahmatul Laah Wa Barakaatuh.
Bin umurnin iyaye a
wurin sakin aure ba wajibi ba ne, kuma saɓa musu a kan haka ba laifi ba ne, sai fa ko
in akwai wani dalili na shari’a da suka dogara a kansa. Amma hadisin nan sahihi
da Abu-Daawud (5138) da At-Tirmiziy (1189) da Ibn Maajah (2088) suka riwaito
daga Ibn Umar _(Radiyal Laahu Anhumaa)_ cewa:
كَانَتْ
تَحْتِى امْرَأَةٌ وَكُنْتُ أُحِبُّهَا ، وَكَانَ عُمَرُ يَكْرَهُهَا ، فَقَالَ
لِى : طَلِّقْهَا ، فَأَبَيْتُ ، فَأَتَى عُمَرُ النَّبِىَّ - صَلَّى اللهُ
عَلَيْهِ وَآلِهِ وَسَلَّمَ - فَذَكَرَ ذَلِكَ لَهُ ، فَقَالَ النَّبِىُّ - صَلَّى
اللهُ عَلَيْهِ وَآلِهِ وَسَلَّمَ - : « طَلِّقْهَا »
Ya kasance ina da
wata matar aure wadda nake son ta, shi kuma Umar yana ƙin ta. Don haka sai
ya ce mini: Ka sake ta, ni kuma na ƙi. Sai Umar ya tafi
wurin Annabi _(Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam)_ ya faɗa masa haka, sai
Annabi _(Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam)_ ya ce mini: Ka sake ta.
Malamai sun ɗauki wannan wata
mas’ala ce da ta shafi wannan matar ita kaɗai, ba abu ne da ya shafi kowa da kowa ba.
Shiyasa a lokacin da wani ya kawo kuka wurin Al-Imaam Ahmad _(Rahimahul Laah)_
a kan cewa mahaifinsa ya umurce shi da ya saki matarsa, sai ya ce masa: Shin
babanka kamar Umar ya ke?!
A taƙaice dai duk lokacin
da wani daga cikin iyaye ko dukkansu suka nemi ɗa ya saki matarsa, ba a gaggawan bin
maganarsu, har sai lokacin da aka binciki matsalar kuma aka tabbatar da
gaskiyar matsayinsu. Kamar idan aka fahimci cewa cigaba da zamansu tare zai
raunana ko ya rushe addinin ɗayansu ko dukkansu.
Wanda aka tilasta
masa a wurin saki, sakin bai auku ba. Domin wanda ba shi da zaɓin ransa, kamar wanda
aka tilasta masa, ko mai maye, ko ruɗaɗɗe, ko wanda yake cikin matsanancin fushi,
malamai sun rinjayar da rashin aukuwar sakinsa ne saboda faɗin Manzon Allaah
(Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam):
لَا
طَلَاقَ وَلَا عِتَاقَ فِي إِغْلَاقٍ
Babu saki ko ’yantawa
a cikin rufewar hankali ko tilasci. _(Sahih Abi-Daawud: 1919)._
Bai kamata kishiya da
taimaka wurin sakin kishiyarta ba. Domin Annabi _(Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi
Wa Sallam)_ ya hana hakan a cikin hadisinsa sahihi a cikin Al-Bukhaariy da
Muslim cewa:
« لاَ
تَسْأَلِ الْمَرْأَةُ طَلاَقَ أُخْتِهَا ، لِتَسْتَفْرِغَ صَحْفَتَهَا ،
وَلْتَنْكِحْ ، فَإِنَّمَا لَهَا مَا قُدِّرَ لَهَا »
Kar wata mace ta nemi
a saki ’yar uwarta domin ta ƙarar da akushinta, ta yi aurenta
kawai. Domin dai tana da abin da aka ƙaddara mata ne kawai.
Don haka, abin da
wannan mijin ya yi nufi a zuciyarsa kuma har ya furta da bakinsa, shi ne abin
lura kawai, ba abin da wani ya rubuta ba. Watau dai, saki guda ne kawai a kan
wannan matar wanda kuma yana iya dawo da ita ta hanyar kome, a duk lokacin da
ya so kafin cikar iddarta.
Shi kuma alƙali bayan ya bincika
kuma ya tabbatar da gaskiyar abubuwa, yana iya yi wa mahaifiyar nasmatariha da
gargaɗi yadda ya dace. Ita
kuwa wannan yana da ikon horar da ita a kan abin da ta yi na saɓa wa hadisin, da ƙoƙarin raba musulma da
gidan aurenta da haramta mata aure da mijin da Allaah ya halatta mata bai
haramta ba.
Allaah ya datar da mu
gaba-ɗaya ga abin da yake
so kuma yake yarda da shi.
_Wal Laahu A’lam._
Sheikh Muhammad
Abdullaah Assalafiy
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.