𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum Malam da fatan kana lafiya. Don Allah Malam shin da hassada da kishi da mata ke yi wai duk abu ɗaya ne? Idan suna da bambanci shin mene ne bambancinsu a addinance?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikis salam wa
rahmatullahi wa barakatuhu.
Kishi da Hassada abubuwa
daban daban ne. Sai dai kowanne yakan janyo faruwar ɗayan
idan har mutum bai ji wa'azi ya gyara zuciyarsa ba.
KISHI: halal ne Mutukar zai
taimaka wa mace wajen neman yardar Allah ta hanyar zage damtse wajen yawaita
ladabi da biyayya da kyautata wa mijinta, kuma kishi yakan zo da ma'anar
"gasa" ko tsere da juna" atsakanin matayen dake karkashin namiji
guda. Kowacce takan yi kokari wajen ganon ta kula da hakkokin mijinta fiye da
sauran abokan zamanta, domin samun cikakkiyar soyayya daga gareshi, kasancewar
ita zuciyar ɗan Adam an horar da ita ne bisa son mai
kyautata mata, da kuma Qin mai munana mata.
A addinance, kishi abu ne
mai kyau da ya halatta idan dai bai wuce iyaka ba. Manzon Allah (Sallallahu
Alaihi Wasallam) da Sahabbai (RA) sun yi kishi. Kishi shaida ce ta tsantsar
soyayya da kima a zuciya. An bayyana namijin da baya kishin matarsa (wanda ake
kira da Dayyuth) a matsayin wanda ya sabawa koyarwar Manzon Allah (Sallallahu
Alaihi Wasallam), kuma ya cancanci tsananin fushin Allah da barazanar shiga
Aljanna. Annabi Muhammadu (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce kishi yana daga
cikin imani, kuma Allah Yana kishin haramcin sa, kamar yadda mumini ma yake yi.
HASSADA: Muguwar dabi'a ce
ta son wata ni'ima ta gushe daga hannun wani mutum ko a samu rashin jin dadi
kan ganin wani ya samu rabo. Wannan haramun ce. Babu wani alkhairi cikinta.
Tunda Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam yace: "Ina tsoratar daku
daga yin hassada. Domin hakika ita tana cinye kyawawan ladan mutum kamar yadda
wuta ke cinye Qirare".
Malamai sun bayyana cewa
mumini na gaskiya yana yin "giba" (fatan samun irin alherin da wani
ke da shi ba tare da fatan alherin ya gushe ba), yayin da munafiki kuma shi ne
mai yin hassada (fatan alherin ya gushe baki daya).
Da yawa daga cikin mata suna
kasa rarrabewa atsakanin waɗannan halayen guda biyu.
Maimakon suyi tsere da abokiyar zamansu wajen kyautata wa maigidansu, sai su
rika yi mata hassada da ita da 'ya'yanta. Suna Qin Kada wani abun alkhairi ya
sami abokiyar zamansu. Daga nan sai abun ya juye ya koma hassada da gaba da
Qiyayya, wani lokacin ma har da Tsafe-tsafe don neman cimma mummunan burinsu
akan abokiyar zamansu.
Ya zama wajibi ga duk matar
dake son rabauta a lahira ta kiyayi zurfafa kishi (wato baqin kishi) wanda ke
makantar da zukata ya raba mutum da imaninsa. Da zarar kinji alamar hassada
azuciyarki game da abokiyar zamanki, ki nemi tsari daga sharrin Shaiɗan,
sannan kiyi mata addu'ar alkhairi. Nan take zakiji hassadar tabar zuciyarki.
WALLAHU A'ALAM.
Zauren Fatawoyi Bisa
Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.