𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Slm. Mallam misali ka yi wa mutum Satan kudi da yakai dubu talatin sannan lokacin da ka yi nadama ka je neman yafiya sai ka tarar wannan mutumin ya mutu ya za ka yi kuma kana tsoron kar ka kaiwa yaran shi su tona ma asiri.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumussalam
warahmatullahi wabarakatuhu
Musulunci ya samar da
mafita mai sauƙi ga mutumin da yake son yin tuba na gaskiya amma mai haƙƙin ya rasu, kuma ba
lallai ba ne sai ka tona wa kanka asiri a gaban yaransa.
Wannan lamari ne da
yake buƙatar natsuwa da kuma biyo matakan da addini ya tanada don
sauke wannan nauyin, tunda har ka riga ka yi nadama.
Tunda mai kuɗin ya mutu, kuɗin sun zama na
magadansa (mata, miji, yara, ko iyaye).
Kana iya tura wani
amintaccen mutum wanda ba zai tona maka asiri ba, ya kai musu kuɗin a matsayin
"kyauta" ko "haƙƙin mahaifinsu" ba gaira ba
dalili, ya kaiwa babban ɗansa da kake da
yakinin zai raba wa sauran ’yan uwansa kuɗin. Ko ka nemo lambar asusun banki (Account
Number) na ɗaya daga cikin manyan
yaran, sai ka tura musu ta banki ta hanyar amfani da sunan da ba naka ba (kamar
yin amfani da POS). Ko Ka sanya kuɗin a ambulan, ka rubuta "Haƙƙin Mahaifinku
ne" a jiki, sannan ka jefa musu ta ƙarƙashin ƙofa ko ka ba wani
yaro ya mika musu ba tare da ya san ko mene ne ba.
Idan har babu wata
hanya kwata-kwata da zaka iya mika wa yaran kuɗin ba tare da an gano ka ba, ga abin
da malamai suka ce za ka yi: Idan babu yaran kwata-kwata ko ba a san inda suke
ba, za ka iya sadakar da wannan dubu talatin ɗin da sunan marigayin. Sannan ka
yawaita yi masa addu'ar gafara da rahamar Ubangiji.
Ka kwantar da
hankalinka, Musulunci ba ya son tona asirin bawa idan ya tuba. Don haka, muddin
ka mayar da dukiyar ta kowace irin hanya ta sirri, Allah zai karbi tubanka.
Idan har ka yi nadama
amma ba ka mayar wa mutum hakkinsa ba (ko ka nema a yafe maka), tubarka ba za
ta karbu wajen Allah (SWT) ba saboda Shi Adali ne kuma ba Ya yafe hakkin wani
bawanSa sai dai idan shi wanda aka zaluncin ya yafe.
An karɓo daga Abu Huraira
(RA) cewa Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: Idan akwai Wanda ya
zalunci ɗan'uwansa (cikin
mutuncinsa ko dukiyarsa) ya nemi ya wanke kansa a duniya. Idan bai yi ba, za a ɗauki kyakkyawan
aikinsa a ba wanda aka zalunta gwargwadon zaluncin da aka yi masa. Idan babu
kyakkyawan aiki (ko kuma sun kare), sai a ɗauki zunuban wanda aka zalunta a ɗora wa wanda ya
zalunce shi. Sahih al-Bukhari 2449.
Wajibi ne a nemi
gafarar wanda aka zalunta ko a mayar masa da haƙƙinsa tun kafin ranar
sakamako. A ranar lahira, kowa zai karbi haƙƙinsa daidai
gwargwado.
Tuba na gaskiya yana
goge zunubi, kuma tunda kana da niyyar gyarawa, Allah zai rufa maka asiri
muddin ka nemo hanyar sirri ka mika musu haƙƙinsu.
Daga karshe ina yi
maka fatan alkhairi da addu'ar Allah shi karɓi tubanka, ya yafe zunubanka, ya sanyaka
cikin salihan bayinsa. Ameen.
WALLAHU A'ALAM
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.